Showing 222001 words to 225000 words out of 260160 words

Chapter 75 - SARAN BOYE Complete Document by Billyn Abdull .txt

29 Nov 2024

19651

da bakwai na cika tai wata irin mahaukaciyar zabura. Sai jikinta ya kama rawa har gadon kansa na jijjiga. Gaba ɗayansu suka rufu a kanta kowa na nuna farin cikinsa. dan kuwa dai ta wuce mataki na biyu kenan. Wanda kuma yafi kowanne haɗari dama a aikin. Matakin ƙarshe shine abubuwan dake a ƙwaƙwalwar ta zasu dawo ko zatayi loosing ɗinsu. Kasancewar ta yarinya ƙarama basu cika damuwa da wannan ba dan a ganinsu tanada sauran isashen lokacin da zata koya duk abinda ta rasa. Sai dai ga Yoohan sam baya fatan haka. Burinsa komanta ya kasance tare da ita musamman karatunta na addini koda kuwa zata manta da sauran abubuwan ciki harda shi kansa.
Dukkanin taimakon daya dace shi suke bata cike da ƙwarewar aiki. A awa guda suka dai-daita komai Alhmdllh. Allurar barci aka sake mata da bama Nurse ɗin da zasu goge mata jiki dama. Amma sai Yoohan ɗinma yace su barshi. da kansa ya gogemata jikin ya canja mata kaya sannan aka maidata ɗakin da zatai jiyya.
Farin cikine sosai tattare da Yoohan. Dan yanaga komai ya dai-daita tana sauke numfashin barci da ajiyar zuciya a kai akai sai ya fito ya koma masauki dan ya sanarma su baba malam wannan daddaɗan labari.


Aiko basu kaɗaiba hatta da su hajjo ƴan Nigeria dake can cike da fargaba da alhini duk sun kaure da farin ciki da murna tamkar ance Aymah ta miƙe a kan ƙafafunta. Hajjo ta kuma sakawa akai abinci mai yawa akai sadaka da shi. suka kuma shirya ita da kaf ƴan gidan sukaje asibiti sukai ziyarar marasa lafiya da bama masu buƙatar taimakon tallafi.
Suma anan daga su baba malam har Yoohan sunta nafilfiline suna nunama UBANGIJI godiyarsu akan wannan ni'ima da yay musu. Washe gari kuma suka tashi da azumi a bakinsu na sake jaddada godiyarsu ga ALLAH. Sun kuma je sun duba ta suma hankalinsu ya sake kwanciya da samun nutsuwa fiye da farko.
Shi kansa Yoohan yau yini yay yana barci cike da kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya tare da daddaɗan mafarki.
Su papa dai baƙin ciki fal ransu. Dan a ranarma sukace zasu koma tunda ta farfaɗo. Daga Yoohan harsu baba malam basu kawo komai a ransu ba game da hakan. Sai ma godiya da sukai musu tare da rakkiya har airport. Shima Yoohan ɗin a ganinsa zaifi samun sakewa da su baba malam ɗin a yanzu fiye da su papa na tare da su.


Aiko hakance ta kasance. Dan suna dawowa daga rakkiyarsu Umm ta koma ɗaki, shiko shi da baba malam wani wajen hutawa suka zauna a cikin hotel ɗin suka shiga hira mai daɗi tamkar ɗa da uba. Dan idan ka gansu bazaka taɓa ɗaukar ba shine ya haifesaba. Yoohan yana bala'in sakin jiki da baba malam fiyema da papa da ke amsa sunan mahaifi a garesa.
A haka Rich daya tashi a barci yazo ya samesu shima. Da farko ya zaunane kawai dan yanajin zafin baba malam da kuma son fahimtar ta wace hanya suka dilmiyar masa da ɗan uwa ya fara salla. Sai dai hirar batai nisaba Rich ya farajin nutsuwa da baba malam ɗin. Harma yake jin hirar na masa daɗi da basa wani irin farin ciki.
Baba Malam kam tsaf ya fahimci Rich najin zafinsu tun isowarsu ƙasar. Sai dai baisan akan wane daliliba. Amma kasancewarsa mutum mai zurfin ilimi da hikima sai ya dinga mu'amulantar Richard ɗin cike da kulawa. Har i zuwa yanzun da suke zaune a tare.
Yoohan duk yana lura da yanda Rich ya fara sakin jiki da baba malam saɓanin farkon zamansa a wajen. Murmushi kawai yakeyi a cikin ransa, yana mai roƙon UBANGIJI ALLAH yasa abokin nasa nada rabon shiriya shima kamar yanda ALLAH ya cidashi ya tsamosa da ga DUHU zuwa HASKE.
Sunja lokaci mai tsayi suna hirar kafin su koma ɗakunansu. Shi dai Yoohan shiri yay ya tafi asibitin dan akwai abinda zaiyi. Kuma lokacin gogema Nu'aymah jikima yayi


____________★


Alhmdllh, yau kwanaki biyar kenan da yima Nu'aymah aiki. Sai dai zamuce har yanzun ba sanin inda kanta yake tai ba. Dan kullum a cikin barci take. A bisa ilimin likitanci ake bata taci ake bata ta sha ta allurai da sauransu.
A komai Yoohan ne ke tsaye a kanta. Dan duk abinda ya dace shine kema matarsa da a kallo ɗaya zaka fahimci ɗunbin tausayinta da tsantsar kulawar da yake bata akan fuskarsa. A yau ne ake shirin barinta ta dawo hayyacinta gaba ɗaya. Dan haka tun sha biyu na daren jiya babu wata allura da aka ƙara mata. Duk wata na'ura dake tare da jikinta kuma an janyeta.............✍


*_Hummm. Ashe haka kuke da tsoron mutuwa dama? Tofa inhar a ranku kunajin jaruman littafi bai kamata su mutuba sai ku daina ƙalubalantar marubuta nasaka rayuwar littafii daya wuce kima. Idan kuma har kun shirya karɓar littafi dai-dai da zahirin rayuwa dolene ku shirya amsar ƙaddarar cikinsa itama dai-dai da zahirin rayuwa. Mutuwa dolece akan kowanne bawa. Dan haka jiya na tunatar da ku muhimmancinta dan shima littafin bazai zama kullum farinciki ba. inhar mutuwar jarumar littafi zata iya ɗaga hankalinku irin haka harda masu iya buɗe baki su zageni bayan sunama karantawa ne basu biyaba😂, to lallai ku ji tsoron zuwan mala'ikan mutuwa mai ɗaukar rai a zahiri ranar da babu tsumi babu dabara, sannan kuji tsoron cin haƙƙin abinda koda ɗaukarsa kuke ba komaiba. Muguji son ziciya dan ƙarshe ɓacin zuciya take zamarwa mai ita. Kai da karantawa kake kaji zafi a ranka dan an rubuta saɓanin abinda bashi kaso ganiba harka furta ALLAH ya isa. Mu kuma da muka ɓata awanni muna rubutawa kika fitarmana, ke kuma kika gani kika karanta da yaƙinin kin samu bati, bayan mun haɗaku da Girman ALLAH mi kake tunani koda bamuce da ku komai ba?. Kunbi kun ruɗar da kanku koma fahimtar bayanin nawa bayi kukaiba😸, nace karku sare, kar kuma ku saka rai, amma shine harda masu rusar kuka😂, da masu kirana suna kuka🤣, kai jama'a gaskiya jiya kun sani dariya kun kuma sakani hawaye saboda tausayin kammu, saboda tunawa da muma mutuwar nan tana tafe a garemu duk daren daɗewa, sannan wasu a cikinmu ma an zare mana mutane masu muhimmanci a rayuwarmu a yau babusu tare damu😭😭. ALLAH ka gafarta mana baki ɗaya. Wannan itace makarantar JIKI MAGAYI bisa gaskiyar zancen Nu'aymah_*😭🙏🏻.




ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗


Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋


Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻




.*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.


No. 57


________________


*Sunana Nafisa k Abdullahi am a singer, actress.. wakokina are based on siyasa da kuma na sarakuna *


https://youtu.be/1VyZ6f1GTWg


*(YouTube link)👆🏾*


*This is my YouTube channel IN SHAA ALLH! I will be bringing to you my latest films, And musical videos*




*NafisaKabdullahi* *Sabuwar ficacciyar jaruma ce data shahara wajen fina finai da kuma wakoki na siyasa, Masarautu da sauran su*


*Ina masoya makaranta littafan zafafa? Ku fito ga dama ta samu, Munason a nuna mana k’auna ta hanyar subscribing a sabuwar channel dinnan ta Nafisa mai suna a sama. 👆🏾A kalla a kuma danna kararrawa domin sauraron shirye shiryen ta a duk sanda ta dora..*


*Danna kararrawa domin kasancewa da ita da zarar ta dora sabbin shirye shrye.*


*DAN ALLAH! Ayi subscribing, Akuma dinga viewing, Inda hali ma ayi comment da sharing zuwa ga wanda basu sani ba...*


*Akwai Facebook page dinta mai suna: https://www.facebook.com/preetyfeenat.abdullahi*


*Domin karin bayani sai a tuntub’i Nafisa kai tsaye ta number ta: *


*08071172003*


*kada ku mance ko minene daya danganci wakokin al’adun hausa, Da ire-iren fina-finan mu na hausa, Nafisa zata dinga kawo muku shi a wannan sabuwar channel din nata, Saboda haka MASOYA a temaka aje ayi mata subscribing a kuma dinga kallan abubuwan data dora.*.




__________


No. 57


...........Ƙarfe goma dai-dai na safiyar wannan rana agogon ƙasar Nu'aymah ta farka a gaban Dr Yoohan da sauran likitocin da sukai mata aiki. Sai baba malam da Umm. Dan ana buƙatar tabbatar da ingancin lafiyar ƙwaƙwalwar ta da kuma tabbatar da idan bata manta komai ba.
Gaba ɗayansu idanunsu cak akan yatsun ƙafarta dake motsawa. Har zuwa hannayenta biyu da suma ke motsin. A hankali gashin idanunta suma ke motsawa, sai numfashin ta dake sauya salon fita daga na barci zuwa na wadda take a farke.
Da farko bata ia ganin komai, ta cigaba da motsa idanun a sannu-sannu har ta fara ganinsu dishi-dishi. Idanun ta maida ta rufe tana matse fuska, babu dai wanda ya motsa a cikinsu harta sake buɗewar a hankali. Akan Dr Sophia ta fara saukesu, tayi kusan sakan goma tana kallonta kafin ta janye zuwa ga na kusa da ita. Shima dai tai masa kallo mai tsaho ta sake maidawa kan ɗayan likitan. Idanun ta lumshe ta sake buɗewa akan Dr Yoohan. Yanda take kallonsa haka shima yake kallonta cike da fargaba. Tafi tsayin mintu uku tana masa kallon ƙurullah da duk ya basu tsoro, dan tamkar tana hasashen wanene?. Ɗauke kanta tai a gareshi ta maida kan Baba malam dake a kusa da shi, sai kuma ta kalli Umm. Haka ta ringa raba kallo a tsakaninsu na tsahon mintuna.
Gaba ɗaya jikinsu duk yayi sanyi har likitancin, dan da alama ta manta komai. A bazata sukaji ta fara magana da ƙyar,
“Yah Yoohan da gaske su Abbana ne?”.
Maganar da ƙyar take fita. Amma duk sunjita duk da a hankali ne. Rikicewa sukai da farin ciki. Yoohan yay azamar zuwa gabanta ya riƙe hannunta data dafe kai da shi saboda yunƙurin tashi zaune da taso yi.
“Please relax koma ki kwanta”.
Cikin rawar murya hawaye na zirara mata a idanu tace, “Kaina namin ciwo kamar zai rabe biyu”.
“Okay, kiyi shiru ki daina magana”.
Ya sake faɗa yana maidata ya kwantar. Kunyar su baba malam da yakeji ne ya hanashi rungumeta dan farin cikin yanda komai yazo yanda sukai fata. Ya ja baya kaɗan dan bama su Umm damar ganinta da ƙyau. Idanunta a lumshe kuwa ta miƙoma su Baba malam hannu alamar suje gareta.
Kallon Yoohan baba malam yay. Ya jinjina masa kai yana murmushi da sake matsawa baya yanda wajen zai ishesu. Ya kuma jawo musu kujeru su zauna.


Tabbas Yoohan da su baba malam suna cikin ɗunbin farin ciki, hatta da Richard ma farin cikin da yaga ɗan uwansa a ciki shima sai yake tayasa. Duk da dai a yanzu shima jin wani girma da mutuncin baba malam ya keyi a ransa. Mutumin yana da wani kwarjini na musamman da iya mu'amula wa mutane.
Hatta da Solomon duk da munafunci nacin ransa sai da ya nuna farin cikinsa. Kafin ya zagaye can baya yay kiran papa ya sanar masa halin da ake ciki. Aiko dai ba ƙaramin baƙin ciki papa ya shigaba. saboda karma Yoohan yay kiransa ya sanar masa farkawar Aymah sai ya sakashi a black list. Sai dai abinda ma bai saniba Yoohan sam bai nemesa ba a lokacin. Dan sunata shigi da fici akan Aymah daketa complain ɗin ciwon kai. Ko idanunta data ɗan buɗe da farko yanzu bata iya buɗesu. Tsoron kar matsalar ta shafi idanunta ya sakasu sake mata allurar barci na awa huɗu. Sunason suga ko barcin bai gama wadatar kanta bane jijiyoyin basu gama dai-daita ba.
Da wannan damar suma su baba malam sukai amfani wajen komawa masaukinsu suka duƙufa addu'a a gareta a cikin tsaftataccen ruwan zam-zam da dama sunzo da abunsu.

A wanni huɗuu na cika Aymah ta sake farkawa. Cikin amincin UBANGIJI kuma an dace dan kuwa yanzu tana buɗe idanun, ciwon kan ma tace can ƙasa yake mata. Kowa yayi farin ciki da hakan. Yoohan ya bata ruwan zam-zam da su baba malam sukai mata addu'a aciki ta sha. shine abu na farko data fara sha. Ya kuma ɗiga mata a cikin ido kamar yanda baba malam ɗin ya sanar masa.
Babu mai shiga inda take sai shi, saboda ba'a son mata hayaniya. Duk da tanata damunsa da ƙara son ganin su baba malam yana lallaɓata.


A daren wannan ranar su Hajjo suka iso. Hajjo, Abban Adawiya, Abban Abdallah, Abba Musbahu. Sai Addah data takura akan sai tazo taga jikin Aymah ɗin. Duk da kuwa ance baza'azo da matan gidan da yara ko ɗaya ba. Su yi haƙuri har Aymah ta dawo tunda ance jikin Alhmdllh. Amma Addah ta nace, da kantama ta biyama kanta ƙuɗin jirgi. Dan ita dai a ganinta bai kamata a yanda suke da Umm ba ace batazo ta duba NU'AYMAH ba. Shaƙuwar tasu hajjo ta kalla tace a barta taje tunda tace zata biyama kanta. dan bazai yuwu a biya mataba sauran matan suga anyi son kai.


Suma sunji daɗin ganin yanda jikin Aymahn yayi ƙyau sosai. Dan da taimakon Yoohan suka samu suka shiga wajenta. Alhmdllh kuma duk ta ganesu. Harma hajjo ta tsokaneta aka cuna mata baki. Dariya duk sukayi, Yoohan ya girgiza kai yana wani ɗan munafukin murmushi, a ransa yana faɗin, ‘Ta dawo duniya yanzu zata addabi kowa. Barema ni data gama rainawa’.
Kamarko Aymah tasan mi yake rayawa. Dan tana can tana masa kallon ƙasan ido ganin yanda ya rame mata a idanu. Sai dai batai tunanin komai a ranta ba ta maida hankalinta gasu hajjo.


Bayan wucewar su hajjo Richard ya kawo abincin da zataci lokacin shan maganinta yayi da barcinta. Dan a yau ne zata fara cin abu mai nauyi bayan kullum da ake bata iya mai ruwa-ruwa kawai dan ba'a son ta tauna abu saboda jijiyiyin kanta dake tare dana haƙori.
Cikin jin daɗi Yoohan ya amsa yana faɗin, “Thanks you Rich”. Ɗan hararsa Richard yayi da faɗin, “Dama akwai godiya ne tsakanina da kai Mr X”. Murmushi kawai Yoohan yayi amma baice komaiba. Shima Richard ɗin sai ya murmusa yana binsa da kallo. Sam baya iya dogon fushi da Yoohan. Ƙauna yake masa ta gaskiya kuma ta haƙiƙa har cikin ɓargonsa. Yanajinsa a jinin jikinsa tamkar ƴan uwansa da suka fito ciki ɗaya. Kuma shi harga ALLAH bai taɓa jin zafinsa akan auran Nu'aymah da yayiba duk da kuwa ta kasance Bahaushiya kuma musulma. Sai dai salla da Yoohan ya farayi yanzu yana matuƙar damun ransa. ya rasa wane kalar tunani zaiyi akan wannan matsalar, wazai tunkara su tattauna domin haɗa hannu wajen dawo da Yoohan cikin hankalinsa?. Da yayi yunƙurin sanarma wani sai yaji rauni da fargaba ta kamashi. dan haka ya barma ransa ko sauran abokansu su Joseph ya kasa faɗamawa....


Yoohan dai tuni ya fice a office ɗin abunsa ya bar Rich da faɗawa dogon tunani. A waje yaga Solomon tsaye. Ya ɗan kafesa da kallon mamaki dan ganin yanda Solomon ɗin yay fakare kamar wanda ya tsorata da ganinsa. Bai dai ce da shi komaiba yay wucewarsa.
Nannauyan numfashi Solo ya sauke yana rumtse idanunsa da wayarsa dake cikin hannu. Yau shikam ya shiga uku, yana fatan Yoohan baiji wayarnan da yakeyi da papa ba. Gaba ɗaya sai wani tsoro na tashin hankali ya kuma baibayesa. Barin asibitin yayi jikinsa na tsuma. dama zuwansa kenan shi da Richard.
Yoohan da haka kawai yanayin Solomon yaso ɗarsa masa zargi a zuciya ya ƙarasa ɗakin da Aymah take yana wasiwasi. Kwance take akan gadon jiyyarta idanunta a lumshe. Har yanzu bawai jikin nata yayi ƙarfi baneba. Dan ko magana ma da ƙa'ida takeyinta. Kai duk ma sauran abubuwa komai zatayi da ƙa'idarsa saboda ƙwalwarta ana buƙatar ta samu isashen hutun da komai zai gama dai-daita. Dan yanzu dai su Yoohan sun tabbatar da komai Alhmdllh, sai dai zata ringa yawaita ciwon kai kafin wani tsahon lokaci da suma basusan adadiba. Sannan idanunta sun raunana zatake amfani da glass shima kafin zuwa wani lokaci. Bawai bata gani bane, tana ganin komai Alhmdllh, sai dai ba a yanda ya kamataba. Dan idan abu yayi mata nisa tana ganinsa bibbiyu ko dishi-dishi. Sannan sun tabbatar da zata rage yawan hayaniya yanzun.
Ƙamshinsa da taji ya yawaita a ɗakinne ya sakata buɗe idanunta a hankali. A kansa ta zubasu, sai dai batai masa kallon sakan uku ba ta janye. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke. ya matsa gaban gadon

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login