Showing 48001 words to 51000 words out of 86122 words

Chapter 17 - BUDURWAR QAUYE Complete-by miss Deejarh-.txt

26 Nov 2024

4810

qofa bare ko kaya tasama jikinta baran tasannayi


Juhaina ina Alamin yake kekuma meya sameki naganki haka


Gagara magana tayi sai da hannu ta nuna masa qofar falo
Tura qofar yayi ya jita gam akulle bubbugawa yafara da iyaka qarfinsa dan abin yaqara bashi tsoro


Papa yanajin bugun qofa gakuma wayar TJ tashigo masa yasa ya taso ya fito falo ya bude qofar


Yanaganin TJ kawai saiya fada jikinsa yaqara saka kuka mai tsuma zuciya


Cikin rudani TJ yace waime ke faruwane man kamin bayani mana kozanji sauqin abinda nakeji


Sake qanqame TJ yayi yana cewa na cuci kaina na biyema san zuciyata na cutar da matata ta gaskiya na baqanta ran mahaifana yaugashi naga abinda bazan taba mantawaba


TJ ma kawai saiyafara hawaye nafarko tausayin papa dikda baisan meya faruba amma yadda yaganshi a hargitse yana kuka da idanunsa tabbas babban abune


Sannan murnan abokinsa ya gane gaskiya


Share hawayen fiskansa yayi yafara lallashin papa da kalamai masu dadi har papa yayi shiru


Sannan yafara bawa TJ labarin abinda ya faru yana furta abinda yagani sai da wasu hawaye masu zafi suka zubo masa


Cikin tashin hankali TJ yakejin abin kamarca mafarki


Nan ya fara tausan papa da banbaki akan ya kwantar da hankalinsa komai zai wuce


Papa yace hankalina bazai kwantaba har sai ka kaini asibiti anmin test na HIV tukunna


TJ yace insha Allahu babu abinda zaisameka ka kwantar da hankalinka


Taya hankalina zai kwanta matuqar ina dauke da wani mugun ciwo wlh jujaina ta cuceni ta shiga tsakanina da fauziyyah dan bayadda fauziyyah zata dawo gareni ina halin jinya


Tj yace ya isa haka muje asibitin inhar hankalinka zai kwanta dan yaga har numfashinsa yana samasama


Amma kabar juhaina ta suturta jikinta kafin ta tafi


Da kyar ya yarda yace amma kada yadawo ya sameta


Nan suka fito TJ ya kalleta yace kitashi kije kisuturta jikinki amma yace kada yadawo yasameki gidansa yanafadin haka ya wuce abinsa dan dama papa ya riga da ya wuce


Sai bayan sunfito TJ yace wanne hospital zamujene


Ka kaini asibitin daddy shine kawai abinda ya iya fada


Suna isa asibiti lab suka wuce


Maaikatan wajen suna gaisheshi baiko amsaba yace subashi abin gwajin HIV kawai


Damamaki kowa ke kallonsa cikin tsawa ya maimaita masu nan take suka miqo masa


Alluraya dauka ya caka wa hannunsa nan take sai jini yazuba yafara zaman zullumi


Bada jimaba saka mako ya nuna negetalive


TJ dake tsaye agefe yace Alhamdulillah bana fada makaba gashi ai d answer is negetive dafatan hankalinka ya kwanta


Shiru kawai yayi ya miqe dan baijin zai iya magana


Tashin da zaiyi ya yanki jiki ya fadi sumamme


Cikin razana TJ ya sumkuya yana kiransa amma ina baimasan yana yiba


Cikin sauri aka kawo abin daukar marar lfy aka turashi sai emergency


Nan suka bashi taimakon gaggawa har Allah yasa numfashinsa ya daidaita sannan aka maidashi dakin hutu amma dai bai farka ba tukun


In hankalin TJ yayi dubu to atashe suke


Sai a lokacin ya tuna yadauki wayar papa dake aljihunsa ya fara kiran momcy


Bugu uku ta dauka tana cewa hello son


Cikin natsuwa TJ yace ba Alamin bane Tijjani ne


Momcy tace ayya ya khairy da mubeen (dansune wadda bai wuce shekara biyuba)


Lfy qalau umm dama Alamin dinne bashida lfy yanzu haka muna asibiti


Salati momcy ta fara tace mai yasamu papa kuna wanne asibiti


Asibitin daddy muke naje wajensama bayanan


Momcy tace eh yau bai fita ba amma muna zuwa yanzu




Daddy ne ya dubeta yana cewa wai meya sami Alamin din




Cikin damuwa momcy tace nima bansaniba kam




Toh dauko mayafinki muje




Suna zuwa suka shige inda aka kwantar dashi




TJ suka sami yayi shiru yana zaune


Bayan yamasu sannu da zuwa daddy yace wai meke faruwane kam


Nan TJ yafada masu abinda yafaru yace shine dai sanadin sumansa


Sannan TJ yace dan Allah daddy kuyafe masa wlh yayi nadama kuma yanzu damuwarsa qaruwa zatayi matuqar baku yafe masa ba


Daddy yace hakane Allah ya yafemu gaba daya ya kuma kiyaye na gaba


Dik suka amsa da amin


Suna nan zaune ahankali ya fara motsi


Kadankadan idanunsa suka washe yafara ganin komai tass


Aiko yana ganin su momcy sai yafara hawaye zaiyi magana


Daddy ya kamo hannunsa yace kada kace komai Alamin munyafe maka duniya da lahira saifatan wannan yazama darasi agareka


Momcy ta matso kusa dashi tana shafa kansa tace ya wuce papa ka kwantar da hankalinka sannan matakin daka dauka akanta yayi daidai Allah yasaka maka sukuma Allah ya shiryesu


Cikin jin dadi ya yunqura zaune yace nagode daddy na gode momcy nagode sosai


Momcy tace sai mutafi gida tunda yasami sauqi


Daddy yace muje amaidaka gida sai muwuce


Girgiza kansa yayi yace bazan iya zama acikin wannan gidanba ni gida zan koma


Momcy tace toh shikenan kutaho a motar tijjani inyaso sai kuje kadauko kayanka




Ahankali ya miqe TJ na riqe da hannunsa har mota




Momcyma gida suka wuce Sukuma suna zuwa gida basu tarar da juhaina ba


Nan TJ ya hada masa kayansa suka fito sai anan yayi magana yabawa maigai key yace idan tazo kwasan kayanta ya bude idan tagama ya kulle ya ajiye key din awajensa


Suna tafiya a mota ba mai magana acikinsu




Papa ya kwanta ajikin kujera ya tallafe fiskarsa da hannunsa yayi nisa cikin tunani


TJ yace haba man karage tunanin nan mana haka yanzu ai saidai ka godema Allah tunda kagane gaskiya sannan Allah ya toni asirin munafukai




Cikin damuwa yake kallon TJ yace man damuwata fauziyyah tafi qarfina ta wuce tinanina fauziyyah ta nuna batama sanniba yazanyi wlh idan ban auri fauziyyah ba mutuwa zanyi sabida ina sonta sonda bantaba jin inayima wata ya maceba aduniya ashe juhaina ma ba sonta nakeba fauziyyah nakeso na yaudari kaina nan idanunsa suka sake kadawa sukayi jajur


Cikin mamaki TJ yacecfauziyyah kuma a ina ka ganta


Nan yafada masa iya abinda yasani da haduwarsu




Tirqashi shine abinda TJ yafada dan yasan tabbas zaayi haka rananda papa ya komwa fauziyyah da sunan so


Papa cikin damuwa yace komai ya jagulemun man,kyiu wati hai bahaa??? Kyiu kyiu (mai yasa wannan canjin yanayin maiyasa maiyasa) ya qarashe maganar kamar zaiyi kuka


TJ yace komai zaidaidaita kaci gaba da addu a kakuma kwantar da hankalinka


Maganar fauziyyah zamu zauna muga yadda zamu bullowa abin


Da haka har suka qaraso gida...




*****
Fauziyyah kuwa tana wucewa awajen tamanta da shafinsa dan sam baya gabanta sannan tunaninsa tsabar tsanan data masa batayi


Qarfe uku ta iso gida sai dai bakowa su momcy basa nan


Wanka tayi ta daura alwala


Sai datayi sallan laasar sannan tayi kwalliya ta shirya cikin wata doguwar riga yar kanti lokacin da zata dawo nigeria tasayeta


Coppee da milk tasha ado mai kyau


Bata saka dankwaliba sai gashinta data kama da milk ribbon ta fesa turare tafito


Tana zuwa falo taga momcy tadawo tace sannu da dawowa momcy


Momcy tace yawwa kindawo baki samemuba munje asibiti ne papa bayada lfy amma ansallamesa ma


Allah ya sauwaqa shine abinda ta furta albarkacin momcy


Momcy tace naga motarki shine na leqa dakinki kina wanka




Tace eh wlh sai danayi sallah tukun nafito


Momcy tace kinci abinci kuwa


Yanzu zanci ta amsa


Kai daugther bakyason cin abinci ko mai yasa toh kije kici


Toh ta amsa sannan ta wuce dinning taci abinci


Falo ta dawo ta zauna kenan su papa suka shigo


Aiko yana kyalla idonsa akan fauziyyah yaji wani sanyi aransa dan baqaramin kyau tamasa ba


TJ ma haka yake kallonta da mamaki ya kuma jinjina abin lalle akwai aiki agaban abokinsa dan yada ko kanta bata dagoba bare tasan da shigowarsu saima wayarta dataketa latsawa




Momcy tace sannu tijjani Allah yabar zumunci papa kushiga mana katsaya anan


Wajema yasamu yazauna yana cewa aa zansha iska kadan anan


Fauziyyah kuwa kamar ta bar wajen amma sai taga kada ya rainata kawai ta matse abinta


Acikinsu ba maimagana dan shi papa kallonta ma yasashi farin ciki sai yaji tsoro kada yamata magana tama bar wajen shiyasa yaja bakinsa ya tsuke




TJ kuwa shakkar mata magana yake kada shima tace bata ganeshiba




Wayarta ce tafara ringing dubawa tayi taja tsaki axuciyarta ganin no Brr.Nabil ne


Yau batasan iya adadin kiran daya mataba kuma bata dauka ba shikuma bai haqura ba




Harta katse bata daukaba sake kira yayi sai taji shaawar ta dauka kodan tasamu hanyar barin wajen




Momcy kuwa miqewa tayi tace barin turo muku da abinci


Fauziyyah cikin daddar muryarta tadau wayar da sallama jin muryarta mai sanyi yasa papa lumshe idanu.....






โœ๐ŸปFaty Mmn Faty




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ




Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€


Written by Faty Mmn Faty


August, 2017




*Wai maiyasa mutane bakwa uzuri ma mutum ne? Idan kukaji shiru kunsan aidai da dalili kuma dai bazanyi typing ban turoshiba idan kuwa har hakane saikuyima mutum kyakykyawan zato masu cewa wai dan andamu nake masu yanga toh ai mai sauqine tinda ku kuka dami kanku ba nina saku ba, sabida haka saiku daina karantawa tunda ba wanda nasaka saiya karanta dole*




4โƒฃ8โƒฃ
Murmushi yayi sannan ya amsa sallaman


Cikin natsuwa tace ina yini


Fara arsa ya fadada yace lfy dan wani dadine ya lillibesa jin yadda ta amsa da faraa sannan yau har gaisuwa ya samu


Cikin murya mai sanyi yace gimbiyar mata asassautamun mana aidai ko haka na wahala


Juya idanuwa tayi cikin murya mai jan hankali tace namefa
Murmushi yayi sannan yace tinsafe nake kira baki dau wayata ba pls ko shiruma nikiyi amma dai kidauka sai hankalina ya kwanta


Hakan daya fada shiyasa ta wani qayattacen murmushi wadda ya qawata face nata tace ayyah aifa ba dagangan bane ba bani kusane kuma yanzun bagashi nadauka ba


Cikin murmushi yace hakane nagode da kika bani lokacinki amma da zaa taimakamun abani dama nazo gida mugaisa


Shiru tadanyi dan harga Allah bata san takuri amma kuma yau sai takejin nauyinsa sosai


Maganarsa ce ta katse mata tunani yana cewa ya kikayi shiru pls fauziyyah kibani dama na bayyana maki irin sonda nake maki wlh tunda nake arayuwana bantaba jin son wata mace aduniya kamar yadda nake sonkiba kuma ni inkika amince mun insha Allah zan zamar maki alheri arayuwa amma kibani dama domin kitabbatar da maganata


Jikintane taji ya mutu murus kuma ya tuno mata da wasu kalaman da papa ya taba fada mata abaya


Cikin sanyin murya tace bakomai ur always wellcome


Wani dadine ya lillibeshi yace thanks a lot my life insha Allah gobe da yamma zanzo


Cikin murya mai kamada shagwaba tace gobe kuma gaskiya is to early


Cikin rarrashi yace haba my life ai da zafi2 akan bugi qarfe amin haquri dai nazo goben kinji my life


Murmushi mai dan sauti tace ok Allah ya kaimu


Papa dayakai har wuya dan takaici dan tini ya fahimci da wani take waya


Jiyake kamar ya shige cikin wayar yazugamasa rashin mutunci dan wani kishine ya tirniqeshi dan ya fahimci ya samu waje tinda taketa zuba murmushi




Cikin qunar rai ya miqe afusace yayi side nasa


Ganin yadda ya tashi afuce nan danan fiskarsa ta canja hakan yasa TJ ya tashi yabi bayansa


Adaki yasameshi sai safa da marwa dayakeyi acikin daki


TJ yana shiga yace yadai man lfy kuwa lokaci daya kacanza


Cikin damuwa yace badole nacanba kana kallo cin fuskan da fauziyyah tamun


TJ yace haba man kada wannan ya dameka kabi ahankli mana kadaina bata ranka


Cikin fushi yace wani irin kada na damu bayan fauziyyah ta nuna batasanniba then gashi tana hira da wani awaya harda yimasa murmushi haba haba


Ya qarashe maganar kamar zaiyi kuka


TJ yace pls man cool down ur temper komai zaizo dasauqi da yardar Allah ammafa saikabi komai ahankali kuma daki2


Cikin sauri yace kamar me kenan pls tell me abokina wlh ruwan kaina ya qare i dont know what to do


TJ yace zauna kaji yadda zamu bullo wa lamarin


Zama yayi ya paying full attention nasa akan TJ


TJ yace dafarko abinda nakeso dakai kasauqe dik wani abinda kakeji dashi agefe sannan ka cire saurin fushi kadau hakuri kasa ma ranka


Wannan shine matakin farko dan dole sai kayi haquri


Sannan kasameta anatse kabata haquri akan abinda kamata kanemi yafiyarta dan inba hakaba bazaka taba samun fiska awajentaba matuqar tanajin haushinka tana kuma tuna abinda ya faru abaya


Amma idan har tayafe maka ta haqura to komai zaizo dasauqi


Papa yace wlh nima inada niyyar bata haquri saidai bansan ta ina zan fara ba tunda lokacin data gannima cewa tayi bata sanniba kuma wlh abin yacimun rai ya dameni kuma ya dagamun hankali


TJ yace tafada ne kawai sabida tanajin haushin abinda kamata shiyasa nace kafara bata haquri tukunna


Sannan katattara dik wani halin banza ka zubarshi agefe wannan shaye shayen banza da wofin ka haqura dashi dan ba macen arziqi da zataso mijinta da wannan halin


Papa yaja wani dogon numfashi yace hakane kamtunba yauba dama komai ya ficemun arai kuma dayardar Allah nabar shan komai tinda suma basa qaran mutum da komai


TJ yace good abokina naji dadin yadda ka yadda da shawarina da haka harya kwantar masa da hankali kafin yamasa sallama ya wuce


Fauziyyah kuwa cikin qunan rai bayan takashe wayar ta nufi dakinta dan aduniya ta tsani abinda zai tuno mata da papa baran tasashi a idanunta


Washe gari da safe papa baiko tashiba ta wuce hospital abinta sai 3 kafin ta dawo gida


Bayan tayi sallah taci abinci sannan ta tsantsara kwalliya sosai


Wajen qarfe biyar saiga wayar Brr. Nabil kan cewar ya iso fa


Mayafinta ta dauka sannan ta fice


Wani murmushi tasake sabida yadda yamatuqar birgeta


Yana jingine jikin motarsa fara tass , sanye yake cikin wani danyen boyel mai kyau da tsada farare sol wanda sin matuqar amsanshi


Fularsa ta dace da kayan jikinsa haka takalnan qafarsa farare sol, hannunsa daure da agogon azurfa sai kyalli yake


Haka kurum taji ya matuqar birgeta dan harga Allah tana matuqar son mutum mai kamala da shiga ta mutunci


Ahankali cikin takunta mai natsuwa harta qaraso wajensa sallama tamasa cikin siririyar muryarta mai dadin sauraro


Lumshe idanunsa yayi ya bude ahankali dan ta tafi da dikkan tunaninsa kwalliyarta kyan fiskanta uwa uba dirinta sannan daddadan muryanta su suka qara narkar masa da zuciya


Waalaikumussalam barka da fitowa sarauniyar mata


Murmushi tayi sannan ta sunkuyar da kanta ahankaki tace ina yini


Lfy lau ya gida da aiki


Tace dik lfy lau ya naka


Yace well um gaskiya aikinmu ba dadi sai dai shukrah


Tace ayyah Allah ya taimaka, Amin ya amsa


Gyara tsayuwarsa yayi yana cewa yau gani ga gimbiyata dafatan zan samu mazauni acikin zuciyarki


Murmushi kawai tayi batace komaiba dan nauyinsa takeji sosai


Nan yasake gabatar mata da kansa ya kuma tabbatar mata ba dawasa yakeba kuma bashida mata dan baitaba aureba


Cikin gamsuwa da baya nansa tace bakomai amma yabata time tadanyi nazari


Yace badamuwa ya bata kwana biyu ammafa zai ringa kiranta suna gaisawa awaya tace badamuwa


Papa ne ya shigo gida kamar wadda akace ya duba gefensa kawai yaga fauziyyah da wani mutum atsaye sai faman kallonta yake yana murmushi kamar zai cinyeta


Nan take yaji qirjinsa ya buga wani kishi ya taso masa,jiyake kamar yaje shaqesa


Da kyar ya lallami zuciyarsa yayi parkin motarsa ya fito


Cikin gida ya wuce zuciyarsa adagule


Brr Nabil yace to madam nizan wuce naga kamarma na takureki kinyi shiru bakiyin ko magana


Dubansa tayi aa nibaka takurenba kawai dai nagajine yau awajen aiki




Yace eyyerh kishiga gida kihuta toh inyaso da daddre zankiraki


Tace toh nagode sosai Allah ya kiyaye hanya agaida gida


Insha Allahu zasuji bude mota yayi ya miqo mata wata shopping bag mai kyau baby pink colour yace ga wannan bayawa kisha swt


Aa nikam kabarshi nagode


Bata fiska yayi da sigan lallashi yace haba dai pls kikarba badanniba


Yadda ya tsareta da idanuwansa yasa tasa hannu biyu ta amsa tace nagode


Yawwa dear saikin jini yafada yana tada motar


Itakuma juyawa tayi ta nufi cikin gida tana bude qofar falo zata wuce taji anjawo veil nata hakan yasa tayi saurin juyowa


Papa kuwa tunda ya shigo ya gagara shiga ciki dan gaba daya jiyake kamar yaje shaqe wanda yaganshi yana tsaye da fauzinsa


Ganin papa ne yasa ta tsuke fuska tace lfy malam wani abu kake nema


Dubanta yayi da kyau cikin shan mur yace wayene waccan dana ganku tare


Kallon uku saura kwata ta watsa masa tace mene damuwarka da son sanin wayeshi kumama kaidin wayene dazaka tsareni kanamun wasu silly question


Cikin zafin zuciya yace au bakisan niba kikecewa ma




Tace eh banma taba ganinka tunda kadamu kaji wayeshi mijin dazan aurane ar u satisfied now


Yace lalle kinyaudari kanki barin fada maki bakida miji saini kuma ke matata tace sabida haka da kin daiba yaudarin kanki


Wani murmushi tayi na takaici tace Allah ya sauwaqa ni nazama matarka kuma ma kaga mundace dakai ne


Kadubi yanayin Brr. da shigarsa ta mutunci da kamala shine yadace da mijina ba kai wadda ko shigar mutunci baka iyaba dan shayeshaye kawai mazinaci Allah ya mun katangar qarfe tsakani na da kai kuma ni kadaina iqirarin matarka ce bansankaba bantaba saninkaba arayuwata tana fadin haka ta wucesa abinta .........




โœ๐ŸปFaty Mmn Faty




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ




๐ŸŒพ๐ŸŒพ๐ŸŒพ






Budurwar Qauye๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€๐Ÿคท๐Ÿผโ€โ™€


Written by Faty Mmn Faty


August, 2017




4โƒฃ9โƒฃ
Jikinsane yayi sanyi jin yadda take fadan munanan halayensa wadda ashe tana riqe dasu acikin ranta


Yadan jima kafin ya nufi side nasa cikin tunani kalakala


Zama yayi yana nazarin hanyar da zaibi ya wanke kansa awajen fauziyyah


Yanason ya shafe dik wani tunanin dake akansa na halayen banza ta daukeshi a mutumin kirki


Shiru yayi yana nazarin hanyar da zaibi kuma tabbas dole ya dauki shawaran da TJ yabasa idan yanason gane kanta tinda haryanzu tana riqe dashi da abinda ya mata acikin zuciyarta


Cikin sanyin jiki ya dauko wayarsa ya lalimo layin TJ yafa kira


Bayan sun gaisa papa yace TJ pls gobe irin 10am inason karakani wani waje mana


Ok Allah ya kaimu ya jikin dai


Dasauqi sosai thanks saimun hadun


Yana ajiye wayar yafara tunanin gara yafara shigan mutanen kirki wataqil fauziyyah tacanza tunaninta akansa tunda har take kwatance da wani


******
Itakuwa tana wucewa dakinta ta shige zuciyarta namata zafi cos tunawa da irin azaban da papa ya mata abaya


Allah ya qara ta furta afili dan momcy ta bata labarin matar papa


Tunani take wani irin mataki zata dauka akan katsalandan dayakeson ya mata arayuwarta


Shiru tayi kafin ta miqe ta shige toilet dan kanta harya mata nauyi gashi dama a gajiye take


Washegari bayan papa ya fita office ya dan duba patients nasa ten thirty ya fito ya nufi office din su TJ


A office ya sameshi yace ya zamuje ne ko kana da ayyuka mubari sai da yamma


TJ yace ina zamuje ne kam


Papa yace inda kake sayan kaya daka rakani saimuje wajen tailor naka dinki nakeso amun


TJ yace lalle nayarda abokina kacanza


Papa yace wlh jiya fauziyyah tafadamun abinda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login