Showing 54001 words to 57000 words out of 86122 words

Chapter 19 - BUDURWAR QAUYE Complete-by miss Deejarh-.txt

26 Nov 2024

4812

noo wlh kadana kuma ganinki da wani dan iska agidannan ko awani waje


Da mamaki take kallonsa kawai yadda ya haqiqance yana masifa kamar zai daketa


Cikin jin haushi tace toh miye damuwarka kuma miye hadinka dani dazakazo kanamun wasu magana marasa maana da dadin sauraro


Oh maganan tawace marar maana ya tambayi kansa wani haushi ne yasake kamasa kallonta yake ido cikin ido yace becouse meh tumse pyarr kartahoo( sabida inasonki)


Wani wawan kallo take binsa dashi tagagara cewa komai sai idanu kawai take binsa dashi cos she is totaly speechless


Ahankali bakinta ya furta pyarr(so)


Yess hah kahona pyarr hai(eh inasonki)


Girgiza kanta tayi cikin wani qunan rai dan ji take kamar ya watsa mata dafi


Tace kayi gaggawar fadin istigfari


sabo nayi yafada yana kallonta


Tace aiya wuce saboma inka manta na tuna maka


Kaikuwa mai zakayi da yar qauye qazama wawiya jaka yarinya qarama wadda batada abin shaawa baran na marmari

Wani zufane ya fara tsatsafo masa ta ko ina jin yadda take jero abinda ya dinga fada mata abaya wato bata manta ba


Gagara magana kawai yayi dan baya da tacewa bai kuma san ta ina zai fara ba


Tsabar bacin rai idanunta sunyi qanana da kakkausan murya tace wlh ka cuceni kuma baa taba fadamun baqar magana irin wadda kafadamun ayanzuba wai kana sona bakaji kunyar fadin haka ba


Nace bakaji kunya ba toh koda maza sun qare kaikam nayafe akai kaya masauqi


Sai anan yayi magana yace dik abinda zakifadamun kifada matuqar zaki huce all i know is i luv u with all my hrt


Tace nikuma i hate u n i really hate u ta zuga masa wani wawan tsaki ta wuce tace kana wasting mun time da alama bakada abinyi


Tana wucewa shikuma ya koma da baya ya nufi lambu cikin damuwa kozai samu sauqi da zogim da zuciyarsa takemasa


Tin daga ranan yake binta kullum cikin roqo da ban baki yake akan tasaurareshi amma sam baya samun fiskanta abin duniya yamata zafi yarasa madafa baran taka maimai


Ya rame ya fada sabida ko abinci bai iya ci damuwarsa fauziyyah ta aminta dashi ganin bashida mafita yasa ya yanke shawaran zuwa wajen daddy dik abinda zaayi ayi kawai shidai adawo masa da matarsa....


โœ๐ŸปFaty Mmn Faty








๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ



๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ






Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€


Written by Faty Mmn Faty


September, 2017






5โƒฃ2โƒฃ
Kwanansa biyu yana shawarin taya zai tinkari su daddy baicin abinda ya faru abaya


Cikin kwanaki biyun nan damuwarsa ta tsananta sosai


Har momcy ta gaza haquri sunayin dinner tace baba na lfyrka kuwa two days dinnan


Dagoda kansa yayi hadi da qaqalo murmushin dole yace mene kika gani swt momcy


Naga dik kacanza irin u look so sad haka kamar bakada walwala


Sake murmushi yayi yace babu komai sai dai stress din aiki kawai

Toh Allah ya taimaka tafada amma badan ta yarda da abinda yace ba


Washegari bayan sallan ishai ya yanke shawarin zuwa wajen daddy

Bayan yayi sallah gami da adduoi akan Allah ya dorasa akan daddy dan yasan idan daddy ya amince zance ya qare


Falon daddy ya nufa zuciyarsa na dukan uku2 da sallama ya shigo yasami waje ya zauna


Daddy ne kadai yana kishingide yana kallon tashar CNN


Dago kansa yayi yana amsa sallamar
Zama yayi yayi shiru yana tunanin ta ina zai soma magana


Daddy ne ya katse masa tunani da fadin yadai Alamin kaxo tayani hira ne


Dan sosa kansa yayi yace um eh daddy naxo taya ka hirane sannan akwai maganar danazo da ita


Ok inajinka ya akayi
Cikin dakewar murya yace umm dama daddy alfarma nazo nema wajenka


Uhum go on name fa daddy yafada yana kallonsa


Cikin sanyin murya yafara magana daddy dan Allah badan niba kataimakamun yadda Allah ya taimakeka kadawomun da matata wlh nayi nadama kuma nagane kuskurena bazan sake aikata makamacin abinda yafaru abaya ba


Kallonsa daddy yake sosai yace Alamin banfahimcekaba explain to me further


Cikin murya mai rauni yace daddy nayi nayi iyaka qoqarina fauziyyah taqi ta saurareni wlh daddy inasonta zan iyah shiga wani hali matuqar fauziyyah ta gujemun


Dan Allah kasa baki daddy kataimakeni tunda tanajin maganarka yaqara maganar kamar zaiyi kuka


Daddy yace kafazomun damagana adunkule kafito straigh forward kayi magana mana


Toh daddy gaskiya matata fauziyyah nakeson adawomun da ita


Wani kallo daddy yake binsa dashi kamun ya tashi daga kishingidar dayake ya zauna dakyau yana dubansa


Yakai minti biyu kafin yace Alamin kana da hankali kuwa kasan me kake fadi kuwa tohma ta ina tazama matarka ko kamanta da ba aure atsakaninku


Daidai shogowar momcy kenan


Zama tayi agefen daddy tace lfy kuwa meya faru daddy?


Daddy yace wai cewa yake adawo masa da matarsa


Cikin takaici momcy ta dubesa tace ashe bakada hankali bansaniba


Ta ina kataba ganin anmaida aure akan saki uku eye?


Nadauka kayi hankali ashe dasaurnka haryanzu daka samu Allah ya taimakeka ya rabaka da raqai dakuma lfyrka shine zaka tono wani abinda baxai yiyuba


Daddy yace baki fahimcesa ba ashe ai gara yace amayar masa da matar da yayima saki uku akan abinda yazo dashi amma gaki gashi ya maki bayani da bakinsa


Duban papa tayi cikin rashin fahimta tace nifa kunasani aduhu wai meke faruwane


Kansa tsaye yace matata fauziyyah nakeso adawomun da ita


What? Shine abinda momcy tafada tana kallonsa kafin tace toh gaka ga daddy wannan ba magana ta bace


Daddy ya kallesa da kyau yace kasaurareni da kyau kaji abinda zanfada maka


Abinda nakeso dakai kada nasakejin wannan maganar abakinka koda kuwa awasane


Daddy dan ....


Daga masa hannu yayi yace banason jin wata magana daga bakinka ingar akan shirmen banzan nanne


Juyawa yayi wajen momcy yace pls momcy kitaimaka mun ki....




Itama katsesa tayi tace papa tashi kafita saida safe dan banason damuwa kajiko


Daddy yace oyah tashi kabani waje stupid kawai


Jiki asabule ya miqe ya fito harjinsa yake kamar bashida nauyi tsabar yarasa tudun dafawa


Ranan haka ya kwana idonsa biyu cur tsabar damuwa da rashin madafa


Tunani iya tunani yayi amma yaga bayada mafita dole wajen daddy zai koma amma bari ya bari sai bayan kwana biyu


Cikin kwana biyun nan dik wanda yagansa yasan yana cikin damuwa matsanan ciya


Idan ya fita aiki acan zai wuni daya dawo ya shige side nasa sai dai sallah ke fito dashi ko cin abinci bai zuwa yadawo shiru abinsa iya da safe ya gaidasu kafin ya fita ko break bai tsayawayi


Bayan kwana uku yauma yasake dawowa wajen daddy




Daddy naganinsa ya bata fiska yace yadai kagama fishin da kake damune?


Girgiza kansa yayi yace wlh ko daya nibana fushi daku taya zanyi fushi daku kuma


Dan Allah daddy kasaurareni kataimakeni kamayar mun da matata kuma ko wanne irin sharadi ka shimfidamun na amince zanbi zanbi


Daddy yace kai banace banason sake jin wannar maganar ba


Idan har aure kake buqata ko a inane ka nemo zan shige maka gaba amma banda fauziyyah


Yarinya mai hankali da natsuwa ba irinkaba ai kaikam da ita kunyi hannun riga dan bata dace dakaiba baka dace da ita sabida haka kwarya tabi kwarya


Kuma aidai kana sane cewar aurenta ma ya kusa ko


Dam yaji gabansa ya buga


Yace yes aurenta ya kusa ko atunaninka zaa maimaita irin abinda ya wucene asake rabata da masoyinta na gaskiya abaka kaje ka wulaqan tata aidai ko kulya mutum ya ajiye zai kula da ita bare mutum dan adam bayan kagama azabtar da ita hakan bai makaba sannan kazo gabana kamata sakin walaqanci ka tozartani ko kana tsammanin na mantane wannan cin mutuncin dakamun haba haba cikin tsawa yace katshi kafita agabana kada kasa nayi abinda banyi niyyaba kafita nace


Durqusawa yayi yana hawaye ya riqe kafar daddy yana cewa nasan nayi kuskure kuma ban kyautawa kainaba daddy nayi danasanin abinda na aika ka taimakeni daddy kada karabani da fauziyyah wlh inasonta kuma itace rayuwata kada karabani da rayuwata


Daddy yace baka sotaba saida kaga tazama mutum ko kuma aikai kanisanta kanka da ita sabida haka kaje kasamo uwar mata ka aura wannan yarinyar ba saarka bace


Riqe daddy yayi yana kuka yana roqonsa amma daddy sam bai saurareshiba saima kwace qafarsa yayi ya wuce abinsa yabarshi durqushe awajen yana kuka .....






โœ๐ŸปFaty Mmn Faty








Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€


Written by Faty Mmn Faty


September, 2017


5โƒฃ3โƒฃ
Momcy da ta taho wajen daddy tinkafin taqaraso taji kamar alamun gunjin mutum na kuka


Cikin sauri ta qarasa hankali tashe bako sallama ta fado cikin falo


Turus tayi ganin papa durqushe yana kuka


Dasauri ta qarasa wajensa tana tambayarsa papa meya faru nace meya faru


Bai amsataba sai rungumeta da yayi yana kuka


Cikin tsanin tashin hankali dan batasan meke faruwa ba tace am asking u kya hua(ina tambayarka meke faruwa)


Da kyar ya iya furta momcy pls help me wlh inasonta inasonta bazan iya rayuwa ba ita ba kitaimakeni ki lallashi daddy yayi fushi dani yana magana yana kuka kamar qaramin yaro


Wani iri taji har cikin ranta kuma yadda taga papa ya gigice tabbas yanzu yanason fsuziyyah kuma so mai tsanani sai dai ba yadda zaiyi saidai yayi haquri tunda dama shiya sake damarsa tun farko


Wani irin tausayinsane ya kamata haka takejin kukansa har cikin ranta amma haka ta danne zuciyarta


Tace toh me kakeso namaka papa baicin what ever happens is all ur fault


Yace i know momcy nina janyo ma kaina kuma wlh nayi dana sanin kuma tun fauziyyah bata dawo nagantaba nake fama da matsanancin sonta bawai yanzune nafara sonta ba kiyi wani abu momcy


Ganin yadda ya birkice yaketa surutai yasa ta saka hannunta tana patting bayansa smoothly hadi da lallshi


Haba papa ya kana abu kamar qaramun yaro uum
Ya isa haka nan ka kwantar da hankalinka ko so kake wani ciwon ya kamaka


Look at ur self ya kacanza just in two days haba


Nidai kawai kitayani bama daddy haquri sannan hankalina ya kwanta


Naji amma saika kwantar da hankalinka tukunna


Shiru yayi ya kwantar da kansa akan cinyanta yana sauqe numfashi


Miqewa tayi tariqe hannunsa suka nufi side nasa


Fauziyyah dataji maganar momcy cikin firgici baicin tare suke zaune ta wuce wajen daddy ta barta hakan yasa tabi bayanta da sauri
Tana zuwa bakin qofa ta tsaya jin maganar dasukeyi akantane
Cikin damuwa itama ta fara hawaye kuma jin yadda alamu momcy zatabi bayan danta tunda gashi ta nuna damuwarta akansa


Wani iri taji har ranta yadda momcy ta dauketa tamkar yarda ta haifa acikinta amma ace tasanadinta ta janyo mata tashin hankali
Sai dai duk da haka batajin zata iya komawa gidan papa gara ta sanarma Brr. Ya turo kawai tinda dama ya matsanta mata itace take dan jan abin


Jin takun fitowansu yasa tayi saurin barin wajen ta nufi dakinta tana hawayen da batasan dalilin yinsa ba


Dakinsa sukaje tace maza jekayi wanka barinzo ko


Abinci ta kawo masa ta lallabashi yaci sosai sannan tace ya bari zuwa kwana biyu zata lallami daddy amma sai inhar ya kwantar da hankalinsa


Bayan kwana biyu da faruwan haka suna zaune da daddare dikkansu afalo daddy yace ma fauziyyah daugther dama inason sanar dake kifadama Nabeel ya turo iyayensa maganar aurenku amma kafinnan zanyi magana da Abba muji wacce rana ya dace asaka zuwannasu


Wani irin tsinkewar zuciya taji wadda batasan dalilin hakanba


Papa kuwa da kyar yasamu ya lalimo numfashinsa wadda yayi barazanar daukewa


Ahankali ta furta toh daddy


Momcy kuwa shiru tayi harga Allah tanason papa da fauziyyah tunda yagane kurensa amma kuma tunda ita fauziyyah bata sonsa bawani mafita ya haqura shine kawai
Saidai tana tunanin irin halinda dannata zai shiga kallonsa kawai take tana nazarin yanayin dayake ciki


Fauziyyah ma dakinta tawuce tafada gado tana kuka tabbas tasan tanason Brr. Amma kuma batajinsa aranta kamar yadda taso Yasir
Nan tasakejin tabbas tayin rashin masoyinda takeso har abada


Papa ma haka ya miqe ya nufi dakinsa ya sanya makulli ranan kwana yayi acikin wani yanayi marar dadi


Washegari kasancewar saturday yasa har yamma bai fitoba


Zazzabi mai zafine ya rufesa shiyasa ya wuni a kwance


Gashi daddy yahana momcy zuwa ta duba lfy bai fitoba


Sai da yamma tukun ya lallaba ya fito
Fita yayi ya nemo magani awani pharmacy dake kusa dasu


Bayan yadawo da kyar ya sha dan ruwan tea yasha maganin namma saida momcy ta matsa masa afalonta ya kwanta


Daddy ya shigo momcy tace yanzu zanshiga wajenka dama Alamin ne baida lfy


Cikin ko inkula yace Allah ya sauwaqa kicema fauziyyah tafada ma nabil ranan saturday suna iyah zuwa dazu munyi magana da Abba


Yana fadin haka ya juya


Nan papa yasake birkicewa zazzabi ciwon qirji momcy harta tsorata




Amma cikin ikon Allah washegari yadan samu sauqi dan yasha magani


Kullum cikin lissafa kwanaki yake har anci kwana uku
Tunani badare ba rana yakeyi ta ina zaisamu mafita


Yanzu hanya dayace ta rage masa baibiba shine Abba


Kuma gaskiya yanajinjina taya zai kalleshi bayan abinda ya aikata abaya


S
ai dai kuma yaduba yaga baya da wani option gara yaje yasami Abba wataqil yadace acan tunda yasan Abba mutumin kirkine...


โœ๐ŸปFaty Mmn Faty






๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ






Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€


Written by Faty Mmn Faty


September, 2017




5โƒฃ4โƒฃ
Shikadansa ya gama shawarinsa baikuma fada ma kowaba
Gari na wayewa sassafe asuban fari ya dauki hanyar dambam


Cikin ikon Allah qarfe tara ya shiga garin dambam
Gidan Abba ya nufa saidai zuciyarsa tana ta bugawa dan baisan yadda Abba zai karbi maganar ba shinko zai sauraresa ko zaimasa irin abinda daddy yamasa


Da haka harya qaraso qofar gidan yana isowa Abbah yana qoqarin fita


Parkin yayi cikin dauri ya fito dan harya shiga mota


Saida yazo har jikin motar sannan Abba ya ganesa dan yasha jumfer har qasa ga hula hakan yasa Abba baikawo shibane


Da faraarsa ya bude motar yana qoqarin fitowa cikin sauri papa ya tsugunna yana cewa sannu Abba


Aa tashi tashi zaka bata jikinka ai tashi muje cikin gida mana


Tare suka shiga side din Abba dan mama bata gari sunje biki jos


Harqasa ya duqa ya gaisheshi


Shima da faraa ya amsa yace amma dai agarin ka kwana ko


Cikin ladabi yace aa yanzu isowana


Ah lalle kayi sammako yasu daddy dasu hajiya


Dik lfynsu qalau ya amsa


Masha Allahu yayi kyau


Shiru ya danyi kafin yace dama wajenka nazo Abba


Abba ya gyara zama yace toh lfy daikam inasauraronka




Qasa da murya yayi yafara magana cikin nadama yace Abba tabbas nimai laifine awajenku kuma nasan nayi kuskure amma kuyafemun badan halina ba kuyi haquri...


Katseshi Abba yayi da cewa ya isa haka Alamin kaifa danane kum ni bakamun komaiba sabida haka komai ya wuce kuma naji dadin yadda naganka cikin kamala ubangiji Allah ya yafemu gaba daya


Cikin jin dadi yayita godia Abba yace bakomai ya wuce


Sannan yasake qasa da murya yace dama Abba nazo roqon alfarmace awajenka


Abba yace namefa Aminullah


Yace dama Abba fauziyyah ce nakeso tadawo dakinta shikuma daddy yaqi amincewa nan ya zayyane masa yadda sukayi da daddy
Abba dan Allah badan halina ba kutausayamun yanafadin haka yayi shiru dan jinsa yake kamar zaiyi kuka




Abba ya nisa ya dubesa cikin kulawa kafin yafara magana
Yace da darko sai ince Alhamdulillahi daka fahimci kuskurenka kuma naji dadin yadda kaxo kasameni kaitsaye tun abubuwa basu kwabe


Kuma gida bai qoshiba aibazaa bawa dawo ba
Amma alhji bai kyautamunba yana sane da kanason maida matarka ya hana sannan ya shigoda wata magana


Kuma shi wadda yake neman nata aibaasan halinsa ba


Tunda Allah yasa kazo kasanarmun halinda ake ciki to tazo gidan sauqi insha Allahu gobe zanzo bauchin muyi magana da Alhajin


Wani dadine marar misaltuwa yaji yana ratsashi ta ko ina


Sake risinawa yayi yana godia sosai


Abba yace dakaida fauziyyah dik daya kuke awajena sabida haka ka koma abinka kasa aranka fauziyyah matarka ce insha Allahu


Godia sosai haryasa kalmar dazaiyi amfani da ita tsabar murna


Haka yayima Abba sallama ya kamo hanya zuciyarsa wasai
Rabonsa dayaji farin ciki irinna yau harya manta ranan


Gabda laasar ya iso gida wanka yayi ya fito yaci abincinsa hankali kwance


Momcy dai tayi mamakin canzawarsa amma dai tayi shiru batace komaiba


Yana nan zaune afalo tafito ta wucesa tinda yaga fitanta awannan lokacin yasan wannan man dinne yazo ko ajikinsa saida yagadama sannan ya tashi ya dauko car key nasa da wayoyinsa yayi waje


Motarsa ya shiga saida yazo dafda su sannan ya sauqe glass ya nunasa da hannu yace hey kada kabari nadawo nasameka tareda matata kuma zaifi maka sauqi idan katafi kada kasake dawowa


Duban papa yayi da kyau yace matar ka kuma ta ina tazama matarka


Yace bani da tym inada wajen zuwa amma katambayeta ita zata amsa maka ai yana fadin haka ya daga glass din motarsa ya wuce abinsa


Fauziyyah kuwa abu biyu su suka dameta nafarko yadda ta boyema Brr cewar papa shine mijinta na farko sannan yadda papa yake iqirarin wai ita matarsa ce


Brr. Ya kalleta da kyau yace wane ne wannan awajenki


Ahankali tace yaya nane


Yace kada kimaidani bitacan mana inason kifadamun gaskiya miye alaqarki dashi dan najima da fahimtar akwai abinda kika boyemum game dashi


Nan idanunta sukayi raurau tace wlh ba abinda nake boye maka kawai dai banason tuna abinda yafaru abayane


Yace naji amma kada kifadamum shine mijin da kuka rabu


Murya na rawa tace shi shine


Wani baqin kishine ya taso masa cikin fada yace i see shiyasa ashe yakemum abinda ya gadama kekuma kikaqi sanar dani ashe dama tsakaninmu akwai yar boye


Tace bahaka bane


Yace toh ya ne inba haka ba kawai bakida abinda zaki fadamun


Haka taita bashi haquri dan ta lura ransa ya baci shima haka ya tafi yana tunani kalakala


Washegari Abba yazo inda suka zauna da daddy akan maganar su papa


Amma fir daddy yace baisan zancenba idan har papa aure yakeso ya nemo awani waje


Abba yace toh shikuma baiga dalilin da zaa hana papa fauziyyah ba


Nan dai suka ringa muhawara har Abba yayi nasaran shawo kan daddy amma da sharadin sai fauziyyah ta amince


Abba yace batun wannan yaron sai adakar su amma aini har raina ya baci ace taya zaka hana alamin fauziyyah


Daddy yace bawai hanashi nayiba kawai abinda ya aikatawa kansane


Abba yace aiyawuce Allah ya kiyaye nagaba


Abba yace toh shizai tafi amma yanason magana da fauziyyah


Bayan tazo Abba ya dubeta yace mama na ya aiki


Lfy lau Abba ya mama sai gobe zadu dawo tacemun ko


Yace eh sai gobe insha Allahu ai anyi biki kam kuma sunyi ziyra


Tace hakanekan


Abba yace mamana ya maganar yaronda yake zuwa wajennaki kinsanar masa ya turo dinne


Shiru tayi tana tunanin dama akan jiyane zata sanar masa saikuma yatafi cikin bacin rai hakan yasa bata fada masa ba


Abba yace baki amsamunba


Ahankali tace aa banfada masa ba tukunna


Abba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login