Showing 225001 words to 228000 words out of 260160 words
Chapter 76 - SARAN BOYE Complete Document by Billyn Abdull .txt
sosai ya zauna, kama hannunta yay cikin nashi. Cikin magana ƙasa-ƙasa da ko kana a ɗakin bajinsu zakai ba yace,
“How are you feeling?”.
Hannunta da ke a cikin nasa taɗan motsa, idanunta a lumshe, cikin magana a hankali fiyema da tasa tace, “Alhamdulillah”.
“Masha ALLAH”. ya faɗa da harshensa karyayye.
Batare da yace mata komaiba ya kamata zai tayar. Buɗe idanun tayi sosai. A rashin sanin ita yake kallo suka faɗa a cikin nashi. Saurin kauda kanta tayi tana motsa baki kaɗan. Duk da ba magana taiba yasan tsiwarce ta motso, sai dai yanzu kam babu bakin yi yanda ya kamata. Filo ya saka mata ta jingina yanda zataji daɗi. Ya zauna a kusa da ƙafafunta dake a miƙe. Gaba ɗaya jitai ta gama takurewa a wajen. Ga ƙamshinsa yayi bala'in adabawa numfashinta. Shi dai da baisan tanayi ba, ya san dai tunda ta kasance jinin masoyinsa baba malam bazai taɓa gajiyawa wajen jinyarta ba tamkar yanda yasan iyayenta zasu kula da ita. takeaway ɗin ya buɗe yana fuskantarta. Duk da ya fahimci kallonsa takeyi sai bai nuna ya ganiba. Batare da ya kalleta ba yace, “Yau zaki fara cin abinci mai nauyi. Insha ALLAH yanda jikinki keyin ƙyau zamu samu sallama da wuri. Amma sai kin daure kin ringa cin abinci ko yaya ne. Dan yanzu zakiji ɗanɗanon sa sam baya miki wani daɗi. Sai a hankali ne ɗanɗanon harshenki zai warware”.
Fuska kawai taɗan yamutsa. Dan harga ALLAH kam abincin ma ganinsa kawai da takeyi yanzu amai yake neman sakata, sai dai kuma itama tana buƙatar ganin an sallameta ta bar asibitin nan da duk take jinta a takure.
Bai damu da rashin yin maganar tata ba. Ya ɗiba abincin a spoon ya nufi bakinta da shi. Har zata kauda kanta yay saurin faɗin, “No, Please!”. Daurewa tai ta buɗe bakin idanunta a rumtse. Ya zuba mata tausayinta na ƙara ratsasa. taja kusan minti biyu tana juya abincin a baki sannan ta haɗiyeshi da ƙyar. Sake ɗiba yayi ya bata. Nanma dai sai da ta ɓata lokaci. Da ƙyar ya samu taɗanci, sai dai sunja lokaci mai tsaho ana ƙaƙa nakayi, dan harda hawayenta shaɓe-shaɓe a fuska. Da ga ƙarshe dai ganin ta ɗanci ya haƙura ya barta. Tissue yasa ya goge mata bakinta da hawayen datayi. Yana ƙoƙarin tashi ta riƙo hannunsa. Kallonta yay kawai sai dai baice komaiba.
A mamakinsa sai yaga ta ɗauki cokalin daya bata abincin ta ɗibo ta nufo bakinsa. ba ƙaramin harbawa zuciyar Yoohan yayiba. Duk da ba abincine daya cika damuwa da shi ba haka ya buɗe bakin kawai yana kallonta. Zuba masa tayi kuwa batare da ta yarda sun haɗa ido ba. Ta ƙara ɗebowa tana magana a hankali. “Ka rame da yawa. da alama kaima baka da lafiyar kuma bakacin abinci. Amma gashi ni kazo ka tsareni sai da naci. To kaima tsareka zanyi sai kaci”.
Yanda tai maganarne a sakalce ya sakashi yin murmushi. ya fahinci kuma da iya gaskiyarta take faɗin abinda ke a ranta. Hannu ya kai saman fuskarta a hankali yana faɗin, “Thanks you”. Kallo ɗaya tai masa ta janye idanunta batare datace komaiba. Sai dai taji daɗin thanks you ɗin daya ce mata. Hannu tasa akan hannunsa dake saman fuskarsa ta janye, dan yanda yake mata a kumatu jitake tsigar jikinta na tashi. Murmushi ya kumayi yana cigaba da amsar abincin. itako taƙi yarda su haɗa idanu sam, sai danna masa abinci takeyi.
A wannan yanayin Dr LiLiya shigo ya samesu. Da tsokana yake cewa, “Irin wannan soyayya haka bazasu bari a warke ba?”.
Sosai Aymah ta waro idanu akan baturen likitan. Sai dai kuma batai magana ba. Ta ɗan harari Yoohan dake murmushi. Sai kuma ta ajiye spoon ɗin ta kwanta abunta da juya musu baya. Ƙaramar dariya Yoohan yayi har haƙoransa na bayyana sosai. Ƙasa-ƙasa ya cema Dr Liam “Kaga ka jamin an bar bani”.
Dr Liam dariyar shima yayi yana haɗe hannaye waje guda alamar Sorry.
Ita dai Aymah bata sake kulasuba. Da za'a bata magani ma ƙin yarda tayi ta kalli kowa a cikinsu. Tana sha kuwa ko mintuna goma cikakku batayi ba barci mai nauyi yay awon gaba da ita. Sassanyar ajiyar zuciya Yoohan ya sauke. Ya kama hannunta data bashi abinci ya sumbata yana wani lumshe idanu. Daga haka suka fito suka bar mata ɗakin shi da Dr Liam
____________★★
Yau kwanakin su Hajjo biyu da zuwa. gobe idan ALLAH ya kaimu kuma zasu koma harda su baba malam ma. Sunzo sun duba Aymah da jikinta keta ƙara warwarewa Alhmdllh. Sai dai batason cin abinci sai Yoohan yata lallashi da dabara. A hakanma bata yarda taci ita kaɗai. sai dai idan ya ɗeba spoon ɗaya ya bata itama sai ta ɗiba ta bashi. Ita a ganinta wayo takeyi dansu cinye tare ya rage mata aiki. shiko hakan ba ƙaramin shauƙi yake sakashi a ciki ba, da jinsa on top. Ta kai ko ruwan addu'arta ya bata tasha itama shima sai ta rage ta bashi ya sha. Dan harga ALLAH ramar da taga yayi kuma na damunta a cikin rai. Ta tabbatar koda rashin lafiya yayi to harda damuwar halin da take a ciki. Dan ta fahimci shi mutum ne mai tausayi sosai dama.
Dr Yoohan da Dr Liam Sai Richard sun fito daga Ward ɗin dake gefen wanda Aymah take sai wayarsa tai ring. dakatawa yay domin ya amsa su kuma suka wuce. Papa ne, sun gaisa da maganar data shafesu ya maida wayar cikin aljihun farar rigarsa ta likitanci daya ɗora ya cigaba da tafiyarsa dansu Rich sun wuce.
Kamar da wasa sai yaji ana hausa ta lungun daya gitta. Duk da bajin hausar yake ba mu'amula da hausawa da yakeyi a yanzu tana ƙara sakashi fahimtar yaran hausa kaɗan-kaɗan. musamman zama da Nu'aymah duk da bawani jimawa sukai tareba. kawai dai shi mutum ne mai kaifin basira ɗaukar yare dama.
Samun kansa yay da ɗan komawa da baya. Na daga ƙafa zan bisa nima na ɗakko muku rahoto xoxo da rano sukazo suka tsaidani da surutu🙄, wai su nan sunga wadda suka sani a ƙasar Austria, sunja mana rashin samun wannan rahoton. Dan ina gaisuwa da su ne hankalina nakan lungun da Yoohan ya shiga. Kafin mu gama sai gashi ya fito fuskarsa a tsuke. Kuma tamkar wanda yaga wani abun dayay matuƙar rikitashi ko ɗaure masa kai. Da kallo na bisa. batare dana tsaya munyi sallama da su Rano ba nai azamar binsa a baya. Suna ɗagamin hannuma ko saurarensu ban ƙaraba. Nai gaba ina faɗin, “Maƙalallu sun maƙalle a asibitin nan sun hanani ɗaukar rahoto”. Ina ɓullowa na hango Huguma da Mamu sun ɓullo suma. da alama tare suke dasu xoxo dinma dai. Washe baki suka fara irin su sunga wadda suka sani dinnan dai. saurin ɗauke kai nayi ina cuskule fuska na canja hanya kamarma ban gansu ba. Ina jiyo su Rano na basu labarin wai yanzu suma na gama musu yarfi dan ina tare da Dr Yoohan, Wai ai zamu koma Nigeria zan gane kurena, suma zasu rama ne😣😒.
A office na iske Yoohan nata kaiwa da komawa. da alama dai tabbas abinda ya tada masa hankali ya jiyo ya kuma gano. Dan yanayin nasa yayi kama da wanda ke acikin ruɗani da al'ajab, harma da kullewar kai.
To nidai bansan tayaya zanbi na san mi wannan bawa ya gano ba. Sai dai mu cigaba da bibiyarsa kuma kozamu fahimta anan gaba.
Washe gari da safe su baba malam suka wuce Nigeria harda Richard. Akabar Aymah da Yoohan da Solomon kawai. (Jelar Yoohan😜). Kuka sosai Aymah tasha dan bataso wannan tafiya tasu baba malam ba. gudun samun matsala su Yoohan suka danna mata allurar barci data jata tsahon lokaci.
Su kansu su Umm ɗin badan sunsoba suka taho, sai dai tunda jikin nata Alhmdllh gara su dawo kan harkokinsu suma tunda mijinta tsaye yake akan dukan lamuranta, ko a fuska basu taɓa ganin gajiyawa daga garesa ba. Hakan yasa ƙaunarsa ta ƙara shige musu zuciya da bargo sosai. Suna sake taya Nu'aymah murnar dacewa da tai da miji na gari mai kyawawan halaye. Hakan na nufin a haifeka cikin musilinci ka rayu da girma a cikinsa bashi bane ke nuna zakafi kowa kyawawan halaye. Balle har kayi tunanin samun lasisin hantarar wanda ya tuba daga baya da masa takama kai kaine mai addini. Shi wannan da kake kalubalanta da jifansa da kalmar tubabbe dan kawai ya shigo addinin islama daga baya sai kaga ya fika rabauta a wajen UBANGIJI. Ya fika ƙyawawan halaye nagartattu abin koyi. Mu kiyayi aibanta waɗanda suka shigo musilinci saboda mu an haifemu a cikinsa, dan wlhy mu hausawa munada wannan banzan halayen a rayuwar zahiri. ALLAH ka shiryemu dai.
Sun iso Najeriya zukatansu cike dajin daɗin yanda suka baro jikin Aymah. Sun kawoma sauran ƴan uwa labari mai daɗi da saka kwanciyar hankali. Fatan kowa kuma ALLAH ya ƙara mata lafiya ya kuma maidosu gida lafiya.
_________★★★★__________
Nu'aymah ta cigaba da jiyya da samun kulawa ga mijinta. Duk da kuwa bayan tafiyar su Umm taso rikita kanta da damuwa. Amma Yoohan yayta lallashi da lallaɓa harta haƙura ta cigaba da sakin jikinta da shi yanda ya kamata. Dan duk abinda ya fahimci tanaso shi yake mata. Wannan ya saka ƙara samun nasara sosai game da lafiyarta, wata shaƙuwa ta musamman kuma na sake shiga tsakaninsu. uwar ramar da tayi ta ɗan fara cikowa. Yakan kama hannunta yaɗan fita da ita su zagaya cikin asibitin dan tasha iska. Hakan kuma na sakata farin ciki da sake godema UBANGIJIN daya bata lafiya. Dan idan taga halin da wasu suke ciki zuciyarta na ƙara raunana. Taga ciwonta ba komai baneba ashe.
Haka rayuwar ta cigaba da gungurawa har ga su Yoohan da cika sati uku a ƙasar Austria, cikin birin Vienna. Alhmdllh yanzu kam jikin Aymah ko makiyi ya gani yasan an dace. Sai dai tana amfani da glasess ɗinta da yay mata wani masifar ƙyau kai kace na kwalliyane ma. Sai ko yar ramar da har yanzu bata gama cikowaba yanda ya kamata. An basu sallama a daren yau, tare da ɗorata a kan magunguna da zata sha na tsahon watanni biyu har komai ya karasa dai-daita. Sai allurai guda hudu da za'ai mata a kowanne wata sau biyu suma.
Sosai Yoohan yake a tsananin farin cikin cikama baba malam burinsa na ganin lafiyar Nu'aymah. Hakama Solomon ya nuna jin daɗinsa. Uwar gayya Nu'aymah kam ai ba'a magana. Dan tsabar jin daɗi har rungume Yoohan tayi batare data farga da abinda tayi ba. Gaba daya saita sake sagar masa da gaɓɓan jiki. dan a yanda take masa abubuwa a asibitin nan gaba ɗaya rikita masa lissafin tunani takeyi.
Haka dai suka tattaro zuwa hotel ɗin da Yoohan sukai masauki. Bayan sun gumtsama ƴan 9ja labarin sallama. Masoyan su na gaske sun sake tayasu murna. Yayinda maƙiya kam sam ba hakan bane. Wasunsu ma sai shiri da suke musu na wasu bala'oin domin tarbarsu da shi. Dan a cewarsu babu abinda za'a fasa. Yanzu ne ma wasan zaiyi zafi.
Nidai nace, “Hummm”.
______________________________
Tunda suka iso ƙayataccen Hotel ɗin daya gama haɗuwa da ƙawatuwa, Nu'aymah take jinjina girman UBANGIJI da rahamarsa. Hotel ne daya ginu, ginuwa mai ban mamaki da al'ajabi. dan wannan ba fasahar masu gini bace, wani ikone da rahamar UBANGIJI da hikinarsa. Ginine mai tsananin tsayi da ado, harma batasan yaya zata musalta gamai karatu ba. Mutane nata kaiwa da komawa duk da kuwa dare ne, maza da mata harma da iyaye da yaransu. Daka gani dai kasan wajene na hutawa, dan harda baƙakenmu tsilli-tsilli a wajen ana more rayuwa.
Cike da neman tsokana Yoohan yace, “Kar dai kisa ace mana ƙauyawa hajjaju”. Hararsa ta ɗanyi, sai dai batace komai ba dan yanzu ba Aymahn da baceba. Sam bata cika son magana ba da hayaniya. Shiyyasa wani lokacin idan yaji shirun nata yayi yawa sai ya takaleta koda hararsan tayi. dan yanason yaga ta dawo kamar da ɗinta mai tsiwa abin na masa daɗi. Amma yasan sai a hankali. Koda kuwa zata koma kamar da ɗin ba hundred percent ba.
Batare da tasan daga ina Solomon ya ɓullo ba ta gansa a gabansu. Cike da girmamawa ya risinar da kansa yana gaishesu da mata sannu da zuwa da taya murnar samun lafiya.
Ta amsa masa kadaran kadahan. Dan mamakin irin wannan lamari takeyi, kenan a ko ina Yoohan yake suna tare da wannan mai gadin ko mi?. Bata da mai bata amsa dan haka ta hadiye abunta ta maida hankalinta ga sauraren bayanin da Solomon ke ma Yoohan akan ɗakin da zasuje, ya mika masa wani ɗan card. Nu'aymah ta fahimci da ba'anan suka saukaba kenan. A yau ne Yoohan ɗin ya saka suka dawo nan ko kuma yaya ai oho dai. Sai dai batasan minene dalilin yin hakanba, bakuma ta tambaya ba.
Hannunta ya kama suka shiga har cikin hotel ɗin har masaukinsu. sai dai har suka iso ƙofar ɗakin tanata faman kalle-kalle. dan da gaske ta zama baƙauya. Duk da kuɗin gidansu iyayensu basa taɓa barinsu zuwa irin waɗanan wajajen koma tace ƙasashen. Iyakar yawonsu baya wuce Saudia shima Umrah ko aikin hajji ke kaisu. Sai ko mazansu da kan je harkokin kasuwanci dana karatu wasu ƙasashen. amma dai su mata ba'a barinsu sam.
Kati ya fiddo a aljihun green jeans ɗinsa ya saka a wani abu kamar na atm yay danne-danne ƙofar ta zuge kanta gida biyu. Zare katin yayi ya kalleta da mata nunin ta fara shiga. Bismilla tayi haɗe da sallama ta saka kafarta cikin ɗakin.............✍
_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[6/22, 1:18 PM] +234 803 139 8734: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 58
............Wani irin ɗumi ne mai daɗi da saka nutsuwa ya ratsa mata jiki. Ga ƙamshi mai kwantar da zuciya na tashi. Ɗaki ne ƙaton gaske da yaji ababen more rayuwa da birgewa. Ga wasu irin ƙwayayen wuta dake bada kalar blue, green, an purpule ƙanana. Idan wannan ta kawo sai ta dauke wannan ta kawo. Hakanne ya ƙara ƙawata ɗakin da adon da akai masa na musamman daya tilasta Aymah nutsuwa tana kallon komai daki-daki.
Jinsa a bayanta ya sakata juyowa ta ɗan kallesa, ganin ita yake kallo tai saurin janye idonta. Kafarta ta ɗaga ta cigaba da takawa tsakkiyar ɗakin inda aka ɗaura wasu balan-balan da sukaja hankalinta masu zubin love, dan kamar sunanta take hange a jikinsu.
A hankali takai hannu kansu dan kuwa tabbas sunanta ne a jiki. Tana taɓawa suka shiga fashewa da kansu har taɗan zabura dan tsoro. A bazata sai jin abu na zubo mata a jiki tayi mai ɗan karan ƙamshi. Tanason ta kalla amma yanda yake zubowar ya hanata damar hakan. Dole ta tsaya a waje guda kawai ta lumshe idanunta abin na cigaba da sauka a kanta tamkar ana fesoshi.
Tsahon mintuna biyu cif sannan ya daina zuba. Buɗe idanun tayi a hankali tana kallon ƙyawawan kalolin flowers ɗin dake zube a ƙasa alamar sune suka zubar mata a jiki. Samun kanta tai da tsugunnawa tasa hannu ta dumtsosu tare da kaiwa kan hancinta dan ƙamshinsu ya mata masifar daɗi..
Shaƙa tayi ta lumshe idanu wata irin nutsuwa na saukar mata. Ta buɗe a hankali tana ɗagowa ta kalli inda Yoohan ke taye jikin bango ƙafafunsa a harɗe. Hannayensa duka biyu cikin aljihun wandonsa yana mata wani irin kasallen kallo da lumshe idanu. Ga wani irin ƙyaƙyƙyawan murmushi akan fuskarsa.
Samun kanta tai da sakar masa wani lallausan murmushi itama batare data san kona minene ba. Ta miƙe a hankali tana takowa garesa har lokacin idonta dake cikin siririn farin gilashin na kansa. A fuska ta watsa