Showing 165001 words to 168000 words out of 260160 words

Chapter 56 - SARAN BOYE Complete Document by Billyn Abdull .txt

29 Nov 2024

19616

Haka suka fita a jere ana bin amare da addu'ar tafiya a sa'a. Dama mafi yawan ƴan biki na kusa duk sunata guduwa suma. Zuwa goma na dare sai hayaniyar gidan ta ragu sosai, wasu sunyi barci, wasu sun tafi.



★★★


Su baba malam sun fara miƙa Hajarah ne dan itace ƙarama. Gidanta mai ƙyau da tsari a anguwar GRA, kowa ya yaba da addu'ar zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba. Sun sami tarba ta mutuntawa daga dangin ango su bakwai da sukazo tarbar amarya daga can gidan surukan Hajarah. Kasancewar sunsan dokar su baba malam ɗin suma cikinsu harda maza uku. Bayan sun ɗan zauna a falo akai addu'a baba malam ya kama hannun Hajarah har cikin Bedroom ɗinta ya kaita, zaunar da ita yay a bakin gado yay mata addu'a da saka mata albarka. Ya juyo zai tafi ta riƙe hanunsa. Tsayawa yay tare da juyawa jikinsa duk a sanyaye yana dubanta. Haka yake shi, yanada son yara, shiyyasa har ƴayan ƴan uwan nasa ƙaunarsu yake har cikin ɓargonsa. Duk kuma sanda yay irin wannan rakkiyar sai yayi ƙwalla dajin ɗacin rabuwa da yaran nasu ta dalilin aure ƙanin mutuwa.
Hajarah data buɗe fuskarta ta share hawayen dake silalo mata. Cikin dasashshiyar muryarta tace, “Abbah dan ALLAH inason in roƙeka wani abu”. Kansa ya jinjina mata, yace, “Komi kikeso zan miki inhar baifi ƙarfina ba Hajarah, dan haka faɗamin koma miye kinji”. Sake share hawayenta tayi tana jinjina masa kai. “Abbah dan ALLAH idan yah Abdallah yace bazai maida aurensa da su Adawiya ba karku takura masa”. Jimmm baba malam yay yana kallonta. Sai kuma yace, “Uhm Hajarah miyasa kika buƙaci hakan? Bayan kinsan shi ɗin mai laifine”. “Abbah zan faɗa maka dalilina amma ba yanzu ba, dan ALLAH kuyi mani wannan alfarmar, suma su Abba zan kirasu duk na roƙesu har Hajjo”.
Numfashi baba malam ya ɗan sauke, sai kuma yace, “Karki damu zan duba na gani, kibar kukan nan haka karya saki zazzaɓi. ALLAH ya baku zaman lafiya”.
Daga haka ya fita ya barta tana cigaba da rabzar kukanta.
Daga gidan Hajarah saina Kubrah. Itama dai gidan ya haɗu masha ALLAH. Sai dai ita tana da abokiyar zama harda yaranta uku. Amma kowa da sashensa dan gidan babbane. Itama dai an tarbesu da mutuntawa. Baba malam kuma ya rakata har nata ɗakin ya ƙara mata addu'a sannan ya fito suka wuce gida kowa aka barsa da halinsa kuma.


____________________


A ɓangaren Yoohan kam tunda suka baro gidan su baba malam sai ya koma Hotel ɗin da su papa suka yada zango. Babu yanda baba malam baiyiba akan su sauka a ɗaya daga cikin gidajen baƙinsu amma papa ya ƙi fir. Wajen ɗaurin aurenma da yake jirgin 12 suka shigo suna isowa ana idar da sallar juma'a, hakan yasa saida ma aka ɗan jirasu kafin su iso wajen ɗaurin auren daga airport. Yoohan ne kawai yazo tun goma na safe. Bayan an ɗaura auren aka ɗunguma har dasu hall ɗin da su baba malam ɗin suka tanada domin gudanar da walimar cin abinci. Anan akaci aka sha cike da farin ciki. Babu wanda zai kalli baba malam da papa yace akwai wani abu na rashin jituwa a tsakaninsu. Suma su papan sun sake sosai a cikin mutane bazaka taɓa cewa ga daga addini ko ƙabilar da suka fito ba. Musamman ma daya kasance a cikin manyan mutanen ƴan ɗaurin aure akwai waɗanda suke da alaƙa dasu sosai musamman ma ƴan siyasa. Wasuma papan ya sake gayyatarsu bayan gayyatar da baba malam yay musu.
Bayan an kammala walimar ne mafi yawan baƙin suka kama gabansu, su kuma su papa da tawagarsa suka nufi hotel bayan sunƙi amsa tayin baba malam. Hakan yasa yanzun acan Yoohan ya iskosu. Sai dai kasancewar jirgin ƙarfe bakwai da rabi zasu bi zuwa Abuja duk ya iskesu sun fito shi ma suke jira. Basu wani zauna zaman ɓata lokaci ba duk suka shiga motocinsu. zasu kaisu airport ɗinne su dawo su kwana da safe suma su ɗauki hanya. Dama da safe suka taho kafin su papan.
Ko mintuna goma cikakku basuyi da zuwa airport ba jirginsu ya lula birnin tarayya abuja. Inda a canma dai ɗaukarsu akazo akayi. Abokan papa kowa ya nufi gidansa, papa da Gebrail, Richard, Joseph, Godwin, Osin, Uncle Marcel, Uncle Anthony, kuma suka nufi gidan papan. Sai Solomon jelar Yoohan😂.
Sun iske gidan a hargitse da rikicin da suka bari su Mama Debora nayi akan auren Yoohan ɗin. Faɗa mai lasisi sosai akasha tsakanin tsofin biyu. Kuma duk akan sufa basu yarda jikansu ya aure bahaushiya mai salla ba. Momy da papa ya gama sanar mata komai akan manufar auren tanata ƙoƙarin fahimtar da su duk da kuwa jitake kamar tafi kowa shiga tashin hankali, amma sun ƙi fahimta. Sai kiran dangi suke na nesa a waya suna sanar musu. Miracle kam yanke jiki tayi ta faɗi a sume dama tunkan su Yoohan su wuce. Akace kuma ya dubata ya tsallake yay ficewarsa batare daya ko tanka musu ba.
Hakan daya aikatane ya sake fusata kakanninsa sabon wutar bala'i ya ƙara ruruwa. Sai asibiti aka kai mira bayan wucewarsu ɗaurin auren.


Tunda Yoohan ya shigo idonsa ya sauka akan kakannin nasa sai ya sake tsuke fuska fiye da yanda take. Ɗauke kansa yayi ya nufi upstairs duk da yaga yanda suka miƙe zumbur suna kallonsa cike da wutar masifa.
Cikin yare, mama Debora ta shiga ƙwala masa uban kira kai kace gidan zata fasa. Ko waiwayensu baiyiba ya buɗe ƙofarsa ya shige bayan ya amshi babbar rigarsa a hannun Solomon dake biye da shi a tsorace. Ruf ya rufe ƙofar ya murza mata key yama barshi a ciki dan kar wani yay tunanin amfani da wani key ɗin.
A falo ya zube yana sauke numfashi da jan dogon tsaki. Jin an fara buga ƙofar tasa da ƙarfi ana masifa ya kuma jan wani tsakin ya miƙe ya nufi bedroom ɗinsa. Bai zaunaba anan, kayansa dake ta zuba ƙamshinsa dana Nu'aymah ya cire yanata faman lumshe idanu. Dan a matuƙar gajiye yake. Babu abinda yake buƙata a yanzu sama da kwanciya. Ya gaji harma baisan tataya zai faɗa ba a tausaya masa. Ga ihun su Mama debora da yake jiyowa sama-sama yana neman saka masa ciwon kai. ‘Nasan maganinku ai. Kwanan nan zaku bar gidan nan ku koma inda kuka fito’. Ya faɗa a fili yana harar ƙofar kamar sune wajen tsaye.
Daga haka ya shiga yay wankansa kamar yanda ya saba. Ya jima bai fitoba daga bayin kamar mai naƙuda🙄😏. Sai kuma gashi ya fito a yanayin gajiyar da yake ciki. Sama-sama yay shirin barci cikin tausasan kayan barci, yana fesa turare wayarsa tai ring. Kallon wayar yay, ganin Richard ne sai ya basar ya cigaba da hidimarsa. Sai da Rich ya sake kira bayan ta katse sannan ya ɗaga. A dakile yace, “Kana damuna fa”. A fusace daga can shima Richard yace, “An damekan, shine dan tsabar wulaƙanci ka wani kullema mutane ɗaki? Da ace babu wasu ɗakunan ina kake tunanin zamuje mu kwanta?”.
“Oho muku” Ya faɗa a taƙaice da yare.
“Zakace oho kuwa tunda mun gama maka wahala, mtsoww! Ka wani saka mutane zuwa cikin.....” Katse wayar Yoohan yayi batare da ya bari Richard ya ƙarasa ba. Ya taɓe bakinsa yana cilla wayar saman gado. Yanaji Rich ya sake kira bai kulaba. Sai da ya kammala shirinsa tsaf yay sallar magriba da isha'i da shafa'i da wutiri da addu'oinsa sannan ya mike ya haye gadon. Wayarsa daya cillar gefe ya ɗauka. Number baba malam ya lalubo yay dailing. Ring uku kuwa ya ɗaga.
Tamkar Yoohan yana gabansa haka ya risina cikin girmamawa yana gaishesa. Daga can kuwa baba malam na amsa masa da kulawa.
“Abba mun iso babu jumawa. Ina fatan jikin nata babu wani matsala zuwa yanzun?”.
Murmushi baba malam yayi da duban Nu'aymah da Umm ta gama canjama kaya zuwa na barci. Ya ɗauke kansa yana sauke numfashi. “Alhmdllh Yahya. ALLAH ya huta gajiya, ya kuma saka albarka. Dama yanzun nan muka gama waya da baban naka shima ya kira ya sanarmin isar taku. Mamana kuwa har yanzu barci ma take batako farkaba tun bayan allurar”.
Sassanyan murmushi Yoohan yayi babu shiri, yace, “Alhmdllh Uncle, insha ALLAH zuwa da safe zata farka normal, ALLAH ya ƙara lafiya. Bara na barka ka kwanta sai da safe”.
“To Yahya ALLAH ya huta gajiya”.


Daga haka sukai sallama. Baya yay ya kwanta ƙafafunsa a ƙasa yay filo da hannayensa. Idanunsa ya lumshe a hankali ya faɗa duniyar tunanin da shi kaɗai yasan akan abinda yake yi.


__________★★★★_________


*_To masu karatu sace shin ina Abdallah da Nasir😱🤗?._*


Tam nima dai tsayawar wannan tambayar a raina ce taja ra'ayina shiga bulayin nemansu a cikin gidansu Nu'aymah. Sai dai na karaɗe ko ina da ina tsaf babusu babu mai kama da su ɗin. Sai acan bakin su Omar dana tsinkayi yana faɗama Momynsu yanda ɗaurin auren ya kasance naji.
Ashe faɗan da Abdallah da Naser suka tafka ne a daren shekaran jiya daya bama kowa tsoro yajawo su baba malam canja shawara akan zaɓin Nu'aymah. Ananah da hajjo sukai dogon nazari da shawarar canja komai. Dan yanda abubuwan ke nan canja salo tabbas zumincinsu zai iya girgiza akan matsalar Naseer da Abdallah. Dan haka suka kira su baba malam a wannan daren tare da Abban Naseer daya iso suka tattauna. Abban Nasir shine ya bada shawarar hana Abdallah da Nasir gaba ɗaya. Ya kuma bada shawarar aurama Yoohan kamar yanda ya bukata dan a samu zaman lafiya. Hakan zai kawo masalahar Abdallah ya maida matansa. Nasir kuma yaje ya auri wata.
Kowa yayi na'am da wannan tunani na Abban Naser. Babu ɓata lokaci ko jinkiri suka kira Yoohan suka sanar masa. Yoohan kuma bai ɓata lokaci ba wajen sanarma papa. Sai dai yayi matuƙar mamakin ganin yanda Papa ya bashi goyon baya babu wani ja inja ko ƙalubalantar lamarin, ya kuma gargaɗesa karya sanarma Momynsa (Madam Chioma😸) shi zai sanar mata.
A wannan daren papa ya bada akai masa invitation na layin waya aka turama duk wanda yake da buƙatar gani a wajen ɗaurin auren ɗan nasa. Washe gari kuma ya ƙarasa dukan kai kawo da yake buƙata tare da bincikar duk yanda al'adar auren hausawa yake. Duk abinda ake buƙata sai da papa ya saya aka shiryasu a mota.


Anan kuwa kano su Abdallah basusan wace wainar ake toyawa ba. Kowannensu dai ya ɗauki alwashi akan ɗan uwansa tsakanin shi da Nasir. Hakan yasa sukaje ɗaurin auren kamar kowa cikin kwalliya ta musamman. Sai dai kuma ganin Yoohan da tawagar ƴan uwansa da abokai ya basu matuƙar mamaki. Gashi waje ya ƙure balle su tambayi iyayen nasu. Basu fita daga ruɗanin ganin Yoohan ba aka fara ɗaurin auren. An fara ɗaura na Kubrah da angonta Al-ameen yuseef durɓi, sai Hajarah da angonta Dawood Sulaiman Rano. Naseer na jiran yaji shi da Nu'aymah sai yaji Zainab Sooraj Hashim jibiya da Yahya Goshpower”.
Turƙashi zance ya girma. Ba Nasir kawaiba ne a ruɗani, Abdallah kansa hajijiya yaji tana ɗibarsa. Hakan yasa Omar dake kusa da shi ya taimaka masa suka fito daga cikin hayaniyar ya kaisa mota. Shima acan Nasir sai Ahmad ne ya kamashi ya fito da shi. Sun koma sanarma su baba malam, Abdallah ya tada motar da Omar ya sakashi ciki ya bar wajen batare da kowa ya sani ba. Nasir kam da ƙafa ya bar wajen shima a birkice.
Daga wannan tafiyar ne har yanzu babu wanda yasan ina suke. Su baba malam sunyi neman a waya harsun gaji. Dan duk wayoyinsu a kashe suke. Halin da suka ahigo suka iske Nu'aymah a gidane ya sakasu yin shiru da zancen rashin su Abdallah ga kowa. Duk da kuwa Hajjo nata tambayarsu bataga Abdallah da Nasir ba.


WASHE GARI..........✍






ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗


Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋


Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻




*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.




No. 44




*_IDAN kaji ƙi gudu sai in sa gudu bai shigo wajen ba. Ƴan uwa abokan tafiya, gafa magani A GONAR YARO. domin tabbas idan kaji gangami akwai labari_*.


*_Ina masu wahala kullum cikin neman maganin sanyi (imfection) amma babu biyan buƙata. Kinyi na asibiti har kin gaji babu canji, na gargajiyarma taɓawa kike babu wani ƙyaƙyƙyawan sakamakon. Tofa kakarku ta yanke saƙa. Domin kuwa ga dama a tafin hannunku. Munada maganin NI'IMA, maganin GYARAN HIPS (mai gida bye bye😉). Muna da maganin BOOBS (mai gida welcome🙈). Maganin BASIR mai hana sakewar zama. Duk ku garzayo domin samunsu akan farashi mai sauƙi da rahusa, ga kuma inganci domin an samosu ne daga tsaftatacciyar hanya mai nagarta._*👇🏻


*AISHA S BAYERO TRADITIONAL MEDICINE AND HERBAL RESEARCH CENTER...*


_KUNJI SUNAN KO? CENTER CE TA MAGUNGUNAN GARGAJIA, WANDA DUK WANI DAMUWA DAKE DAMUNKA IDAN HAR KAZO WAJEN S BAYERO TA KARE DA YARDAR ALLAH.. KADAN DAGA MAGUNGUNANTA SUN KUNSHI:_


_MAGANIN SANYI_
_MAGANIN NI'IMA SET_
_MAGANIN NANKARWA_
_MAGANIN KIBA BABBA DA KARAMI_
_MAGANIN HIPS_
_MAGANIN GYARAN NONO_
_MAGANIN RAGE KIBA_
_MAGANIN SAKA FEELING_
_MAGANIN CIDA KWAI_
_ZUMA YAR ASALI_
_MAGANIN BASIR KOWANNE IRI_
_HODAR NI’IMA_
_MAGANIN MALLAKA_
_GUMBAR NONON RAK’UMI_
_GUMBAR MADARA_
_TURAREN FARIN JINI_
_KAZA MARA KWAI_
_TURAREN MALLAKA 3 STEP_
_HAD’IN MATAR MINISTER 1_
_KAZA ME KWAI_


_STEP 2:_


_TURAREN MALLAKA ME KWALBA_
_ME KUNAMA DAN MATSI_
_TURAREN GOSHI_
_TURAREN QIRJI_
_TAUWADAR MATA_
_MEMORY_
_KAHON MALLAKA_
_YAJIN MAZA_
_TEA DIN MAZA_
_DAMBUN MATSI_
_MAN AYU_
_MAN DAMO PURE_
_KWALLIN IDONKA IDONA_
_GARIN SHA DAKA ME KYAU_
_KUBEWAR MATA_


_DUKA WADANNAN INGATTUN MAGUNGUNA NA GARGAJIYA HAJ AISHA NA DASU GANGARIYA.. HERBAL MAGUNGUNA NE MASU KYAU DA INGANCI.. TAFIYAYYU NA KASAR CHAD. CHADIAN HERBAL MEDICINE AND RESEARCH CENTER.. KYAU, INGANCI.. RAHUSA... SAI MAGUNGUNAN *AISHA S BAYERO TRADITIONAL MED AND HERBAL RESEARCH CENTER....*_


_NUMBER WAYAR WHATSAPP: 08121491609 KO KIRA TA NUMBER 08145873617._


_ADIRESHI: KUNTAU KARSHEN KWALTA KAN A KARASA YAN TIFA, DAIyDAI GADON KAYA CEMENT.._




Sai kunzo😘😘🤝🏻
_________________________




No. 44


..........WASHE GARI normal Nu'aymah ta tashi kamar yanda kowa yay fata. Sai dai rashin ƙarfin jiki da damuwar maganar auren da ta sake tabbatar an ɗaura mata shi. Dan bayan baba malam ya dawo daga massallaci zaunar da ita yay ya ringa mata nasiha mai ratsa jiki da ɓargo. Tun tana hawayen zuci, harta koma na zahiri. Hawaye suka dinga kwarara mata daga ido suna sauka saman fuska.
Fuskar baba malam ɗauke da murmushi ya kai hannu ya share mata hayen. Ya kamo hannayenta duka cikin nashi yana sake kwantar mata da hankali. “Kukan ya isa haka kinji mamana. Duk abinda kikaga ya shigo cikin rayuwarki saɓanin tunaninki ki ɗauka hakan shine mafi alkairi a gareki. Idan kuma har kika rasa abinda ke shine burinki da fatanki, ki saka a ranki UBANGIJI bai baki shi bane saboda ba naki bane, hanakin kuma shine yafi alkairi. Akwai abubuwa da yawa dana san suna damunki a cikin rai. Amma inason ki ɗaukesu ki watsar da su acan nesa, ki kuma manta da su ki shafe babinsu a tunaninki. Dan jiyanki ta wuce, kina cikin yau ɗinki ne. Kinga yafi kamata ki maida hankali wajen hangen gobenki. ALLAH yay miki albarka. Ya yaye miki damuwarki. Ya share hawayenki. Yay riƙo da hannunki. Yay miki jagora a gobenki da jibinki”.
“Amin Abbah na gode, ALLAH ya ƙara maka lafiya da tsahon rai”.
“Amin mamana nima na gode. Kije ki kwanta ki sake hutawa kinji. Sai dai ki zama cikin shiri dan zuwa jibi idan ALLAH ya kaimu kema za a miƙaki gidan mijinki”.
Kanta kawai ta ɗaga masa. kamar zata tambayesa waye mijin nata sai kuma tayi shiru. Ɗago idanunta dake jajur tai ta kallesa. Muryarta na rawa tace, “Abba dan ALLAH ka yafemin dukan abinda kake ganin na maka a sanina ko saɓanin haka. Sannan wlhy kaji na rantse ban aikata abinda likitocin nan suka tabbatar ba. Abinda ke a cikin hotunan nan kuma ya farune bisa ƙaddara........”
Duk abinda ya faru a waɗan nan ranakun biyu sai da Nu'aymah ta sanarma baba malam. hatta da farkon haɗuwarta da Yoohan. Sosai baba malam ya gamsu da dukan bayaninta. Dan duk abinda Yoohan ya faɗa shine ta maimaita. Inda sukai saɓani kawai shine ita tana ganin da gangan ya aikata mata. Shi kuma ya sanar dasu baba malam duk akan taimakonta zata faɗi komai ya faru. Ya san Nu'aymah tun tana yarinyarta da wahala kaji tamaka ƙarya akan abu. Koda kuwa za'a daketa idan tai laifi aka tambayeta saita faɗa.
“Na yarda da ke Mamana. Insha


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login