Showing 1 words to 3000 words out of 86122 words

Chapter 1 - BUDURWAR QAUYE Complete-by miss Deejarh-.txt

26 Nov 2024

4795

ο»Ώο»Ώ[10:34PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾




Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty mmn Faty


July, 2017




Bismillahirrahmanirrahim, ina godia ga Allah daya bani ikon fara rubuta wannan littafi, sannan wannan qagaggen labarine banyishi dan wata ko wani ba, Allahu yasa mudace, AmeenπŸ‘πŸ»




0⃣1⃣
"Alhaji Abubakar Muhammad da Alhaji Usman Sanusi, aminan junane qud da qud wanda hakan yasa suka zama tamkar yan uwa na jini "


" Alhaji Abubakar haifaffen garin Dambam ne ta jihar bauchi, wanda yakasance d'a na uku ga sarki Muhammad bin Abdurrahman wato sarkin dambam"


"Alhaji Usman Sanusi shikuma d'ane ga malam Sanusi mai almajirai wanda ya kasancewa malamin sarkine a fada kuma limamin babban masallacin garin dambam"


Tun tasowansu suke abota mai qarfi, tare suke Komai kusan ba wadda bai san da zaman abotarsu ba"


"kasancewar gidansu ba nisa atsakani, tare suke cin abinci hatta bacci basa raba makwanci sabida Alhaji Abubakar bai dauki kansa da wani abuba haka zasuje gidansu Alhaji Usman suci abinci hatta kwana sunayi tare acan"


"tare sukayi primary da secondary school dinsu, bayan sun qare ne daganan suka rabu amma rabuwa na wajen zama"


"Alhaji Usman shi baicigaba da karatu ba daganan ya fara kasuwanci, yana kuma noma, yayinda Alhaji Abubakar kuma yasamu fita waje qasar india karatu inda yasamu gurbin karatu a jami'ar new delhi yana karatun likitanci"




"Ranan da zasu rabu sai da sukayi kuka kamar wasu yara qanana, haka Alhaji Usman yayi ta zaman kadaici wadda daqyar ya saba da hakan"


"acan new delhi ma haka Alhaji Abubakar da qyar yasaba da kewan gida had'i da rashin aminnsa, ya fiskanci karatunsa sosai, lokacin da yayi shekara 1 anan ne yazo gida, yana arba da aminnsa sai kukan murna, ranan kwana sukayi suna hirar yaushe gamo "


" hutunsa na qarewa ya koma daganan bai sake zuwaba sai bayan Shekara guda da haka2 har ya kammala karatunsa, lokacin daya dawo gida yasanar da mahaifinsa cewar yazo ne amma zaikoma dan yasamu aiki acan sannan kuma yana da shaawar zama nawani lokaci acan, mahaifinsa baiqi ba amma yasanar masa sai dai ya tafi da iyali dan bazai je can ya auro wata qabila ba ya kuma amince da hakan "


" yana fitowa gida wajen aminnsa ya nufa sai dai abin farin ciki ya tarar amininsa yayi aure watanni hud'u da suka wuce "


" nan suka sha hira inda ya kawo masa alheri sosai kamar yadda yasaba dik lokacin daya zo , ya kuma sanar masa batun komawarsa hadda abinda mahaifinsa ya fad'a, ya taya shi murna kwarai "


" Alhaji Abubakar ya nisa yace kasan meye aminina? Aa sai kafad'a ya amsa masa, yace wlh nibansan ta ina zan fara neman matar bama kuma na tabbata mai martaba bazai lamunce mun tafiyar nan batare da dana cika umarninsaba, Alhaji Usman yace inaga abinda zaifi kawai kabasu zabi nasan bazasu maka zaben tumun dare dare ba, nan yayi naam da shawarar aminnsa"


"nan suka shiga cikin gida wajen matar aminnsa, suka gaisa ya kuma yaba da hankalin ta sosai inda yayi addu'a Allah ya bashi mata mai natsuwa kamar matar aminnsa "


" lokacinda Alhaji Abubakar yajewa mahaifinsa da zancen ya basu zabin matar dazai aura sunyi farin ciki nan take mai martaba yayi shawari da uwargidansa nan suka tsaida zance akan zaa hada shi da saudah yar kanin mai martaba "


Cikin qanqanin lokaci aka tsaida maganar aure, saura sati daya sutafi aka d'aura aure, cikin kwana uku aka gama shagalin biki, ana gobe zasu tafi suna sallama da amininsa sai Alhaji Usman yace shikenan yanzu inkatafi da iyalinka xumuncinmu ya qare kenan dan bawanda yasan sanda zaka sake zuwa kuma "


"yace haba dai ai zumuncin mu har 'ya'yanmu sai sunyi, nidai kamun alqawarin idan Allah yasa da namiji ka haifa to motarsa acikin yara nane idan kuma nine nafara haifan da namiji to matarsa tana acikin 'ya'yanka, na amince aminina Allah yasadamu da alkhairi, nan suka rungume juna da qyar suka rabu "




*INDIA*
" tinda Alhaji Abubakar yatafo da matarsa saudah new delhi, bai sake waiwayan gida ba, afannin aikinsa kuwa yasamu ci gaba sabida kwazonsa, har kwatance suke da shi a asibitinsu sabida kwarewar sa akan aikinsa"


"zamansa da saudah zamane na amana ahankali suka fara son junansu, cikin qanqanin lokaci Alhaji Abubakar ya kamu da son saudah fiye da tunani sabida saudah wayayyar mace ce, nan itama ta sami wata college ta ci gaba da karatunta "


" Bayan shekara 1,saudah ta haifi yarta mace kyakyakyawa kamarta daya da mamanta, suka mata suna da *MABARUKHA*, sai da mabarukha ta shekara tukun suka shirya zuwa gida nigeria "




*NIGERIA*
" afannin hajar matar Alhaji Usman kuwa, har yau Allah bai basu haihuwa amma hakan bai d'aga hankalinsu ba dan sunyi tawakalli da Allah shine mai badawa da hanawa "
" watarana Alhaji Usman yadawo kasuwa da yamma suna zaune shida hajar atsakan gida suna hira, kwatsam sukaji sallama, wazasu gani Alhaji Abubakar d matarsa harda yarsu "


" sunyi murna sosai da ganinsu, nan yake cewa tin jiya da dare muka iso, dasafe kuma nasan katafi kasuwa shiyasa nace mubari sai dayamma sai mushigo, nan sukasha hiransu, hajar tana riqe da mabarukha kamar subarmata ita dan yarinyar tashiga ranta "


" watansu 1 suka koma new delhi, tinda suka tafi basu sake zuwa ba sai bayan shekara uku nanma suka zo da yarsu mai watanni 9,takwarar mahaifiyar Alhaji Abubakar Maryam suna karanta niima, awannan zuwan ne da yayi ne ya biya masu hajji shida amininsa "


" inda suka tsananta addu'a aka'aba akan Allah ya cika masu burinsu, na alqawarin da suka d'aukanma junansu"


"Bayan sun dawo ne Alhaji Abubakar suka koma Bayan shekara 1 abin mamaki sai saudah tasamu ciki, dik da planning dasuke, haka suka reni cikin har yakai haihuwa, saudah ta haifi da namiji kyakykyawan gaske kamarsu 1 da babansa, suka saka masa suna *Muhammad Alameen* takwaran mai martaba, amma sabida babban suna gareshi yasa suka masa alkunya da *Papa* wato baba sunbi harshen india "


" papa nada watanni shida suka zo nigeria, kowa yayi farin cikin qaruwan da rana suka samu, awannan zuwan ne yasaima amininsa gida mai, sunje ganin gidanne Alhaji Abubakar yace ma amininsa, kaga lamarin ubangiji ko sabida haka kada ka fidda rai Allah y rubuta matar papa daga cikin yaranka ne shiyasa Allah bai baku haihuwa ba har yanzun "


" Alhaji Usman yace Allahu yashaa, inanan kullum ina addua Allah yabani haihuwa, Alhaji Abubakar yace insha Allah, Allah zai baka, bayan sati biyu suka koma india "






✍🏻Faty Mmn Faty
[10:35PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾




Budurwar Qauye πŸ€·πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty mmn Faty


July, 2017




*Wannan page nakune Mmn Faty Fans, Allah yabar qauna, Mmn Faty luvs u all 😍😘*




0⃣2⃣
"Kwanaki sun wuce, watanni sun shud'e, shekaru sunja, Allahu maji roqon bawansa "




" Kwatsam ba zato, ba tsammani Allah ya azurta hajar da samun ciki, murna farin ciki ba kalan da basu yiba, hatta wani nasu ma ya taya su murna matiqa "


" cikin ikon Allah suka raini cikin lfy har tasauqa lfy, ta haifi yarinya mace, kyau kam kamar ita tayi kanta, dik wadda ya kalleta sai yace masha Allah, ranan suna taci sunan mahaifiyar Alhaji Usman wato Fateema suna kiranta da Fauziyyah, tindaganan kuma basu sake samin haihuwaba "


" haka suka ci gaba da rainon Fauziyyah cikin so da kulawa, Fauziyyah ta taso cikin gata sai dai son dasuke mata bai hana su tarbiyantar da ita ba "


" Fauziyyah tana da shekara 4 aka sakata a makarantar allo sai dai me, albasa batai halin ruwa ba, dan Fauziyyah bata dakko halin mahaifinta na haquri ba baran mahaifiyarta dako yatsa kasa mata abaki haka zaka cireshi "


" wasa, barna, tsokala dik ta had'a abin baa cewa Komai, idan taje makaranta wanda tafishi tadakeshi, wanda ya fita kuma ta tsokaleshi malam har gaji da kawo masa qarar ta da ake, gashi dududu shekarar ta 4"


"Fauziyyah nada shekara 6 aka sanya ta a makarantar primary, nan danan kowa yasanta a makarantar dan Fauziyyah akwai ilmi gata yarinya qarama , uwa uba kuma tsokalalta su suka saka kowa yasanta "


" tin abin bai damin mama harya fara daminta, wata rana Alhaji Usman ya dawo daga kasuwa da yamma suna zaune, sai yana hajar tayi shiru kamar mai tunanin wani abu"


"dubanta yayi cikin kulawa yace, mmn Fauziyyah yadai kikayi shiru haka? Nisawa tayi tace hmm wlh Alhaji alamarin Fauziyyah yanzu yafara bani tsoro, cikin sauri yace namefa? Fahimtar dani, tace wlh ba hali Fauziyyah ta fita baa kawomun qarar taba, kona hanata fita haka zata fakeni ta fice, tin ina ganin yarintane har abin yafara wuce tinanina "


" murmushi yayi yace haba hajar, dik ma shekarun mama na nawa suke, shekarnta shida da d'oriya nefa, kuma kowa da kalan yarintarsa, zata bari bari ta qara girma kiga dik zata bari, tace toh Allah yasa mudace amma Fauziyyah ga barnan ganganci datakemun ban isa na aje abina afili ba saita tab'a"


"dariya yayi yace to kinga yarintar kenan, tace hakane Allah yasa mudace, yace amin, kinsan ni yanzu ba abinda ke damina kamar rashin jin labarin aminina yau kimanin shekara 7 kenan rabonsa da gida abinda bai tab'a yiba kenan, tace gaskiya kam Allah yasa suna cikin halin lfy, yace dan lfy kam lfy suke sai dai kawai bai samu daman zuwaba neba, tace toh Allah yasadamu da alheri, ya amsa da amin "




*INDIA*
β€œWata kyakykyawar mace nagano zaune awani qayataccen falo, idanunta sanye da siririn farin glass tana duba wata doguwar takarda"


"lokaci 1 tad'ago kanta sakamakon bud'e qofar dataji anyi, wani qayataccen murmushi tafara lokaci guda, kallon qofar nayi dan naga metakema wannan murmushi mai tsadan "


" wani matashin saurayi wadda akalla shekarunsa bazasu fice 16 ba, amma kyau kam iya kyau Allah ya bashi daganinsa zaka fahimci d'an kwalisane, kuma d'an gata lura da irin kayan jikinsa da wayoyin dake hannunsa "


" shima da murmushi afiskansa wanda yaqara qawatar da fiskartasa, ya nufo inda take, zagayowa yayi ta bayan kujerar datake zaune, rungumeta yayi ta baya ya d'aura kansa akan dokin wuyanta, da cool voice nasa yace hello momcy, kesi hoo? (yaya kike), tace am fine my son aur tum ? (kaifa), yace me too momcy, lekin (sai dai) am tied wlh, momcy tace oh papa aikin me kayi har kagaji, cikin shagwab'a yace haba momcy deko (duba) naje wajen salman, daganan mukaje shan ice cream fa dik kice bangajiba, shafo lallausan gashin kansa tayi, da sigan rarrashi tace eyyerh sowwie jawo kamre (kaje d'aki) kahuta ko"


"miqewa yayi ya wuce harya kai bakin qofa ya juyo yana cewa, kahahe daddy momcy? (ina daddy momcy), ya fita kasan gobe jirgin karfe 10am zamu wuce "


" oh momcy bazaa barnaganan zuwa nijer dinnan ba, yafad'a rai b'ace, tace haba papa ba mungama maganar nan ba just 1month nefa zamuyi mudawo sabida karatunka n pls ka haqura, wucewa yayi bai sake kulata ba sai ma qananun surutai dayake akan bai son zuwa nigeria "


" d'akinsa ya wuce, yana shiga ya fad'a kan tangamemen gadonsa rai b'ace, afili ya furta why daddy why kskeson zuwa nijer, always baka da magana sai na nijer wani dogon tsaki yaja ya furzar da wani iska mai zafi daga vakinsa, miqewa yayi kamar an tsunkuleshi ya nufi bathroom, shower ya sakarma kansa sosai, ya kai 30mins kafin y fito "


" wasu shirt da 3quater nashan iska yasaka, sannan ya bud'e wata drower, wasu drugs naga ya d'ebo ya watsa abakinsa ya bisu da ruwa sannan yabi lfyr gado, nan da nan bacci yai gaba dashi "


" papa kenan dan gatan daddy da momcy, yataso cikin so da qauna d kuma kula ta mahaifa, papa tin yana qarami haka yataso da ra'ayi idan baiso abuba aka sakashi to tabbas abin ba zaiyi kyauta"


"tin tasowarsa haka yake komai nasa unique ne, dan baison qazanta, baison hayaniya haka baison rayuwar area shiyasa ya tsani zuwa nigeria, acewarsa mutanen can sunfaye hayaniya "


" yanzun yagama secendary school nasa, zai tafi universty amma idan kaga irin shagalinsa dayake sha wane wani wanda ya kammala jami'a"


"tin yanayi ab'oye har ya zamana baya b'oyewa, tsiyarsa yake tsulawa, shaye2 kuwa baacewa Komai, su momcy kullum adduarsu Allah ya shiryeshi"


"amma dik abinda yake baya wasa da sallah, haka karatunsa kullum d gread mai kyau ya fitowa, shidai matsalar 1 baison zuwa nigeria dik sanda zaa zo sai yaji damuwa tamasa yawa papa kenan dan daddy da momcy"


"Washegari suka tafo amma basu iso ba sai wata Washegari, nan gida gida ya rud'e da murnan zuwansu, da daddare ana cike afalon mai martaba anata hira amma banda papa, mai martaba yana lura dashi, azuciyarsa yace tabbas wannan dik acikin jikokina da takwarorina babu wanda ya gadoni ya kuma cika jinin sarauta kamar Aminu, da hannu ya nuna masa alamun yazo kusa dashi, ba musu ya je wajensa kuma papa ya sake dashi har suna hira yana ta murmushi "


" Washegari da yamma daddy, momcy, didi (adda) mabarukha, didi niima da papa, suka tafi gidan Alhaji Usman, suna isowa qofar gidan kowa ya fito amma banda papa"


"daddy yace muje mana kazauna anan, b'ata rai yayi sannan yace main hoon nah daddy(ni ina nan daddy) daddy yace oh Alamin don't say that mana umm, ohyah lets go "


Haka dai ransa baiso ba yafito, dik sun shige shine na bayan shiga aiko yasa qafarsa zai shiga yaji anbige ta baya anwuce shi da gudu"


"bayanta kawai yagani kamar walqiya ta wuce ciki bai idah tinanin mai ya koro ta gudu haka har tana bigeshiba yaga wata yarinya tana cewa wlh zaki fito sai naci ubanki badai inkika daka kika gudu ba, toh bazanma kai qararkiba baran abani haquri, shegiya kawai tana kaiwa nan ta juya ta wuce"


"papa dai ya gama quluwa jiyake tamkar ya juya, haka yaqarasa ciki, nan ya tarar da su daddy sai murnan labarin dasuka samu na fauziyyah suke, Alhaji Usman yace baku ko zaunaba wannan shashashar tashigo da hauka, daddy yace ai nikam bazan iya zamaba "


" ikon Allah, sai haka yake maimatawa, momcy ce ta jawo fauziyyah jikinta tace zonan 'yata, nan suka zauna aka shiga hirar bayan rabuwa, mama ce tace da fauziyyah baki iya gaisuwa bane kina rakubewa dan kinyi saa ban dakekiba"


"daddy ne yace haba dai amata ahankali mana, zonan matar Alamin, daram gaban papa ya fad' I, dasauri y d'ago kansa yana kallon daddy sai yaji Abba yana cewa aiko zaisha fama dawannan rigimar "


" ransa ya gama baci, nawa yake da zaa masa zance aure, aurenma da wata qaramar yarinya, qazama, yar qauye, burinsa bai fice su tafiba kozai samu amsar tambayansa awajen daddy "


" basu suka tafi ba sai kusan sallan magriba, aiko suna shiga mota yace daddy wai wane Alamin ne mijin wannan jaririyar? "


" daddy yayi dariyansu na manya yace momyn yara kinji danki da wani zance, tace inajinsa daddy papa sai kai daddy nikam rigima zai tsayar mun"




"daddy yace dana fiso muyi maganar anatse, amma tunda katambaya nan ya bashi labarin alqawarin dake tsakaninsa da amininsa"




"papa yace ammadai baniba dan auri wannan qaramar yarinyar, yar qauye villager haba god fobid, daddy yace aifa kaima karatu zaka fara, kafin kagama Itakuma ai tazama budurwa "




" papa yace never mai zanyi da *BUDURWAR* *QAUYE*, kuma ma nifa mata basa gabana kawai ka warware wannan alqawarin cos I can't marry that villager girl that's all"




✍🏻Faty Mmn Faty
[10:36PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾




Budurwar Qauye πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


July, 2017




0⃣3⃣
"Daddy yace kawai abar maganan nan sai lokacinta yayi, n all I want u to know, I can't break that promise, yeh hai vadha (this is a promise) "


" papa yace kyiu Daddy kyiu? (meyasa, meyasa)
Daddy yace mubar maganan nan ko, ya isah haka, ya fadi hakane dan yasan yanzu sai yatayar masu da rikici "


" niima ce tace bross kadafa ta girma kazo kana rigima, afusace ya juyo, momcy Allah kimata magana "


" su mabarukha sai dariya suke masa, momcy tace mabarukha bass(ya isa), rabu dasu kaji, har suka zo gida baisake maganaba, kallo 1 zaka fahimci ransa ab'ace ne"


"tin daga ranan bawanda yasake tada maganar fauziyyah, amma aqasan zuciyarsa wani tsana yakeji gameda da ita baran idan ya tuna yadda ta bugeshi ta wuce da gudu, afili ya furta pagal(mahaukaciya) "


" watansu 1 suka koma akan sai After six months dasu dawo bikin mabarukha dan sun dai dai ta da dan yayan daddy, harma an masu baiko "


" bayan sun koma da 1month papa ya fara zuwa skull, inda yake karantan medicine, acan sake samun wasu friends, inda iskancinsa yafi nada "


*6 months later*
Suka shirya tahowa bakin mabarukha, wannan zuwan papa yana doki sabida bikin sis nasa"


"satinsu biyu da zuwa akayi biki nagani nafada, aka kai amarya gidan mijinta acan abuja inda yake aiki "


" daganan suka koma, bayan shekara biyu Daddy ya yanke shawarin dawowa nigeria da zama, haka suka shirya suka taho inda sukabar papa acan sabida karatunsa"


"kowa yayi farin cikin dawowansu, inda yace amma agarin bauchi zai zauna, bata lokaci ya sai fili a unguwar gida dubu ya hau gini hadda ginin asibitinsa"


"watanninsu shida a dambam suka koma bauchi, inda yanzu zumuncinsa da amininsa yaqara qarfi dan yana yawan zuwa dambam shima kuma yana ziyartarsa "


" afannin papa kuwa, tinda su daddy suka bar india baizo nijer ba, dan baya cikin kad'aici, ya had'u da wani friend nasa d'an bauchi shima karatu yakaishi can, tare suke sheqe ayarsu, tun papa bai iya shan giyaba yanzun yazama expert, shiyasa yake manta zuwa gida ma, watarana suna waya da daddy yake cema daddy shifa idan yaqare karatunsa bazai dawo ba, daddy yace bai aminceba ganin ran daddy ya baci sosai yasa ya haqura "


*After 4years*
"kyawawan motoci qiran zamani suka tsaya a qofar wani tangamemen gate inda mai gadi ya bud'e masu suka shige ciki"


"motar dake gaba daddy da momcy ne suka fito fiskansu dauke da murmushi, dayar motan kuma wani kyakykyawan saurayi na gano tabaya, dogone sosai qirjinsa yana da fadi, ina zagayowa naga papa ne dan nayi zaton hakan"


"papa ne yagama zama cikakken saurayi, daga yanayinsa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login