Showing 72001 words to 75000 words out of 260160 words

Chapter 25 - SARAN BOYE Complete Document by Billyn Abdull .txt

29 Nov 2024

19588

ta kasance a gareta. Idan da rabo zasu hadu da yah Ab ɗinta a gida mafi tsada shine Aljannah.
Da wannna tunani ta ɗauki aikan Hajjo ta fice bayan ta shiga bedroom ɗinta ta ɗakko hijjab dan akwai kayanta anan sashen hajjon.


*_ABUJA_*


“Wai nikam Khadijah mike damunkine haka kwanakin nan? Ina lura dake kullum walwalarki da farincikinki ƙara nisantar rayuwarki da mu'amularki sukeyi. Ko baki da lafiya ne?”.
Idanun Momyn Ab cike da ƙwalla take kallon mijin nata. Ta matso hawayen nata suka gangaro saman kumatunta tana girgiza masa kai.
Tausayintane ya sake kamashi, dan tsaf ya fahimci damuwar tata akan Abdallah ne da a yanzu ko kiranta a waya baya sonyi sai idan shine ya kirashi ya balbalesa da faɗa. “Khadijah!” ya sake kiran sunanta cike da taushin murya.
Kanta ta sake ɗagawa ta dubesa. Sai kuma ta duƙar tana fadin, “Na'am”.
“Mike damunki? Ki faɗamin dan ALLAH?”. Jin ya ambaci ALLAH ya sakata sake fashewa da kuka, cikin rawar harshe irin na mai kuka tace, “Abdallah ne, gaba ɗaya Abdallah yaƙi sauka daga fushin rashin Nu'aymah. Kuma nama lura yanzu fushin nasa duk a kaina ya tattarashi bansan miya saka ba?. Bayason kirana sam yanzun, sannan ƙiri-ƙiri yaki yazo ko sau ɗaya mu gansa. Idan wancan karon yana ganin baida iyali rashin zuwansa bai damemuba ai yanzu yana dasu, ita kanta tana buƙatar ganin nata iyayen ai Adawiyan. Kuma wancan karan a rana sai muyi waya sau uku hardama video call. Yanzu kam kaga inma bakai ka kirasa ka baniba sam ya manta dani?”. ta ƙare maganar da rushewa da kuka mai ban tausayi.
Jawota jikinsa yayi kasancewar darene sosai ansha aruwa. Dan sunama zaune ne sun kammala ƙiyamullaili suna jiran lokacin sahur ya ƙarasa su tashi yaran suma.
Bayanta ya rinƙa shafawa a hankali shima yana jin ɗacin hakan a maƙoshinsa. dan bama ita kaɗai Abdallah kema hakanba, kowama yana masa. Sai dai su da sauƙi saboda harkar business na shiga tsakaninsu akai-akai. Amma ko ranar sai da baba malam da kansa yay wannan ƙorafin na banza da kowa da Abdallah yayi tun tafiyarsa.
Baki ya buɗe a hankali yace...........✍


_____________________
SAHFAT PREORDER!
______________________


Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗.


SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya.


Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske.


*_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._*


_To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_.


Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU.


Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa.


*_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_*


_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________


Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗


Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋


Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
*_INA MASU NEMAN INDA ZASU SAMU INGANTATTUN:_*
*_HERBALS APHRODISIAC NA GARGAJIYA BANA HADIN BATURE BA MAI SIDE EFFECT..?_*


*_TO KU SAURARA KUJI, DOMIN NESA TAZO KUSA.._*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC!_*
*_ZEE HERBALS APHRODISIAC!!_*
*_ZEE HERBALS APHRODISIAC!!!_*


*_MUNZO MUKU DA INGATTTUN KAYAYYAKI WANDA ZASU GYARA CIKI DA WAJE_*
*_MUNADA SUPPLEMENT MASU GYARAN JIKI DANA FATA, WANDA ZASA SAKI KIYI SHEKI FATAR KI TAYI LAUSHI. TAYI LUWAI! LUWAI! TAMKAR TA JARIRAI_*
*_AKWAI SUPPLEMENT NA KAYAN MATA WANDA ZASU GYARA KI, KIJI KI TAMKAR BUDURWA, SUPPLEMENTS DINMU BASU DA SIDE EFFECT, DOMIN AN HADO SU NE DAGA INGATTATTUN ITATUWA, WATO NATURAL PRODUCTS NE ACIKI._*
*_KAI BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA, MUNA DA INGATTUN KAYAYYAKIN MATA WANDA KESA KISHIYA KWAFA, WANDA DUK INDA SARAUNIYA TAKAI KIN WUCE, WANDA ZASU TSATSO MIKI MARTABAR KI DA KIMAR KI_*.


*_AKWAI INGATTATTUN MAGUNGUNA, NA CUTUTTUKAN DA SUKA SHAFI DAN ADAM DAMA JINNU.. KAI DAMA WANDA BAMU AMBATA BA.. ZEE HERBALS APHRODISIAC (MASARAUTAR INGATTATTUN MAGUNGUNA KENAN)_*
*_KYAU, ARHA, INGANCI, RAHUSA... SAI ZEE HERBALS APHRODISIAC_*
*_MANHAJOJIN MU NA SOCIAL MEDIA: KAMAR INSTAGRAM DA WHATSAPP DAMA NAMBAR TARHON MU: DOMIN SHIIGA KUGA IRIN KAYAYYAKIN MU TUNTUBE MU TA_*


_INSTAGRAM LINK DIN MU:_
www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac


_WHATSAPP LINK DIN MU:_
https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz


_NAMBAR TARHON MU_
08169380189


*_KARKA BARI A BAKA LABARI GWARA KA BAYAR.. KIZO A DAMA DAKE YAR UWA, KI ZAMO DAYA DAGA CIKIN KASAITATTUN MATA MASU AJI.. MUNA GARIN KATSINA, SANNAN KAYAN MU MUNA BADA SU AKAN FARASHIN SAYA ‘DAI DAI KO SARI.. MUNA TURA KAYANMU A KO’INA A FADIN NAJERIYA._*


__________________________________
No. 19


..............“Khadijah tabbas kin cancanci ki damu, amma karki manta nima fa ina cikin damuwarne har kashi biyu. Ta shi da taki kema, dan farin cikinki shine nawa dana sauran yarana. Akasin haka duk a wani hali zaki sakamu. Ko yau ke baki lura da yanda Omar ya yini sukuku ba saboda yanda yake ganinki?. Kofa makaranta bai fitaba sai da nai masa magana”.
Zaune ta tashi sosai tana share hawayenta. “Kayi haƙuri to na daina, amma kodan Adawiya ka sakashi ya biyo Hajjo idan zata dawo suzo suyi salla a gidan dan ALLAH itama iyayensu su ganta, sannan musan yaya zaman nasu yake tafiya”.
Ɗan murmushi yay mata da shafa kumatunta. Yace, “Karki damu zanyi ƙoƙarin hakan insha ALLAH, nima gobe idan ALLAH ya kaimu zanje kanon, inaga Omar ne zaiyi tafsir ma gobe idan ALLAH ya kaimun insha ALLAH”.
Kanta ta jinjina masa da addu'ar fatan ganin wayewar garin lafiya.


_____________________________


Washe gari Abban su Abdallah ya nufi kano domin yin sallama da hajjo da suke shirin wucewa nan da kwanaki biyu. Yako isa da wuri, dan sanda ya shigo gidan ma duk ƴan uwansa na nan, baba malam yanama barci bai tashiba tun ɗazun daya ɗan kwanta. Yaran sun baibayesa da oyoyo kamar yanda suka saba a sashen hajjo, kowa na tambayar ɗan uwansa da suke sa'anni. Yayinda shi kuma yake tambayarsu azuminsu nawa-nawa.
Ya jima yana biyema shirmensu kafin ya nufi ɓangarensu da babu kowa a ciki, sai dai zuwan nasa Hajjo ta saka Amal da Nu'aymah zuwa su gyara duk da yace ba kwana zaiyi ba. Wanka yaɗanyi ya kwanta kafin azhar ya samu ganawa dasu baba malam, dan yama iske Abba Musbahu yana wajen tafsir danshi na safe ya keyi.


Bayan gama gaisuwa da Abban su Abdallah Nu'aymah ta nufi sashensu ranta duk a cinkushe, ko kaɗan bata sha'awar wannan zuwa Umrah duk da tana buƙatar hakan fiye da komai a ƙasan ranta. To amma fitinar da take hangoma kanta a tafiyar ta fahimci sai tafi daɗin yawa.
“Lafiyarki kuwa Nu'aymah? Kina tafiya kamar hankalinki baya jikinki?”. Umm dake zaune a falo tana duba littafin KITABUT TAUHID ta faɗa tana kallonta.
Zama Nu'aymah tai kusa da ita, tare da ɗora kanta gefen kafaɗar Umm ɗin. “Umm azuminne fa yau nikan tun yanzu na fara jinsa ALLAH, ni koma wajen tafsir bazanjeba yau barci zanje nayi”. Shiru Umm tai kawai tana kallon Nu'aymah, dan gaba ɗaya a watannin nan tana kula da ita kamar akwai abinda ke damunta. Ta zaunar da ita yafi a ƙirga tana tambayarta amma sai tace mata babu komai. Da yake ta san akwai damuwar Abdallah tattare da ita har yanzu sai take danganta yanayin Nu'aymahn da hakan. Shiyyasa ta duƙufa gayama ALLAH akan lamarin. Idan da rabon aure a tsakaninsu ALLAH ya kawo mafita ayi, idan babu kuma ALLAH ya saka musu salama su duka itama ya bata miji nagari.
Jin Umm batace komaiba itama sai bata sakeyin magana ba, tama lumshe idonu kamar mai barci.
Sun jima a haka, kafin Umm da taji Nu'aymah ta mata nauyi a kafaɗa taɗan ɗago ta kalleta, numfashi take saukewa a hankali na barci. ta girgiza kai kawai da ɗagota a hankali ta gyara mata kwanciya a kujerar tare da ɗaura kanta saman cinyarta. Aiko kamar jira take saita sake gyara kwanciya da ƙyau a cinyar Umm ɗin.
“Ita wannan lafiya take kuwa?” Baba malam da Umm bataji fitowarsa da isowarsa wajenba ya faɗa yana ɗaura hannunsa saman goshin Nu'aymahn. Ɗago ido Umm tai ta kallesa dai-dai ya janye hannun ya sake maidawa a gefen wuyan Nu'aymah.
“Lafiya lau take, barcine kawai”. Janye hannun yay yana sauke ajiyar zuciya da faɗin, “To Alhmdllh, bara na leƙa massallaci Mustapha yasanar min da zuwan baƙi”.
Kanta ta jinjina masa cike da girmamawa, tare da masa addu'ar dawowa lafiya. Da amin ya amsa yay gaba. Harya kusa ficewa a falon sai kuma ya tsaya tare da juyowa. “Banji motsin Muhammad ba, shi yana inane?”.
“Inaga yana ɓangaren Hajjo, dan tun isowar Abbansu na Abuha ya fice”. Umm ta bashi amsa. “Oh Rizwan ɗin yazo ne?”. Yay maganar yana ficewa batare daya saurari amsa daga Umm ɗinba. Itama ganin ya fice ɗin sai batace komaiba ta maida hankalinta ga kallon tafsir ɗin da takeyi yanzun a WISAL HAUSA.


________________________


Kasancewar baba malam da anyi magriba yasha ruwa yake barin gidan sai suka yanke shawarar ganawa bayan sallar zuhur shi da sauran ƴan uwansa biyu dan Abba Musbahu yana Lagos.
Bayan ya kammala da baƙin da sukazo ganinsa bai shigo gidanba dan lokacin salla yayi. Sai da suka idar da salar zuhur ɗin sannan suka shigo gidan a tare ta ƙaramar ƙofa abin sha'awa. Kansu tsaye sashen mahaifiyarsu suka nufa. Inda suka isketa ita kaɗai sai Kubrah dake fashin salla tana barci a kujera. Sallamarsu kuma ta sakata farkawa. Sai ta koma bedroom ɗin hajjo ta kwanta bayan ta gaishesu.
Duk a ƙasa suka zauna suka zagaye mahaifiyarsu, dan wannan al'adarsu ce inhar suna wajenta basa zaman kujera sai dai ƙasa. Sun gaisheta ta amsa cike da farin cikin ganunsu kamar yanda ta saba. Harda ɗan barkwancinta akan autanta. “Kunzo duk kun zagayeni babu autana”. Dukansu murmushi sukayi, Abbansu Abdallah yace, “Inna ai tunda kin gammu kin gansa”. Dariya taɗanyi irin tasu ta manya. Tace, “Gara dai shima na gansa ɗin dai yaji ɗumina”.
Dariya suke mata cike da ƙaunarta. Kafin su tsagaita su fara tattauna abinda ya tarasu game da abinda suke tsarawa na hidima bayan tafiyarta. Sun shafe kusan awa ɗaya suna ƙulla abubuwa masu muhimmanci da amfani. A cikin maganganun nasu ne Abbansu Adawiya ke kawo shawarar ya kamata su gayyato bawan ALLAH nan daketa hidima a garesu shan ruwa idan a cikin kano yake inhar yanada halin zuwan.
Baba malam da shawarar taima daɗi sosai yace, “Mustapha kaga kuma fa kazo da shawara mai ƙyau gaskiya. Dan wlhy bazan ɓoye mukuba inajin matuƙar son ƙwaɗaituwa da ganin wannan bawan ALLAH. Akwanakin nan kodan na saka lamarinsa cikin raina sai nakanta mafarki da shi duk da ban taɓa ganinsaba. Sai dai yanda mafarkin nasa ke zuwamin sai abin yakan zauna cikin raina sosai. Shiyyasa nakeson mu ƙara ƙaimi wajen masa addu'ar fatan alkairi, idanma wani al'amarine ke damunsa ALLAH ke nunamin ta hakan ALLAH ya warware masa”.
Duk da sun fahimci mafarkin akwai abu mara ƙyau a ciki sai basu takura kansu nason saniba, suka shiga addu'a a garesa da alƙawarin sakashi a duk ibadunsu insha ALLAH. Sunja kusan awa biyu da rabi a wajenta sannan suka fito dan la'asarma tayi. Basu koma ciki ba sai suka nufi massallaci kawai.


________________★


Shirye-shiryen tafiyar hajjo da Nu'aymah da Yah Ahmad Umrah ya gama kammala tsaf, insha ALLAH gobe idan ALLAH ya kaimu zasu wuce. Ta kama dai-dai da cikar azumi kwana goma sha biyar kenan.
Duk hanyoyin da Nu'aymah zatabi nason ganin tafiyar bata yuwu da itaba tabi amma bata samu mafita ba. Hakan yasa taci kukanta ta haƙura ta barma UBANGIJI ikonsa, dan ta miƙa kukanta wajen ALLAH akan wannan tafiya har batasan iyakaba. Ganin al'amarin ya kasa gagara saita ɗaurasa a mizanin hakan shine mafi alkairi a gareta shiyyasa.


Zaunar da ita Umm tayi tai mata doguwar nasiha akan wannan tafiya, tare da tunatar da ita manyan ibadu da idan taje zata maida hankali a kansu ba shashanci ba. Tsaf Nu'aymah ta riƙe komai a ranta, tareda ƙarfafa ranta akan insha ALLAH zata zama mai himma. Saboda ma ta gujema abinda take gudun ganin daga Adawiya da Yah Abdallah saita ƙudiri niyyar shiga ittiqafin idan sun isa.

Washe gari ƙarfe biyu na rana jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasa mai tsarki ita da Yah Ahmad da Hajjo. Ta tafi cike da kewar Umm da Muhammad harma da baba malam da sauran jama'ar gidan. Musamman ma su Amal da badan basu ƙarasa jarabawarsu guda biyu data rageba da tare zasu tafi.


To Nu'aymah a sauka lafiya. Duk da muna tare dake dan muji yaya wasan zai kaya ke da Adawiya da Yah Abdallah🤔🤗🚶🏻.


_______________________________
*_DOCTOR YOOHAN_*


Kwance yake acan cikin garden ɗin gidan nasu daya ƙawatu da korayen ciyayi da furanni kala-kala, tare da ƴaƴan itatuwa da ALLAH yayma bayinsa ni'ima da su. Kwanakinsa biyu kenan a Abuja ya ɗauki hutu na kwanaki goma ne saboda jikinsa daya ɗan motsa masa.
Fuskarsa a cinkushe take matuƙa, dan rashin walwalarsa ta yau ta ɗara ta kullum ma. Sosai zuciyarsa ke a matuƙar ƙuntace, shiyyasa ma ya waro kansa daga cikin gidan ya dawo nan cikin garden ɗin a gaban swimming pool dake gefe ya kwanta. Haka yake, a duk lokacin da abin nasa ya motsa yakan tsinci kansa cikin wani irin ƙunci da takuruwa. Komai na rayuwa yakan koma masa baƙiƙƙirin. Yaji ya tsani komai da kowa har aikinsa na taimakon al'umma da yake matuƙar so fiye da komai. Idan yana a wannan halin ko magana baya sonyi da kowa ciki harda iyayensa kuwa. Shiyyasa da ya motsa sai yay wuf ya ɗauki hutu domin samun damar zuwa ya keɓance kansa batare da ya shiga haƙƙin wani ba.
Duk yanda iskar garden ɗin dana ruwan pool ɗin ke kaɗawa da ƙamshin furanni masu daɗi sam bayajin wani nishaɗi tattare da shi. Hasalima yazo wajen ya zaunane badan yay farin cikiba ko yaji daɗi. Hannayensa da yay filo dasu ya sake gyarawa yana yamutsa fuska kaɗan. Sai kuma yaja tsaƙi tamkar wanda akaima wani abu.
A haka Solomon ya shigo cikin garden ɗin a ɗarare, dan yafi kowa sanin idan ogan nasu na irin wannan yanayin babu mai raɓarsa a gidan har iyayensa, suko wani lokacinma sallamarsu yake daga gidan gaba ɗaya ma.......
Duk da Yoohan yaji motsin mutum a wajen baiko motsaba, har sai da Solomon yay magana cike da rawar baki, “O...Oga good everning, dama saƙone aka kawo maka daga hannun manager ɗin com.......” kasa ƙarasawa yay saboda yanda Yoohan ɗin ya buɗe fararen idanun nan nasa da suka rine suka koma jajaye a kwanakin nan uku da ciwon nasa ya motsa.
Yanda yake jifansa da kallon ba ƙaramin tayar masa da hankali yayiba, ya ɗanja baya kaɗan dan yana shawarar juyawane kafin abinda baiyi zatoba ya afku yanzun nan.
Yoohan da duk yake kallonsa ta ƙasan ido ya maida idanunsa ya lumshe batare da ya nuna alamar yama san da zaman Solomon ɗin a wajen ba. Juyawa Solo yayi da sauri yabar garden ɗin, dan zuciyarsa ta bashi shawarar gwara ya juya yaje ya ajiye masa saƙon a ɗaki idan ya gadama ƙila ya duba daga baya.


Shigowar Solomon falon ya saka madam Chioma dake cike da tsantsar damuwar halin da Yoohan ɗin ke a ciki ta ɗago tana kallonsa. Risinawa Solomon yay ya gaidata yana nuna mata abinda ke hannunsa da faɗin, “Ma'am zan ajiyema oga wannan a ɗakinsa”.
Muryar Madam Chioma a cinkushe tace, “Yana ina?”. “Yana garden kwance Ma'am” ya bata amsa cike da girmamawa. Batace komaiba sai miƙewa da tai ta nufi ƙofa, shi kuma Solomon ya nufi sama dan ajiyewa.


A


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login