Showing 237001 words to 240000 words out of 260160 words

Chapter 80 - SARAN BOYE Complete Document by Billyn Abdull .txt

29 Nov 2024

19635

takeba satar kallonsa kawai takeyi tana gulmarsa a zuciya. Tunda ya fahimci kallonsa takeyi shima sai ya kasa ci gaba da yin aikin. Saboda tsabar neman magana ya tura ƙafarsa ya tanƙwaɓe littafin nata ya faɗi. Ya kuma fiske abinsa yaƙi kallonta tamkar bashi ne ya aikata ɗin ba.
Ƙara tsuke fuska tayi tanabin buk ɗin dake yashe a ƙasa da kallo, ɗan bakin kuwa sai motsawa yake amma ta kasa magana. Cike da takaicin daya kumeta ta ɗauki filo ta maka masa a ƙafa harda cije baki.
“Ouch!” ya faɗa yana saurin janye ƙafarsa. “Silly girl!. Wane mugunta ne haka? Mina miki?”.
Harara ta balla masa. batare da tace komaiba ta duƙe zata ɗauki buk ɗinta. Sai dai kuma hannunta bazai kaiba dole sai tazo ta gabansa. Fitowa tai tazo har inda littafin yake. ta ɗauko harma ta miƙe zata koma inda take ya saka mata ƙafa. Sai ko gata a kan cinyarsa ɗare-ɗare.
Mutsu-mutsun ƙwace jikinta ta fara ya saka hannayensa yay mata zobe. Duk yanda taso ta motsa kuwa sai ta kasa. Sake kumbura baki tayi da ƙyau, dan haka kawai ta tuno randa ya taɓa rungumeta a gidansu har Aunty Kubrah ta gansu.
Kansa ya ɗora bisa kafaɗarta yana busa mata numfashinsa. Cikin magana raɗa-raɗa yace, Silly girl, K ba'a zama lafiya da ke sai kinja faɗa ko?”. Wani shegen mintsini ta bashi a cinya wanda ya sakashi sakinta babu shiri. Miƙewa tsaye tai daga jikinsa tana masa gwalo. Yanda ya ɓata fuska kamar zaiyi kuka ya sakata ƙyalƙyalewa da dariya tana nufa hanyar ƙofa. Yatsu biyu ta ɗaga masa, ɗayan hannunta riƙe da ƙugunta tace, “Wannan na yadda buk ne na maka. Saura na......”
Ganin ya miƙe ya sata kwasa da gudu tai ciki batare data ƙarasa faɗaba. Baya ya rufa mata har cikin ɗakin. Nanfa suka shiga zagaye ɗakin. Duk yanda yaso kamata taƙi tsayawa, duk da dai da alama ya barta ne kawai. Ganin yanda yake hakki da nuna matuƙar gajiya ya saka taketa ƙyalƙyala masa dariya tana masa gwalo. Harda yin yanda yara keyi na tsokana. Tana saka yatsunta a kunne da jujjuyasu tana masa gwalo.
Shiko ƙara narkewa yake irin shifa ya gaza kamata. daga ƙarshe ma ya faɗa saman gado yana hakki da faɗin, “Silly girl”.
Zuwa tai har inda yake kwance ta shuri ƙafarsa zata gudu. Dama tarko ya mata. Yako harɗota da ƙafar sai gata a jijinsa. Da dai taga da gaske an kamatan saita fara kukan ƙarya tana kai masa ƙananun duka a ƙirji. Dariya ya farayi ya haɗa duka hannayen ya riƙe tare da juyata akan gadon ya koma kanta. “Wana kama to yanzun?”. Ya faɗa yana busa mata iskar bakinsa a kan idonta dake hawayen ƙarya.
Baki ta sake kumburawa tana matso hawaye. “To bakai ka fara tsokanata ba. Ni dai dana fita ai banma kulaka ba amma ka takaleni”.
Ƙanƙance idanunsa yay da ɗage gira sama. Yace, “Yarinyar nan kin iya sharri. A yaushe na tsokanekin?”.
“Na rantse da ALLAH kai ne ka fara tsokanata, kuma bazan ƙyaleka ba sai na rama”.
“Da gaske?”. Ya faɗa a hankali yana sake matsar da fuskarsa dab da tata har hancinsa na gogar nata. Cikin sarƙe idanunsa cikin nata ya sake faɗin, “Yaushe zaki daina rashin ji ne?”.
Duk yanda taso bashi amsa ta kasa. Saboda goga mata lips ɗinsa da ya farayi akan nata. Tai ƙoƙarin kauda kanta gefe, yay saurin tarewa da nashi yana faɗin, “Uhmyim?. Faɗamin yaushe zaki san kin girma?”.
Ba ƙaramin harbawa zuciyar Aymah tayiba saboda jin a yanda yay maganar, kafin tai wani yunƙuri ya haɗe bakinsu waje ɗaya. Tabbas yau kam tamafi ranar shan chocolate, dan Yoohan ya tabbatarma Aymah a matuƙar zalame yake dason kasancewa da ita. Duk yanda yaso sassauta mata ya gagara, sai da ya ɗora mata sabon salon karatunsa mai wahalar haddacewa.
Gaba ɗaya kukan da taso masama sai ta nemesa ta rasa, sai wani irin tsoro da matsananciyar kunyace da bata taɓa karo da itaba a rayuwarta ta lulluɓe ta. Tunda ta samu ya barta ta tura kanta cikin filos bata sake yarda sun haɗa idanu ba. Sun kwashe mintuna talatin a kwance kafin taji ya sake matsota. Ba ƙaramin bugawa ƙirjinta yayi ba jin ya kwanto a bayanta. Amma sai ta daure tana ambaton sunan ALLAH.
“Akwai matsala fa”.
Ya faɗa a cikin kunnenta yana tura hannunsa a rigarta. Saurin riƙe masa hannu tayi ta zabura zata matsa yaƙi bata space. Dole ta haƙura sai daifa mutuniyar taku tsorone fal cikinta.
“Kin jamin sai nayi wanka, kuma ni ban iya ba”.
“Hu'um. wankan ne baka iyaba? Babu dai ƙyau manya na ƙarya”. Tai maganar da son jan jikinta. Saurin sake ruƙota yayi ya matse. A kunnen nata Yace, “Bafa normal wanka bane, Uncle ya sanarmin a addinin musilinci wanka ya kasu kashi da yawa. *_Fitar maniyyi kai tsaye, ta hanyar jin dadi daga mace ko namiji. 2. Ɓoyewar kan azzkari a cikin farji. 3. Idan mutum ya mutu ya wajaba ayi masa wanka, sai dai in shahiɗi ne. 4. Musuluntar kafiri ko wanda ya yi ridda. 5. Jinin al’ada. 6. Jinin biki (wato jinin haihuwa). 7. Wankan jumu’ah. 8. Wankan shiga harami (da hajji ko da umarah). 9. Wanka ga wanda ya yi wa mamaci wanka, Wankan idi biyu (na zuwa karamar sallah da babbar sallah). 10. Idan mutum ya farfado daga hauka ko
farfadiya. 11. Wankan shiga Makkah.
12. Wanka domin sallar kisfewar wata ko kuma rokon ruwa. 13. Wanka na mai istiha a kowacce sallah. 14. Ga kowanne jima’i an so a yi wanka._* �kinga kenan yanzunma sai nayi fa tunda kin sakani na fitar da......”
Wani irin wuntsilowa Aymah tayi ta dafe masa baki tana faɗin, “Na shiga uku ni Zainab, ni dai wlhy babu ruwana”. Ta fashe masa da kukan taɓara.
Wani mugun dariya ne yaji yana taso masa. Amma sai ya danne da ƙyar dan karya ƙara tunzurata a samu matsala. Hannu yasa ya janye nata dake akan bakinsa. Fuskarta kuma har yanzu tana a ɓoye. “Okay yi haƙuri bake bace nine. Yanzu dai kisan yanda zakiyi dani lokacin salla yayi”.
“To ni ya kakeso in maka?”.
“Ki koyamin”.
Tamkar zata fasa masa sabon kuka tace, “ALLAH ya sani nama fasa zaman hutawar ka maidani Nigeria kawai tunda na warke”.
Shi dai dauriya yaketa yi dan kar yay dariya matsalar tafi haka. yace, “To naji, yanzu dai tashi muje ki koyamin yanda zanyi wankan”.
“Ni dai babu inda zanje, idan kanaso na koya maka a haka kaje kayi abunka”.
“A'a gaskiya, sai dai fa kiyimin practical zanfi fahimtarki. Haka ake malami yayta ragema ɗalibi mudun koyarwa”.
Shiru tayi taƙi motsawa, taki kuma tanka masa. ya tashi zaune yana faɗin, “Okay shikenan, bara kawai na kira Uncle saina sanar masa abinda ya faru daga nan ya koyamin yanda zanyi wank.......”. Zaune ta tashi dingangan ta ɗare masa jiki da danne bakinsa da hannunta tana waro idanun dake cike da ƙwalla.
“Yanzu dan baka da kunya sai ka kira Abbana ka sanar masa wannan abun?”. Hannunta ya ture yana marairaice fuska shima. “To yaya kikeso nayi ne Sweet girl? Kinga dai babu damar nayi salla babu wankan nan? Kema kanki nasan fa sai kinyi”. Ya kai ƙarshen zancensa da kashe mata ido ɗaya. Filo ta jawo ta maka masa a hannu sannan ta sauka masa a jiki tana ƙunƙuni. Duk yanda yaso danne dariyarsa ta gagara sai da yayi abinsa.
Itako data sauka a gadon sai masifa takeyi a ranta tana sharar ƙwallan da babu tantama najin kunya ne. Shi dai Yoohan ganin ya samu yanda ya keso tasowa yayi ya biyota inda ta koma ta zauna akan sofa tana sharar ƙwalla. Ɗaukarta yay cak zuwa bayin tanata wantsala ƙafafu da faɗin ita ya sauketa. Tama fasa koyawar yaje yay Searching a Google ai zai gani. Ko jintama shi bayayi sai da ya direta cikin wajen wankan, zata gudu yay saurin kunna shower ɗin. A take tai musu jalab da ruwan data sheƙo. Ya jawo hannunta ta dawo saman jikinsa. Jin santsin ruwa zai jata ta faɗi dole ta rirriƙesa ruwan na sauka musu a jiki. Da wannan damar Yoohan ya kafe gaban rigarta daya jiƙe da ruwa komai ya fito yanda ya kamata da kallo. Bata fargaba sai da taji hannunsa a wajen. Ƙasa tai da sauri tana ture masa hannu. A ranta kuwa al'amarin sake firgitata yakeyi. ƙara ƙarfin shower ɗin yayi, hakan yasata tilas ta sake miƙewa tana sharce ruwar dake sakko mata a fuska ko gani da ƙyau yana neman hanata. Numfashi ma takai da baki take firzarwa. Shi kansa ruwan ya masa yawa. Amma saboda karta gudu yay haƙuri yana saka hannu yana sharcewa kamar yanda takeyi itama. Sai da ya tabbatar sunyi jagab sannan ya kashe shower ɗin. Ya koma hanyar ƙofar wajen wankan ya tsaya. A mamakinta sai gani tai ya fara cire rigarsa. Ƙasa tai da kanta gabanta na faɗuwa. Ganin wandonsa ya saɓulo ƙasa ta ƙara kiɗimewa. Da sauri ta juya bayanta. Hakan ya bashi damar matsawa ya manna bayanta da ƙirjinsa.
“Karki zama malama mai yima ɗalibanta rowar ilimi fa”. Yanda yake maganar yana yawo da hannunsa akan cikinta sai ya nema sake susutata. Tama rasa tunanin da zatayi akan wannan al'amarin nasa mai wahalar fashin baƙi. Tanaji tana gani yay amfani da ƙarfinsa wajen zame mata riga da wandon jikinta. Sai dai fa duk yanda yaso cire harna cikin taƙi yarda sam. daga ƙarshe ma sai ta saka masa kuka. Ƙyaleta yayi ganin dai ankai inda ma baiyi zatoba. A haka ta fara ƙoƙarin koya masa wankan duk dan ta samu ta kuɓuta daga wannan dabaibayin da yayma rayuwarta baki ɗaya.
Sai da tai nisa a koyawarne ta fahimci ya iya, dama ashe kawai danya bata wahala da kallar mata jikine ya sashi cewa ta koya masan. Wannan haushin ya sakata harya ƙarasa wankan ya fita ya barta dan taki yarda tayi ita tana antaya masa harara. Duk da ƙaryar datai masa na cewar babu wani wanka daya hau kanta yana fita kuwa sai da tayisa. Dan duk wautarta tasan abinda takeyi tunda tanada ilimin addini. Aiko dai ansha ƙunƙuni. Tana cika baki da iska ta miko hannu akan ya bata Bathrobe da towel, dan yana a bayin bai fitaba.
Hand dryer ɗin hannunsa ya ajiye. Ya ɗauki rigar wankan ya kai mata sai dai babu towel. Hannun nasa ma sai da ya sha harara sannan ta amsa. Ganin babu towel ɗin kuma taita ƙunƙuni. Koda ta fito kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kanta ganin daga shi sai towel iya ƙugu zuwa gwiwa. Shiko gashinta dake ɗigar ruwa yabi da kallo. A cikin ransa dariya ya sanya mata yana faɗin, ‘Yarinya ashe kinada lafiya tunda saƙona ya isa inda na aikashi?’. A fili kuwa sai ya fuske abinsa. Tai saurin ɗaukar towel ta naɗe kanta wai dan karya gani.
Ƙarasa hidimarsa yayi ya fito ya barta. Koda ya fito mai ya shafa yay shiri cikin ƙananun kaya. Baƙin wando da pitch color ɗin shirt mai dogon hannu. Yana fesa turare ta fito.
“Kiyi shirin fita”. Ya faɗa yana ajiye turaren.
Bata tanka masaba. Tai tsaye har sai da ya matsa a wajen sannan ta buɗe akwatin nasu ta ɗauki jallabiya ɗaya. Bayi ta koma ta sanyo sannan tazo ya jasu salla. Suna idarwa yace ta ƙarasa shirin yana zuwa.
Fita yay, ita kuma ta miƙe ta shafa mai, da ƙarasa kimtsawa. Tana gamawa kuwa yana dawowa. Zata fara feshi da turarensa ya amshe yana faɗin, “Silly girl ya isa haka dan ba tallanki nazo yima Austrian ba”.
Ita dai bata tanka ba. Bakuma ta yarda sun kalli juna ba dan wannan fushin da takeyi tsabar jin kunyarsace kawai ke ɗawainiya da ita.
Tsaf suka fito abinsu gwanin sha'awa. Tamkar ka sacesu ka gudu. idan ka gansu sai ka ɗauka ƙaramar ƙansawarsa ce ma. Yau dinma bata cuci kantaba sai da taita kalle-kalle har suka fito ƙaton reception ɗin hotel ɗin. Zuwa yay yayi signing kamar yanda dokarsu take. Daga haka yaja hannunta suka fito............✍




ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗


Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋


Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.




[6/24, 3:26 PM] Black Gal👩🏾‍🦱🥰: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.




No. 61


...........Da Solomon sukaci karo a jikin wata dalleliyar mota tsaye. sai baturen dake cikin Uniform ɗin hotel ɗin. Da girmamawa Solo yake gaisheta da sake tambayarta ƙarfin jiki. Cike da takaicin zamantowarsa tamkar jelar Yoohan ɗin ya sakata amsawa a taƙaice. Yoohan ya buɗe mata da kansa ya taimaka mata ta shiga. rufewa yay, ya zagaya inda baturen ya buɗe masa shi kuma ya shiga. Baturen ne ya shiga a matsayin driver, Solomon kuwa gefensa. wannan abu ya zafi Nu'aymah a rai. Kenan duk inda mijin nata yake dole wannan basamuden sai ya kasance da shi?. Dolene tasan matsayin wannan bibbinin kuwa. Galla masa harara tayi lokacin da drivern ke harba motar a titi suka fice daga harabar hotel ɗin.
Idanu Yoohan ya lumshe da jingina kansa da kujera. Ya saki ajiyar zuciya, a ransa yana ayyana ‘hakan shine kawai mafita a gareni. idan ba ɗan fitar mukaiba bazan iya barin yarinyar nan ba. komai zan iya aikatawa kamar yanda zuciyarsa ke bani ƙwarin gwiwar game da ita’.
Nu'aymah dai ta fahimci motar hotel ɗince ya ara. Sai dai batasan ina suka nufaba. Dan haka ta ware idanu da ƙyau tana sake kallon tsarin garin na Vienna da ya gama haɗuwa da ababen more rayuwa kala-kala. Duk da ranta cike yake da taikaicin tafiya tare da Solomon, kai harshi kansa Yoohan ɗin haushinsa takeji akan Solo.
Sun fara zuwa wani haɗaɗɗen wajen Saloon, bata fahemci hakanba kuwa sai da suka shiga ciki. Ta kallesa tana yamutse fuska, “Mi zamuyi anan?”. Kallonta kawai yake shidai fuska a tsuke shima. Dan shi kaɗai yasan a halin da yake ciki. Sai dai yana mamakin miya ɓata mata rai haka? Ya fahimci tun fitowarsu cikin hotel ɗin wajensu Solo ta ciskule fuska, saɓanin farko da kunyarsace kawai tattare da ita.
Bai bata amsaba, sai ma ma'aikatan wajen da sukazo musu tarba ta mutuntawa. Da Garman language yay musu bayanin abinda suke buƙata. Hakan yasa Aymah bataji komaiba. Saima mamakin dama yanajin yaren data fahimci mafi yawan ƴan garin sunfiyi kenan?. Bata da mai bata amsa, sai jan hannunta da ma'aikaciyar tayi zuwa sashen mata. Binsu yay har ciki, shine ya zaɓa duk abinda za'ai mata. Nu'aymah dai ta zubama sarautar ALLAH ido tana kallonsu. Shiko yaƙi yarda su haɗa idon. Yana gama zaɓa ya biyasu kuɗinsu. Sai shi kuma ya nufi na maza dan yana buƙatar gyaran fuska da yankan farce.
Haushi ya hana Aymah yin magana har aka fara wanke mata kanta. Ganin babu kitso dai yasa bata damuba. An mata wankin ƙafa da gyaran farce, sannan aka kaita wani ɗaki wai na gyaran jiki ne. Nu'aymah dai taga abinda ya girmeta, har tsoron shiga waɗan nan injina ta ringayi, a ganinta idan aka ɗauke wuta mutum na ciki kuma ai shikenan labarinsa ya ƙare. ‘Kai wannan mutumin ba kawoni yay kuwa a markaɗeniba ma?’ ta aiyana a ranta tana ƙunƙuni da hausa. Su dai ma'aikatan ba jinta sukeba. Hakan yasa suketa aikinsu kawai. Anyi mata gyaran jiki na musamman da ita kanta tasan eh ta gyaru ƙwarai da gaske. Aka kuma kaita wani waje wai tausa nankuma za'ai mata. ‘Babbar bala'i’ ta faɗa a fili cikin suɓutar baki. ‘Amma wannan mai jajayen kunnen ya gama sakamin rayuwa a gaba. Yoni nace masa ina buƙatar duk wannan ne ko mi?’. Haka taita zuba mita ana mata tausa. gashi kuma sai faman lumtse idanu takeyi alamar tanajin daɗin jikinta. Bayan kammala tausan an maidata wajen gyaran jiki, daga haka aka ƙarasa gyara mata kanta. Haɗaɗɗun wando da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login