Showing 147001 words to 150000 words out of 260160 words
Chapter 50 - SARAN BOYE Complete Document by Billyn Abdull .txt
ya koma baya ya sake zubewa a gadon yana ambaton addu'ar da Manager Hamza Ibrahim da a yanzu suka sake zama abokai sosai ya koya masa. Ita ya shiga maimaitawa a cikin ransa. Cikin amincin UBANGIJI a hankali yaji ƙirjinsa ya fara rage nauyi, sai kuma wani irin barci ya fara fisgarsa a hankali.
Gaba ɗaya papa ya haukace a gaban abokansa da ƙanninsa. Dan suna a tare lokacin wajen wani meeting ɗinsu na manyan ƙauyensu, dan dama yaje ƙauyensu ɗinne tun jiya da daddare saboda meeting ɗin mai muhimmanci ne suka shirya yi.
Uncle Godwin ne ya kama hannunsa ya zaunar da shi yana faɗin, “Hah Friend. Please calm dawn ”.
Papa ya furzar da wani zazzafan huci jikinsa na wani irin tsuma, ya doka sandar hannunsa a ƙasa yana cizar lip ɗinsa na ƙasa da masifar ƙarfi. Da turanci yace, “Tayaya kake tunanin hankalina zai kwanta Godwin? Ko nauyin faɗamin Yoohan baijiba wai zai auri ƴar arewa, ɗiyar hausawa masu sallah?”.
Da sauri Uncle Mike yace, “Ah!Goshpower wani lokacin kana abu kamar ƙwaƙwalwarka baya aiki da kyau. kai nefa ka sanar min yaron nan ya sanar maka yana da manufa akan duk abinda ya keyi. Mizai hana ka amince masa ya aureta ɗin. Muma wata damace tazo hannunmu akan mahaifinta.....”
A fusace papa yace, “Sai kuma akace muku da ɗana kawai zamu iya samun wannan damar? Salon suje su maidashi mai salla, to ni......”
Saurin ɗaga masa hannu wani da suke kira Chief yayi da sauri. Ya juya maganarsa zuwa yarensu da ayanzuma bilynku bataji ba😪. Magana ya farayi kamar zai haɗiye harshenshi cikin maida gaba ɗaya hankalinsa ga papa. A mamakina kuwa sai naga gaba ɗaya papa ya nutsu yana saurarensa tamkar ƴan uwansa. A hankali na ga fushin papa ya fara sauka daga fuskarsa. Saima ya koma sakin wani mugun murmushi yana gyaɗa kai. Kafin ya miƙe cike da wani irin farin ciki ya rungume Chief ɗin. Suma sauran duk tsantsar farin cikinne ya bayyana a fuskokinsu. Da alama dai shawarar Chief ta zauna da ƙyau a zukatansu.
Tashi papa yay ya shiga neman Number Yoohan. Sai dai kusan kira goma bata shigaba. Canja akalar kiran yay ga Solomon.
Yoohan na kwance har yanzu a gadon Solomon yay knocking. Bai motsaba balle ya amsa masa. Shikuma Solo jin yayi har kusan sau huɗu babu amsa sai kawai ya tura ƙofar ya shigo. Ƙarasawa yay inda Yoohan ɗin ke kwance cike da tsoro da girmamawa yace, “Am sorry sir. Boss ne yace na baka waya”. Kamar Yoohan bazai tankaba ya watsar da shi. sai kuma zuwa can ya miƙa masa hannu alamar ya basa wayar. Yana bashi ya fice abinsa. Yoohan ya ɗora wayar a kunne batare da yayi magana ba.
Cikin sanyin murya papa daga can yace, “I am so sorry my son. Raina ne kawai ya ɓaci dan ina tsoron su canja min kai su cuceni. Amma kuma sai nayi tunani da sake tuna bayanin da kaimin kwanaki sai na fahimci kaima ba ƙaramin abune mai muhimmanci zai saka yin hakan ba. yanzu yaya kaso ayi to?”.
A karon farko Yoohan yayi wani munafukin murmushi ya kai hannu ya shafi sumar kansa har zuwa sajensa. Idanunsa ya buɗe a hankali ya sauke bisa frame ɗin da akai adon ɗakin hotel ɗin da shi. Magana ya farama papan nasa da yare cikin taushin murya.
To su dinɗin dinkum balkisu saina koma gehe kawai ina zare idanu dan anzo dai-dai wajen. Turancinma da yaya nake haɗosa nake masa fassara🙄😜🚶🏻.
Papa da Yoohan sun ɗauki lokaci mai tsaho suna waya. Dan har sai da na ƙosa kafin su kammala. Yanda naga Yoohan ɗin ya ɗan rage buyagin nasa ne ya sakani fahimtar maybe har sun gama tsara wani abune.
★★★★★
Kusan ƙarfe tara na dare Nu'aymah ta farfaɗo. Dr Sa'ad dake tare da ita dan duty ɗin dare ne da shi yay azamar kiran Dr Yoohan da har yanzu yana a hotel ɗin bai kuma waiwayar asibitin ba.
Cikin kuwa mintuna ƙalilan ya shigo asibitin. Tsabar yanda ransa ke a jagule sai ya toshe idanu da baƙin Glasses da yay masifar sake fiddo masa ƙyawun fuskarsa da kwarjinin hasken musilinci dake mamaye da shi. Tunda ya shigo asibitin baiyi magana da kowa ba. Ko gaidashi da Nurses suke da sauran ma'aikatan hannu kawai ya dinga ɗaga musu kansa a ƙasa ya rufe rabin fuskar da p-cap bayan glasess ɗin. Shi dai Solomon na biye da shi kamar jela.
Ɗakin da Nu'aymah ke a kwance ya tura a hankali ya shiga da sallama ƙasa-ƙasa. Dr Sa'ad da Nurses guda biyu dake a tare da shi suka amsa suna ɗagowa. Da girmamawa Nurses ɗin suka risina suna gaishesa. Batare da ya amsa musu ba suma ɗin ya ɗaga musu hannu kawai. Kafin ya miƙama Dr Sa'ad hannun sukayi musabaha shi kuma.
A hankali ya juya kansa zuwa ga sashen da kan Nu'aymah ya ke. Ya ɗan ranƙwafa kanta ƙaɗan ya janye wani igiyan na'uran dake a gefen kanta gab da kunne.
Yanda ƙamshin turarensa ya buga mata hancine ya saka ƙirjinta harbawa. Buɗe idanun nata tayi da ƙyar saboda bala'in nauyin ciwo da sukai mata. Dai-dai Dr Yoohan ya dubeta shima yana ƙoƙarin zare glasess ɗin idonsa. Kallon ido cikin ido sukaima juna, duk da ita ɗin dishi-dishi take ganinsa hakan baisa ta gagara ganesa ba.
Wani irin juyawa kanta ke mata, daga ciki tanaji kamar ana karta mata ƙarfe, zabura tayi, ta yunƙura zata tashi Sai kuma tai saurin dafe kan nata tace, ‘Aushhh kaina!’.
Yoohan da shima zuciyar tasa ke wani irin harbawa, da sauri ya wani ɗauke idanunsa daga kanta cike da basarwa, tamkar bai fahimci halin da take a ciki ba.
Yanda jikinta ke wani irin ɗan karkarwa ga kanta data riƙe da duka hannayenta tana jujjuyawa ya saka Nurses ɗin nufarta da sauri tare da Dr Sa'ad. Yoohan dai na tsaye baiko motsaba. Sai dai yana kallonsu ne ta ƙasan ido. Yanda duk sukaso Nu'aymah ta nutsu hakan ya gagara, dan ganin Yoohan ɗin ya sake dawo mata da komai cikin memory ɗinta, wanda hakan ke mata barazana cikin kanta tamjar ƙwanyarta zata tarwatse.
“Ku barta” ya faɗa a hankali tamkar ba shine yay maganar ba. Baya Nurses ɗin suka ja domin cika umarninsa, amma tausayin Nu'aymah fal ransu. Dr Sa'ad kam sai ƙoƙarin son riƙo hannun Nu'aymah data riƙe kanta da shi gam ya keyi. A bazata yaji an riƙe masa hannun lokacin da yake gab da ɗorasa saman nata..............✍
Ni dai nace ‘Hummm’.😶 inji mai tsoron gulma.
__________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
I'm on Instagram as yerwaincense_and_more. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=ayfowzb2ah8k&utm_content=6k8ur6p.
*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
*Ga breakfast nan aci a hankali har dinner ɗin gobe idan ALLAH ya kaimu sai ku ɗumama😎😁⛹🏻♀️*.
No. 40
............Ƙarfe sha ɗaya na dare Yoohan da Solomon suka bar kano zuwa Abuja. Tafiyar da bata kulle awa guda ba jirginsu ya sauka. Sun iske guards ɗinsa tuni suna a airport ɗin ma, dan haka basu ɓata lokaciba wajen wucewa gida.
Kamar yanda yay tsammani ya iske gidan nasu shiru, alamar duk sun kwanta, madam Chioma kawai suka iske a falo zaune cikin kwalliyar riga da wando da sukai mata ƙyau sosai. Yanda ta zubamasa ido haka shima kallonta yake babu yabo babu fallasa. Cikin takun nasa ya ƙarasa gareta, itama sai ta miƙe tana mai buɗe nasa hannayenta alamar yazo gareta.
Gabanta yaje ya tsaya batare da ya shiga jikin nata yanda ta buƙata ba. Ya kamo hannunta ɗaya yana ɗan shagwaɓe fuska kaɗan. Cikin sanyin muryar da tabbatar da agajiye yake, da yarensu yace, “Mom na girma ni”.
Ɓata fuska tayi itama cikin wani yanayi, muryarta na harɗewa wajen fita tace, “Please my boy”. Karan farko ya saki lallausan murmushin da ya nema sumar da ita a wajen. Ya ɗora hannunsa na haggu saman tattausan sajensa ya shafa yana ɗan kauda idonsa daga gareta zuwa ƙafar benen dake a falon inda Miracle ke tsaye cikin kayan barci, ƙirjinta rungume da madaidaicin teddy bear ta wani kafesa da idanu tamkar zata haɗiyesa ta huta.
A hankali ya janyesu gareta yay wani luuuu da su kamar zai rufe sai kuma ya buɗesu yana sakin hannun Mom yaja baya. Hannayensa duka biyu ya ɗaga mata da faɗin “Sweet mom gudnit”. Kafin tace wani abu harya fara hayewa upstairs ɗin da ɗan sauran kuzarinsa batare da ya sake duban Miracle ba ya raɓa ta gefenta ya wuce.
Su duka da kallo suka bisa harya ɓacema ganinsu, mira ta share ƙwallar data cika mata idanu ta juya da gudu zuwa ɗakin barcinsu ita da joy. Wata malalaciyar harara Mom ta raka Mira da ita. Kafin ta taune lip ɗinta na ƙasa da ƙarfi zuciyarta na ƙuna fiye da yanda gangar jikinta ke tsuma.
Yoohan daya iske ɗakinsa kamar yanda yay fata komai fes bai wani zauna ba ya shige toilet. Bayan wasu mintuna masu ɗan tsaho ya fito jikinsa na ɗigar da raɓar ruwan wanka. Da sauri yaja ya tsaya ganin Mom zaune bisa sofa. A ɗan daburce yace, “Mom lafiya kuwa?”. Saurin ɗago idanunta dake akan wayarta tayi ta dubesa, dai-dai shi kuma yana ƙoƙarin saka farar t-shirt ɗin daya ɗauka. Miƙewa tai ta nufosa tana wani sakin tattausan murmushi, ta ɗauka ƙaramin towel ɗin daya fito da shi a hannu ta nufi sumar kansa alamar zata tsane masa gashinsa dake ɗigar da ruwa. Da ɗan hanzari yaja baya kaɗan yana tsuke fuska.
“Mom!!”
Ya faɗa aɗan tsawace. Jin a yanda yay maganar ne ya sakata tsayawa cak daga yin abinda tai niyya.
Da ɗan shagwaɓa yace, “Haba Mom! Miyasa kike son maidani baya ne kullum? Nifa ba Abraham bane ko Victoria Please”.
Ƙanƙance mayatattun idanunta tayi tana ɗan matsosa, cikin muryarta dake wani irin rawa tace, “Kaine kake ɗaukar kanka babba John! Ita uwa ɗanta kullum yaro ne a gareta. Ina sonka Yoohan fiye da yanda kake tunani, kai ɗin farin cikinane fiye da sauran ƙannenka”.
Ɗan lumshe idanu yay ya buɗe a kanta, ya ɗan sassauta muryarsa da fuskarsa dake a tsuke. Dan shi harga ALLAH bai fassara maganarta da komaiba face soyayyar ɗa da uwa. “Na sani Mom, nima ina sonku da ƙaunarku fiye da zato ke da papa da ƙannena. Amma Please ki ringa rage cewa zakimin wasu abubuwan. Bama ni ba ko Abraham ɗan shekara goma ba komai zaiso kimasa ba yanzun. Mun rigada mun girma, hidimar da kikai mana muna ƙanana ta wadatar uhmyim?”.
Yanda yay maganar cike da lallashi ne ya sake narkar da ita a wani irin yanayi mai wahalar fassara. Ta buɗe baki zatai magana aka turo ƙofar aka shigo. Gaba ɗayansu ƙofar suka kalla. Papa ne cikin kayan barci da alama ma ya fara barcin tashi yayi.
Cikin ƴar shagwaɓa Yoohan yace, “Yauwa papa Please kwashi matarka ku wuce dama ta sakani a gaba nikam”.
Papa dake bin Mom da wani irin kallo ya haɗiye yawu da yin guntun murmushi yana maida idonsa akan Yoohan ɗin da ya sake ƙwaɓe fuska. Muryarsa da alamun barci ya tashi yace, “Yaushe ka dawo?”.
Mirror Yoohan ya nufa yana faɗin, “Yanzun nan babu jimawa nazatama baka gida ai”.
Komai papa bai ceba ya kama hannun Mom suka fice yana faɗin, “Huta abinka sai da safe”. Suna fita Mom ta fisge hannunta da ga na papa tana kumbura kumatu. Baice mata komaiba yay gaba abinsa dan jin Yoohan yana sakama ƙofarsa key. Yasan ko mi zatayi bazai sake buɗe mataba kuma. A ransa kuwa mamakin yanda Matar tasa ke nuna tsananin so ga ƴaƴansu yakeyi. shi bai taɓa ganin mahaifiya mai ƙulafucin ƴaƴa irin Madam Chioma ba.
Yoohan kam koda ya kammala kimtsawa falo ya fito ya haɗa tea ya koma bedroom ɗinsa. Zaman sha yay zuciyarsa da tunaninsa duk na wajen Nu'aymah. Ji yay yana buƙatar sanin yaya take yanzun, dan haka yaja wayarsa ya nema Dr Aysha a karo na farko a rayuwarsa.
Ita kanta Dr Aysha ba ƙaramin mamaki tayi ba ganin kiran Dr Yoohan a wayarta. Abinda bai taɓa faruwa ba. Jikinta har tsuma yake wajen saurin ɗauka. Ta kara a kunne murya a narke tace “Hello! Doctor good evening”. Maimakon ya amsa mata sai cewa yay “Assalamu alaiki”. Idanu taɗan zaro waje jin sallama yayi, saɓanin da da sai dai ya ce maka hii. Itafa dama gaba ɗaya a wannan zuwan nasa abubuwa da yawa taga idan yanayi tamkar ba shiba. Shekaranjiya ma har ganinsa tai kamar ya fito massallaci......
Sallamar da ya sake maimaita matace ta katse mata tunaninta. “I'm sorry sir. wa'alaikissalam. Kunje lafiya?”.
“Humm”
ya faɗa a taƙaice yana lumshe idanu da kai kofin tea ɗin bakinsa. Sai da ya kurɓa ya haɗiye kafin yace, “Ya yarinyar nan ta farka ne?”. Ta gane Nu'aymah yake nufi, dan ita kaɗaice patient ɗin daya kwantar dai. Cikin sanyaya muryarta tace, “A'a har yanzu tana barci, amma an saka mata drip ɗin daka ce ɗin yanzun babu jimawa”. “Okay night” ya faɗa a taƙaice da yanke wayar batare da ya ƙara komai ba.
Nannauyan ajiyar zuciya Dr Aysha ta sauke tana ɓata fuska kamar zatai kuka. Akan laɓɓanta ta furta, ‘Ɗan wulaƙanci’.
Oho baimasan tanai ba, dan shi tea ɗinsa ya ƙarasa sha kafin ya miƙe ya nufi toilet. Alwala yayo. Ya saka sallayarsa sabuwa da baba malam ya bashi ya tada salla kamar yanda ya keyi yanzu a kowanne dare. Idan har ya samu dama yakan fara daga ƙarfe ɗaya ko biyu, zuwa uku sai yaɗan kwanta kafin asuba.
*_WASHE GARI_*
A gidan su Nu'aymah kuwa a safiyar yau bayan kammala breakfast ɗunguma sukai asibiti suka duba jikin ta, kamar ko yaushe basu duka aka bari suka shigaba. Baba malam ne kawai dasu Abba Musbahu. Sai hajjo da Ananah. Umm dama batajeba dan tanason zuwa gidan Gwaggo mahaifiyarta. Daga can zata biya asibitin tare da Gwaggon.
Basu jima a asibitinba suka dawo gidan, baba malam da ƙannensa uku da hajjo sai Ananah a falon hajjo suka yada zango domin tattaunawa. Sunyi zaman kusan awa guda sannan Abba Musbahu yay kiran Abdallah da Naser a waya. Ba a rufa mintuna biyarba kuwa sai gasu dan dama duk suna gida. Zama sukai inda Ananah ta nuna musu kowanne kansa na a ƙasa..
Fuskar baba malam a ɗaure ya dubi Abdallah, “Abdallah zan fara ta kanka, dan karka zata shirun da mukai maka kamar mun ƙyalekane bisa abinda ka aikata mana. Gani ga ƴan uwana ga Hajjo harma da Ananah. Inason ka faɗa mana dalilinka na aikata abinda ka aikata. Shin bamu da daraja a idanunka ne mu da muka baka auren yaranmu kokuwa raini ne dan kaga ka girma?”.
Cikin sauri Abdallah ya ɗago yana kallon baba malam ɗin da girgiza kansa. “Wlhy sam ba haka bane ba Abbah. Kuna da darajar da bayan MANZON ALLAH babu mai ita a idona a duk faɗin duniya sai ku”.
“Ban yarda ba Abdallah, inda ace munada wannan darajar da bazaka aikata abinda kayi ba. Mu aura maka yara ka sake mana su akan wani banzan dalilinka mara amfani”.
“Abba ku gafarceni, amma wlhy ina son Nu'aymah, son da zaku iya rasani idan kuka hanani mallakarta. dan ALLAH a wannan karon karkuce mani a'a”.
“Ba maganarta nai makaba ni ai, maganar yarana daka saki