Showing 45001 words to 48000 words out of 86122 words

Chapter 16 - BUDURWAR QAUYE Complete-by miss Deejarh-.txt

26 Nov 2024

4805

har yadan sami natsuwa


Amma da TJ ya tambayi khairy hanya hanya tamasa kawai taqi fada masa gaskiaya


Shima haka dai yayima walawala ya qi sanar masa khairy taqi fada masa dan kada yaji haushinta


Haka rayuwa tayi ta tafiya inda papa yake cikin wani hali yakumayi dana sanin abinda ya aikata abaya kuma har gobe fatansa Allah ya nuna masa fauxiyyah ya roqi gafararta dan yanxu yagane cewar alhakinta ya ke bibiyarsa


Ba abinda ke qara daga masa hankali kamar yarda kullum sonta yake qaruwa acikin zuciyarsa


Watarana ankawo wata yarinya asibitinsu tasamu matsala a guiwarta daga faduwa


Aifa tun dayaji sunanta fauziyyah shikenan haka yaringa hidima da ita har aka sallamesu sabida yarda yake qaunar mai sunan


Kuma yasama ransa dik ranada yasan inda fauziyyah take kuma bata da aure tabbas koza ayi yaqi sai an maida masa da matarsa idan kuma basu sake haduwaba yasan sontane zaiyi ajalinsa




*****
Fauziyyah ta sauqa lfy, inda tasamu tarba na mutunchi awajen mr khan da matarsa da yaransa yan mata guda biyu


Kwanan ta biyu da zuwa tafara xuwa makaranta tanajin dadin karatunta sosai gashi Amisha tana taimaka sosai akan abinda bata ganeba


Cikin ikon Allah karatunta yana tafiya yadda akeso


Da haka har tacinye shekarar farko


*Bayan shekara biyu*
Fauziyyah ce zaune tana hada kayanta cikin farin cikin sabida gobe zata koma gida nigeria cikin nasarar uban giji ta kammala karatunta da saka mako mai kyau


Yanzu tazama cikakkiyar *PAMACIEST*


Cikin shekaru ukun datayi sau biyu kawai taje nigeria


Washegari jirgin qarfe 9 nasafe ta biyo sai gida


Acan nigeria kuwa su daddy ne da momcy da su aunty mabarukha harda aunty niima sukazo taronta dan akwai liyafar da daddy ya shirya mata a nan abuja


Jirgin na sauqa na hangota cikin jerin fasinjoji amma zaka rantse da Allah baquwace tazo daga india kuma zata koma sabida yadda fatarta ta murje tayi wani haske na musamman kyanta yasake fitowa


Kallo daya zaka mata kafimci zallan wayewa atare da ita dan tana daga cikin jerin mata masu class


Ko yadda take saqqowa cikin natsuwa kawai ya isa ya tabbatar maka cewa lalle wannan mace ce mai jida kanta


Daddy kuwa murmushi kawai yakeyi


Cikin sauri aunty ta qarasa ta rungumeta tana mata oyoyo


Wani daddan murya naji ya daki dodon kunnena hausa takeyi amma kamar maiyin indianci sabida yadda harshenta ya juye


Cikin farin ciki ta gaisa da kowa sannan suka nufi gida


Da yamma aka gabatar da liyafa mai kyau acikin gida


Sunsha hira sosai da daddare daddy ya kirata yace washe gari zasu wuce bh tare amma ita zata wuce dambam gida dagacan zai tura driver ya maidata abuja sai service nata ya fito sai tadawo bh tayi acan


Haka koh akayi watanta daya a dambam ta koma Abuja


Watanta biyu a Abuja service dinta ya fito amma jos aka turata nan daddy yamata cukucuku amaida ta bh


Tsabar tanada daurin gindi ko camp bata shiga ba


Sai byan an musu posting aka duba nata anturata teaching hospital na bh


Ana saura sati daya ta dawo bh uncle salim qanin mijin aunty yazo da abokinsa Barrister Nabil Abdullahi gidan aunty mabarukha
Wajen aikinsu daya a bh yanzuma wani aikine ya kawo su abuja kuma babansa shine commissioner for works n houses na bh


Tunda ya kyalla idanu yaganta ya nacewa uncle salim shifa yaga wata balarabiya kuma tamasa


Har saida ya kira aunty awaya yafada mata abokinsa dasuka zo tare yaga fauziyyah yana so kuma ya fada masa ta taba aure yace ko dik yaran duniya ita ta haifa yaji ya gani


Aunty kuwa hakan yamata dadi nan take ta tura masa phone no fauziyyah


Tunda yasamu no shikenan waya ba dare ba rana text ne meyene amma sam fauziyyah bata kulashi dan ba namiji aranta sam


Ranan sunday ta taho bh dan monday zata fara fita aikinta na service


Isowan yamma tayi lis dan basu taso da wuri ba hakan yasa tayi bacci da wuri


****
Papa kuwa yau tun daya tashi yakejin zuciyarsa wani iri kuncine meye ne baima saniba gashi yana da aiki a office gashi akwai maganar da zasuyi da daddy kafin ya fita office


Dolee yasa da wuri ya shirya ya taho gida daga can ya wuce office


Fauziyyah kuma qarfe bakwai ta tashi tayi wanka ta shirya amma tayi ligh make up sai pink jambaki data goga a lips nata


Kayan su na coppers tasaka ajikinta nan naqare mata kallo da kyau


Rigat ta kamata sosai inda na fulaninta da suke a cike dam gasu atsaye suka cika mata gaban rigan hakama wandon hips nata da bayanta sunfito sosai dan ya kamata sosai


Gaskiya wadda yasan fauziyyah lokacin tana gidan papa yaganta yanzu bazi ganeta sabida yadda tacanza komai najikinta ya canza ga wani kyau na musamman data qara


Kallon kanta tayi tsaf a madubi sai taji kunya bazata iya fita waje ahakaba


farar qaramar hijab ta dauka iya guiwa amma bata saka ba sai ta riqo ahannunta


Nima sake kallonta nayi da kyau nan naga zallan kaman datake da *Arti matar Yash na cikin film din married again*


Cikin natsuwa ta dakko yar qaramar jakarta mai kamar purse ta rataya hannuntabriqe da hijab


Tana fitowa falo da momcy tafara haduwa bayan tagaisheta momcy tayi murmushi tace masha Allah kiyi maza kije wajen daddy sai kizo kiyi break ko


Cikin muryarta mai dadi tace ok sannan ta mufi bangaren daddy


Da sallama ta shiga cikin faraa ya amsa bayan ta gaidashi


Yadan mata nasiha sannan ya miqo mata key din motarta sabuwa dal daya saya mata yace motarki tana waje Allah ya kiaye hanya ki kula da tuki


Nan taringa godia sabisa baqaramin dadi taji ba


Daddy yace kada kidamu jeki abinki kada kimakara


Papa kuwa yana zuwa gida afalo ya samu momcy bayan sungaisa yace bari yaje wajen daddy


Tace toh sannan ya wuce


Momcy kuwa jin fauziyyah shiru gashi kada time ya wure mata yasa ta kwala mata kira


Dauther kiyi sauri kizo kiyi break kada kimakara


Fauziyyah kuwa ta fito tazo daidai kan steps da zata sakko falo taji kiran momcy


Dama sauri take taxo ta nuna ma momcyn kyautar da daddy yamata


Itama cikin daddan voice nata mai dadin sauri tace yess me arihoo momcy(ina zuwa momcy)


Daidai papa yasaka qafarsa zai haura kan steps da zai kaishi side din daddy yaji wata murya mai dadin gaske cikin harshen indianci tana magana


Saida yadan matsa baya data bugeshi dan cikin sauri ta wuce batama lura da mutum ba


Papa kuwa ganin kyakykyawar mace kuma ba india yasa yabi bayanta da kallo amma dake tariga da wuce sai bayanta daya kallah


Wadda hips nata yake masa gwaliyo


Lumshe idanu yayi ya bude gashi ta buleshi da qamshin turarenta


Cikin sauri ya riqe gini dan baisan yayi missing step ba


Jiki a mace ya shige dakin dadi amma muryarta sai yawo yake masa akwanyarsa




Bayan sun gaisa gagara haqura yayi yace daddy baquwa akayi agidanne


Daddy yace baquwa kuma


Papa yace eh kamar ma ba india ce kuma daga nan ta fito


Wani murmushi daddy yayi yace aa kam indai wacce tabar nan yanzune sai dai qanwarka


Papa yace qanwata kuma wacce qanwata nikuma inada qanwace




Daddy yace qanwarka fauziyyah mana yar gidan Abbanku na dambam


Cikin sauri ya dubi daddy yace Fauziyyah kuma itace ta fita anan




Daddy yace yawuce wai itace mana amma bar wannan maganar ina jinka yadda abin zai kasance yasa na ce kazo da safe




Ina papa hankali yayi gaba baimasan daddy yana yiba




Saida daddy ya lura baima tare dashi sannan ya tabashi yace kana jina Alamin


Cikin sauri ya firgita yace me kace daddy


Wani murmushi daddy yayi wanda shikadai yasan maanarsa........








✍🏻Faty Mmn Faty
[7:13PM, 8/26/2017] β€ͺ+234 803 082 4581‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾






Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


August, 2017






4⃣6⃣
Daddy yace maganar bude asibitin nan ne dama najika shiru haryanzu baka fadi wani suna zaa sama ba sannan wacce rana ya dace sabida buga IV


Papa dai yayi shiru yana jin dadi amma harga Allah dakyar ya tsinci kadan daga abinda yake fada masa


Sabida hankalinsa da tunaninsa baya tare da daddy


Cikin wani yanayi yace zanyi tunani akai zuwa gobe zan sanar maka


Yafadi hakan ne kawai dan yasamu ya tashi awajen dan ya tabbata bazai samu natsuwa ba har sai yayi tozali da farin cikin rayuwarsa dan yana da good assurance batayi aure ba tinda ya ganta agida da wannan lokacin


Daddy yace is ok sai najika toh


Aiko daddy na rufe bakinsa ya miqe cikin sauri yana cewa barinje office


Daddy yace Allah ya kiyaye hanya


Yana tafiya ya amsa da Amin


*****
Fauziyyah kuwa cikin sauri ta nufi wajen momcy tana murna


Rungume momcy tayi tana cewa dekho momcy meri gari key (kalli momcy key din motata) daddy ne ya bani kitayani godia


Cikin faraa momcy tace masha Allah, Allahu ya tsare hanya


Amin ya Allah ta Amsa


Momcy tace kije kiyi break kada kimakara


Toh ta amsa sannan ta wuce dinning, dan kadan ta iya ci sabida murna tadawo falo tace zata wuce


Har bakin qofa momcy ta rakota tana cewa ganan motar taki jiya dare aka kawota Allah ya tsare sai kindawo sannan ta juya ta koma ciki


Itakuma qarasa wajen motar tayi sannan ta bude ta shiga tana jin wani dadi aranta


Ahankali tamata key sannan tafara tafiya cikin natsuwa har bakin gate inda mai gadi ya bude mata gate ta fice


Direct NYSC office ta wuce sabida akwai abinda zatayi acan kafin ta wuce asibiti




*****
Papa yana fitowa yaga wayam bakowa afalo sai motsi dayaji acikin kitchen


Leqawa yayi sai yaga momcy ce itakadai


Ziciyarsa ce yaji ba dadi dan fauziyyah yaso yasake kallo


Asanyaye yace na wuce office amma idan nadawo zan biyo


Toh adawo lfy tace dashi sannan ya fice


Motarsa ya shiga ya wuce asibiti driving yake amma hankalinsa na wani waje


Tinani yake yanzu fauziyyah ce tadawo haka yarinyar da ya raina yanzu itace tazama big girl haka


Ikon Allah ne kawai ya kawoshi lfy yana parking ya wuce office nasa


Zaune yake amma yakasa tabuka komai tunani kawai ya addabi zuciyarsa har yafarajin yarasa maike masa dadi


Ya jima azaune amma ko file daya baigama dubawa cikin sauri ya ture su gefe ya miqe


Dan jin kansa yakeyi yamasa nauyi ga wani irin faduwar gaba da kunci dake damunsa


Gara ya tafi gida ya kwanta kawai


Wayoyinsa da key nasa ya zara ya fito


Cleaners da masinja suna gaisheshima amma hannu kawai yake daga masu


Yana fitowa ya nufi parking space sai yaga wata mota mai kyau kalar mata ta tsaya agefen motarsa


Kafin ya qaraso sai yaga ta fito tana rataya jakarta


Sake zuba mata idanu yayi tabbas fauziyyah ce amma badan daddy yafada masa ba bazai ganetaba


Sai alokacin ya lura ashe kayan NYSC ne ajikinta tambayar kansa yake yaushe kenan haka tafaru


Fauziyyah kuwa dago kanta dazatayi wazata hango yana nufota ya Alamin


Tabbas shine dan bazai taba bace mata ba dik da yadan canza yaqara kyau yadanyi qiba kadan sannan daganinsa naira tazauna masa fiye da da


Ahankali tasauqe idanunta tanajin zuciyarta tana bugawa da sauri sauri


Nan take taji wani zafi azuciyarta dan bata qaunar abinda zai hada ta papa ko ahanyane


Daidai da ya qaraso jikin motarsa amma ya qudira aransa zai mata magana dan bazai iyah ganinta ya wuceba


Itakuma yitayi kamar bata ganshiba zata wuce kamar daga sama taji muryarsa wadda kodaga bacci tafarka bazata manceba




Yan mata shine abinda ya furta yana kallonta


Cak ta tsaya dan jitayi kamar ya caka mata wuqa wai yan mata


Dagoda kanta tayi ta sauqe dara2n idanuwanta farare tas masu kamar madara akansa


Nan yaji wani abu wadda bai san mene ne ba kawai yasamu kansa da lumshe idanuwansa yana tasbihi ga ubangijin halitta dan fauziyyah ta tafi dashi gaba daya


Muryarta ta dawo dashi daga duniyar tunani daya tafi


Cikin halin ko inkula da rashin damuwa tayi kamar bata sanshiba


Ya tsina fiskanta tayi tana masa duban rashin sani tace konhei tum(wane ne kai)


Kutt dan zaro idanu kadan yayi sabida mamaki wai harshine fauziyyah zatace bata ganeshiba


Amma sai yadaure yayi wani qayataccen murmushi yace mera naam Dr Muhammad Alamin Abubakar(suna na Muhammad Alamin Abubakar)


Ya tsina fuska tayi ta wani juya idanuwanta tace eyyerh sowwie am not talking with people that i dont know


Tana fadin haka ta wuce abinta bata sake koda kallonsa ba


Shiru kawai yayi yabi bayanta da kallo


Cikin qunan rai ya bude motarsa ya fada yana tuna irin walaqancin da fauziyyah tamasa ta yankwanashi


Afusace yafigi motar wadda dakyar yataka birki yabawa scurity pass sannan ya wuce


*****
Juhaina ce ta dubi munnir tace wai saurin me kakeyi ne kamar wadda ba agidan zaka kwana ba


Yace kinsan najima bangankiba wlh ina kewarki sosai muje ciki narage zafi


Murmushi tayi sannan tace haba dai kaida zakayi 1 week me zai dameka kuma Dr sai yamma shida yadawo


Yace ai har tunani nke next idan zanzo wacce qarya zamu masa tunda munce nazo gyara carry over ne


Dariya tayi tace wannan mai sauqine tunda shi baho ne inba hakaba sai kace ba mutumin daya shiga ajin ABCD ba


Komai aka fada masa sai ya yadda


Shima dariya yayi yace nidai muje toh pls mana


Riqe hannunta yayi suka shige bedroom nata




Nan suka fara mashaarsu da suka saba


Tsabar sunyi nisa basa cikin hankalinsu ko jin shigowar mota basuyiba


Papa kuwa ko parking mai kyau baiyiba haka ya fito ya nufi cikin gida


Ahargitse ya shigo falo dakinsa ya nufa


Yazo daidai dakin juhaina harzai wuce sao yaji kamar nishi


Saurarawa yayi da kyau sai yaji tabbas ba kunnensabane nishintane


Cikin sauri ya bude dakin dan atunaninsa ko batada lfy ne


Yana shiga yayi turus wani jirine yaji ya debeshi yayi saurin riqe qofar sabida abinda idanunsa ya gane masa


Juhaina da munnir kwance haihuwar uwarsu suna aikata zinah


Abinda bai taba tunaninba juhaina zataci amanarsa kuma ma da dan uwanta


Su juhaina kuwa jin anbude qofa yasa cikin sauri suka juyo ganin papa atsaye yana musu wani kallo cike da baqin ciki har idanunsa sukoma jajaye kamar gaunta bushashshe


Dasauri munnir ya tashi akanta itakuma cikin razana ta tashi zaune tanajan mayafi tana kare jikinta


Ahankali yasamu nutsuwarsa ta dawo maida qofar yayi ya rufe da key sannan ya nufo su gadangadan


tsabar tsoro ba juhaina ba hatta munnir jikinsa rawa yake


Yana zuwa ya shaqo wuyan juhaina yace cikin kakkausan murya kifadamun wane ne munnir kuma meye atsakaninku


Aifa cikin tsoro da firgita tace dan Allah kayi....


Wani gigitaccen mari daya zabga mata saida taga wuta shiya katseta


Cikin tsawa yace wane ne munnir zaki fadamun da bakinki kosaina kasheki shegiya tsinanniyah macucuciya Allah ya isa tsakanina da keh wlh kinci amanata


Ganin yadda kamanninsa suka sauya fiskarsa tayi jajur tsabar bacin rai


Murya na rawa tafada masa tsakaninta da munnir tace amma kayafemun wlh bazan sake ba


Bata gama rufe bakintaba ya saka hannunsa ya makata da gini nan tafadi a asume


Munnir kuwa tsabar tsoro ganin yadda yayima juhaina saida ya saki fitsari ajikinsa


Aikuwa da papa ya damqoshi yafara dukansa yana cewa munafiki kana zaune agidana kana zaluntata ashe ina tare da kwarto bansaniba


Mari duka harbi haka yake masa saida kansa bakinsa hancinsa ko ina jini yake amma zuciya ta hana papa ya kyaleshi


Hannunsa yasa yakamo gabansa da iyah qsrfinsa ya jawota ya murde wadda saida ya saki kashin azaba


Hannunsa ya kama ya buga da jikin drower ji kake kass kass ya karyashi


Axaba iya azaba saida yakasa motsi sannan ya kyaleshi ya nufi toilet ya debo ruwa a bucket


Zuwa kan juhaina yayi wacce ke kwance asume ya sheqa mata


Nan ta firgita ta farka aiko itama nan yahau jibgarta da waya yana harbinta


Saida jikinta ya faffashe fiskarta ta kumbura tayi sumtum tsabar duka


Tsabar azaba har saida ta kasa kuka cikin baqin ciki ya jawota har waje tana nade acikin zanin gado amma saida kamanninta ya canza dan ba dukan wasa ya mata ba


Sannan yace tsinanniyah kada nafito nasameki kificemun agida na sakeki saki uku muna fuka


Itadai batada bakin kuka ma bare bashi haquri


Mai gadi ya kira yace suzo suna biye dashi har dakin juhaina yace su fitar masa da munnir agida su kaishi can waje


Haka suka jawoshi kamar har sun kai qofa paoa yace ganan haqorinsa biyu kuhada dashi kufitamun dasu


Suna fita ya nufi dakinsa yafada agado ya fashe da kuka....




✍🏻Faty Mmn Faty
🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾



🌾🌾🌾






Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


August, 2017




*Gaisuwa mai tarin yawa musamman zuwaga Members na Mmn Faty Novel Group, Ina matuqar jin dadin yadda kuke bada gudumawarku da nuna jindadin ku akan littafin BUDURWAR QAUYE nagode sosai Allah ya bar qauna 😘😍*






4⃣7⃣
Kuka yake mai cike da nadama, hawaye wani nabin wani haka suke zuba akan face nasa


Zuciyarsa cunkushe da zallar dana sani akan abinda ya aikata abaya


Tabbas yau ya tabbar alhakin iyayensa ne dana fauziyyah ke bibiyarsa


Kuma ya qara daukan darasi akan bijirema iyaye ba abune mai kyauba tunda gashi yaga saka makon abinda bai taba tunani ba


Wani irin nauyi yaji qirjinsa yamasa


Kuka yake sosai har abin tausayi domin dik abinda mutun ya aika matuqar yagane kuskurensa har yayi nadama nagaske ba tuban baqin muzuru ba dole ya baka tausayi


Sambatu kawai yakeyi yana cewa daddy, momcy, fauziyyah kuyafemun ashe gata kukamun na auramun yarinya yar mutunci kuma mai mutunci


Amma son zuciya yasa na bijire muku yau gashi abinda yasameni wayyo kaicona kaicon halina dama duk masu hali irin nawa...


Maganarce tasarqe qirjinsa ya cushe numafashi yafara masa wahalar fita


Dakyar ya dauki wayarsa yafara kiran layin TJ


TJ yana office saiya ga kiran abokinsa


Hello man shine abinda ya fada yana daukar wayar


Cikin wata raunanniyar murya datake nuna mai ita yana cikin wani hali




Yace pls kazo gida kasameni ina cikin wani hali


TJ baisan sanda ya miqe tsayeba cikin razana jin yadda muryar abokinsa take a hargitse


Meyasameka??? Shine abinda ya maimaita harsau uku


Ahankali papa yace TJ banida lfy juhaina zata kasheni kazo pls kataimakeni


Afirgice TJ yace ganinan zuwa ganinan zuwa am on my way yana fadin haka ya suri key din motarsa ya fito cikin sauri yacema scretery nasa idan bandawoba zuwa 2 ka kulle office kawai


Baijira amsar shiba ya fice cikin sauri da tashin hankali dan baisan yadda zai sameshiba


Cikin gudun balai har ya iso gidan papa wani mahaukacin horn yake dannawa


Maigadima saida ya tsorata dajin irin horn dake masa


Aiko baibata lokaciba ya bude


TJ yana shigowa ko cikkakken parking baiyiba ya hnyar cikin gida daidai qofar falo yayi turus ya tsaya ganin juhaina lullube da zanin gado tana rizgar kuka dan sai alokacin tasamu kuka yaxo mata gashi ya kulle

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login