Showing 60001 words to 63000 words out of 260160 words
Chapter 21 - SARAN BOYE Complete Document by Billyn Abdull .txt
lafiya. Babban abin takaicinma yafi yawa a ɓangaren mata masu haihuwa. Kaga ma'aikatan asibiti nacin zarafinsu dan kawai sun kasance ƙauyawa ko talakawa. Haba ƴan uwana, wannan aikinfa da kike cin zarafin wasu dashi tamkar mabuɗine na gida guda biyu. Wuta ko aljannah, ya rage naki/nak ka zaɓama kanka wanda kafi buƙata. ALLAH ya shiryar damu dai, ya rabbi kai riƙo da hannun ma'aikatanmu masu ƙyawawan zukata domin rahamarka da alfarmarka🙏🏻😭).
__________________________
Tunda Addah ta isko Umm a ɗaki basu iya cema juna uffan ba. Kowa ya zabga uban tagumi ne yana saƙa mai fishshesa. Sun kwashi tsahon mintuna sha biyar a haka kafin Addah ta katse shirun nasu da faɗin, “Ni nama rasa abin faɗa wlhy akan wannan al'amari, har nawa Nu'aymah take da ƴan sanda zasuzo su tafi da ita? Mi ma to tayi musu? Sannan miyasa yaya malam zai yanke wannan hukuncin mai tauri haka?”.
“Wannan sune tambayoyin da nake taima zuciyata Addah, amma sam na gaza samo amsar ko guda a ciki. Ina ƙyautata zaton a tafiyarsu bikin nan koma miye ya faru acan ya faru, dan........”
“Haba Umm miyasa zakice haka? Naga dai su a cikin Orphanage suke? To mima zata aikata da har ace mu bamujisa ba?”.
“Addah yaran nan kafa haifesu ne amma baka haifa halinsu ba, minenema bazasu aikataba tunda basa ganin idon kowa. Ballema Nu'aymah da batajin magana sam, wuyarta dai ta samu sakewa ne kawai, shiyyasa sam banason ko gidanmu tace zataje ta kwana ko wani waje wlhy, danni bansan ina ta ɗakko wannan halin nata na tsiwa da rashin kunyaba”. Yanda Umm tai maganar cikin ɓacin rai yasa Addah saurin faɗin. “Dan ALLAH karki tsaurara harshenki akan wannan abun, mudaibi komai a sannu muji inda matsalar take. Nu'aymah har yanzu yarinyace, kuma sanin kankine duk rashin ji da tsiwar Nu'aymah batayinsa ita kaɗai sai da gudunmawar su Adawiya dama, tunda halin nasu ai duk ɗaya ne.....”
“Humm Addah kema kinsan indai gaskiya zaki faɗa Nu'aymah ta fisu kaifi, dan duk abinda zasu aikata itace jagora”. “To kowa ya zauna akan ra'ayinsa danni bawai yarda zanyi ba, inaga dai bara nakira su Yusrah muji minene ya faru?”. Umm dai batace komaiba, tanata kuma ƙoƙarin danne damuwar dake cizon ranta da kukan dake yunƙuro mata a rai. Duk da Alhmdllh zuwan Addah a gareta ya sanyaya mata fushinta bakamar sanda ta shigoba.
Sallamar Yusrah da Amal ce ta saka Umm da Addah ɗagowa suna kallonsu. Basai an faɗaba, daga gani kukama sukeyi. Hakan da Umm ta gani sai ya sake karya mata zuciya, tai ƙasa da idanunta tana karanto7 addu'ar neman sauƙi da sassauci wajen UBANGIJI.
Zama su Yusrah sukai kansu a ƙasa suna sharar ƙwalla. Addah tace, “Kuka ba shi bane mafita Amal da Yusrah, ku sanar mana mikuka sani game da hakan dan musan hanyar data dace mu kama wajen amso ƴar uwarku”.
Share hawayensu duk sukai, cikin nutsuwa sukaima su Umm bayanin abinda ya faru aranar ƙunshi, sai dai sun ɓoye cewa Nu'aymah ta fasama guards ɗin kai, sundai ce ta wulwula dutse bisa tsutsayi ya daki glass ɗin motar. Hakan da tayine kuma ya saka mutanen tsayawa amma da guduwa zasuyi.
Shiru babu wanda ya iya cewa komai tsakanin Umm da Addah, sai da kusan mintuna uku Addah ta sallamesu suka tafi.
“Umm! Inaga lokaci yayi da zamu fara aiwatar da shirinmu a gidan nan gameda waɗanan abubuwan. Na kula al'amarin ƙara zurfi yakeyi kullum”.
Murmushi Umm tayi idanunta akan Addah, ta ce, “Addah wannan ai babu saka hannun kowa a ciki, itace ta jama kanta. Ni wlhy a yanzuma naji bana sha'awar sanin wanda ke aikatawar.........”
“Me yasa?”
Addah ta faɗa da mamaki.
Murmushi Umm ta sake yi har haƙoranta na bayyana, tace, “Addah to minene amfanin sanin? Babu abinda sanin zai amfanar sai fitina. Idan a gidan nan yake zai zama sanadin lalacewar zumincin da aka gina bisa haƙuri da juriya. Idan kuma a waje yake za'a jawo masa tsana daga mutane a tozarta iyalansa. Addah hakan baida wani amfani a gareni, dan wlhy bana fatan kwana da wani musulmi a cikin raina koda na kwana ɗaya ne, dan bani da tabbacin wayar gari. Koma wanene UBANGIJI ya rufa masa asiri na tsahon lokaci, ya kuma fimu sanin hikimar yin hakan. To mu haƙura kawai mu barsa da UBANGIJIN ya ishesa komai”.
Ba ƙaramin ƙurama Umm ido Addah tayiba, har sai da takai Umm ɗin ta taɓata da faɗin, “Ina kika tafi kuma?”. Murmushi Addah tayi da sauke ajiyar zuciya. Tace na tafi duniyar mamaki ne da tsarkake sunan ALLAH, Umm ki godema ALLAH ya azurtaki da ƙyaƙyƙyawar zuciya wlhy........”
“Kema ai ya azurtaki da ita Addah, dan ina koyi da wasu ƙyawawan halayene daga gareki. Hakan yasa ƙaunar da nake miki ta dabance a zuciyata wlhy, fatar bakima bazata iya kwatantawa ba, kun bani gudunmawa ke da Baba wadda har na koma ga ALLAH bazan gazaba wajen roƙa muku rahama da yardarsa”.
Hawayene ya cikama Addah ido kamar yanda ya cikama Umm itama, suka kama hannun juna suna murmushi cike da ƙaunar juna da ta ginu tun ƙuruciya..............✍
(ALLAH ya bar ƙauna Umm da Addah😅😘🤗)
_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
._____________________
SAHFAT PREORDER!
______________________
Wani kaya sai amale ka ɗauka🤗.
SAHFAT PREORDER maida tsohuwa yarinya.
Kaji masu kawo kayan adon gida dana jiki ƴan gaske.
*_Ina mata masu ƴan bana bakwai? ko uwargidar da ake shirin kawoma ƴar bana bakwai?. Kai hardama matan gayu ƴan ƙwalisa masu son sabunta gida da kayan ado ƴan waje masu sauƙin farashi da nagarta!._*
_To ku garzayo dama ta samu, dan SAHFAT PREORDER sune na ɗaya a wannan fanin. Idan kayan kitchen kikeso masu ƙyau da nagarta a farashi mai sauƙi kuma zaki samu a Sahfat preorder. Idan kayan sakawa kikeso na manyan mata ƴan gayu suma akwaisu babu ƙayarya. Jaka ko takalma na nunawa tsara suma ba'a barsu a baya ba harma da mayafai. Hakama kayan ɗaki basu da tsara_.
Ni shaidace domin dukkan kayana ta hannunsu nake samu nima. Ku garzayo kuma a dama daku dan nasan zakuyi alfahari da hakan insha ALLAHU.
Kiyi magana ta wannan Number 08142957548 insha ALLAH zaki samu ƙarin bayani ƴar uwa.
*_Siyen nagari😇, maida kuɗi gida😉 sai SAHFAT PREORDER🤗🤗😘😍😋_*
_____________________________
*_SAUDIA_*
.............Kai kawo taketa faman yi a falon nasu dake wadace da sanyin ac da ƙamshi kai kace safa da marwa take gudanarwa. Ta canja sosai, dan komai na jikinta ya ƙara girma da cika. Daman can duk tafi su Nu'aymah girman jiki kasancewar ta ɗakko jikin Addah. Yanzu kuma darajar aure saita sake bata damar buɗewa tamkar ba ƴar shekara goma sha takwas ba.
Tabbas tana samun ci da sha da sutura duk irin wadda ta buƙata, sai dai a watanni tara kenan da aurenta da Yah Abdallah babu wata rana da zata ware ta dangantata da farin cikinta. Idan har ta samu kulawarsa to na wasu awoyine da zai biya buƙatarsa. Baya son zaman gidan sam, ita kanta har mamaki take da al'ajabin ina yake zuwa bayan makaranta da harkar kasuwancinsa?.
Duk yanda taso fahimta ko gano hakan ya gagara, babu kalar dabaru da maman Aaida bata koya mataba duk kuma ta bisu daki-daki amma ta gaza samun haske. A yanzu haka wata ƙura ta fahimta baibaye da ita game da mijin nata shine dalilin kaiwa da kawowar tata.
Tun daga randa Abdallah ya fara kusantarta ba'a cikin hayyacinsa ba a washe gari ya haɗata da wasu ƙwayoyin magani guda biyu. Daga haka kuma duk sanda zai kusanceta sai ya batasu ta sha. Tun bata taɓa kawo komai a ranta game dasu ba harta fara zargar wani abu. Ba komai ya kawo mata zarginba kuma sai haihuwa da akullum maman Aaida ke kawaɗaita mata ta sanadinta zata iya samun soyayyar Abdallah, tunda sunyi dukkan wasu dabaru yaƙi hawa network. Da farko Adawiya batason ta haihu yanzu, amma da taji wannan magana daga maman Aaida sai taji ƙwaɗayin hakan itama dan tana masifar son Yah Ab. To amma sai me? Har yanzu babu ciki babu alamarsa a gareta, har zuwa asibiti tayi a ɓoye aka dubata Doctor ya tabbatar mata inhar bata daina sha maganin hana ɗaukar cikiba bazata taɓa samun ciki ba.
Wannan magana ta daki zuciyarta, dan a ɗan hasashenta ta fahimci kenan maganin da Yah Ab ke bata kullum na hana ɗaukar cikine? Duk da zuciyarta taƙi aminta da hakan sai taji tana ƙwaɗayin dubawa ta tabbatar. Wannan shine dalilin kai kawonta tana nazarin hanyar data dace tabi wajen binciken maganin a ɗakinsa batare daya saniba ko ya ganta. Saboda haka taƙi zuwa makaranta yau ta zauna gadin fitarsa. Sai dai kuma har yanzu bataji ko motsin alamar zai fitoba balle tayi tunanin fitar tasama kamar yasan mi take shirin yi....
(Humm muje zuwa baby Adawiya😉😂).
______________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
_______________________
________________________
Dr Yoohan ya bama matar da yazo kano dominta dukkan gudumawar data dace har ALLAH ya bashi nasarar dai-daita komai da taimakon Dr Aysha. Sai dai fa Dr Sa'ad yasha masifa dan tabbas harda sakacinsa. Ba komai ya sashi sakacinba kuma sai kasancewar matar talakace, hasalima Dr Yoohan shine ya biya mata kuɗin aikin dukda kuma shine yayi aikin. Ya kuma bama marayun ƴaƴanta wasu ƴan kuɗaɗe tare da buƙatar takardun makarantar babban yayansu dake riƙe da gidan da ƴar sana'arsa ta saida ruwa a cikin kasuwa. ALLAH ya taimakesa tun mahaifinsu nada rai ya haɗa diploma ɗinsa da ƙyar da siɗin goshi. Wannan alkairi nasa a garesu ya sakasu cigaba da jera masa addu'oin fatan alkairi da nasara a rayuwarsa. Tare da fatan ALLAH yasa yanada rabo cikin addinin islama.
Tunda Dr Sa'ad yaga Dr Yoohan ya wuce sai ya fara sakaci da kula da matar yanda ya kamata saboda takaicin ƴarta data bijire masa tun farko. Da farko shine zaima matar aiki akan matsalarta, ya buƙaci kuɗaɗe masu nauyi daga wajensu na aikin amma suka tabbatar masa basu dasu. Sunta roƙonsa ya taimakesu ko rabi su bada kafin ta warke sai su cika ya nuna bazai iyaba, sai kuma ya koma ta bayan fage ya nema yarinyar matar akan inhar zata bashi kanta shiko zaima mahaifiyarsu aiki ƙyau bama sai sun biyaba. Itako tace bazata aminceba, dan ran mahaifiyarsu a hannun ALLAH ya ke, sun kuma dogara da shi.
Wannan shine farkon matsalar. Lokacin da Dr Sa'ad ke bibiyar yarinyarnan saiko karaf a kunnen Dr Aysha, hakanne yasa ta koma a ɓoye ta kira Dr Yoohan da roƙon ya taimaki yaran inhar yanada halin yin hakan. Da yake tasan yana Abuja yana hutun kwanaki uku. Sanin ƙyaƙyƙyawan halin Dr Aysha ya saka Dr Yoohan yarda ya baro Abuja ta mota ya nufo kano. Da taimakonta sukaima matar dukkan hidima, ya tafi yabar amanar kulawarta a hannunta ita da Dr Sa'ad. dan Dr Aysha ta ɓoyema Yoohan sunansa dan kare masa mutuncinsa.
Da Dr Sa'ad ya fahimci Dr Aysha ta ɓoyema Dr Yoohan sunansa da ainahin gaskiya sai yay shirin ɓata aikin da akaima matar saboda jin zafin rashin haɗin kai da bai samuba na yarinyarta. Dr Aysha dake taimaka musu kuma data fahimci hakan ta tabbatar masa saita sanarma Dr Yoohan ɗin komai. Wannan shine yay masifar tada hankalinsa kafin ta sanarɗin shi ya kira ya sanar.
Yunwa da gajiya taima Dr Yoohan rumusu zuwa yanzun, haka ya fito a matuƙar wahale Dr Aysha biye dashi tana masa bayani akan nasarorin da suka samu game da sauran aikin da yayi a wancan zuwan kafin yima wannan matar aiki. Sosai yaji farin ciki a ransa, dan haka ya biye mata suka shiga zagaya ɓangarorin da marasa lafiyar suke yana dubasu.
Duk inda ya gitta addu'a ake binsa da shi, duk da wasu da an masa addu'ar zakaji sunce. Arne ne fa. Jin hakan kansa wasu jikinsu yay sanyi. Wasu kuma suce dan arne ne baza'a masa addu'a ba bisa ga ƙyautatawarsa?.
To shidai baimasan sunayiba, dan farincikine shimfiɗe a ransa ganin nasara na kuma ziyartar aikinsa a koda yaushe. Amma duk da wannan farin ciki sam babu fara'a kota sisin kwabo a fuskarnan tasa saboda halittarsace haka rashin fara'ar.
Suna kammala zagayawa ya kalli agogon dake a tsintsiyar hannunsa. Ganin yaci a wanni uku a cikin uku da rabi na hutunsa ya sauke ɓoyayyen ajiyar zuciya. Bashi da tabbacin samun jirgi mai komawa Lagos yanzu, dan haka ya yanke shawarar nufar Abuja a mota kawai, sauran patients ɗinsa kuma sai dai Richard ya dubasu.
Da wannan tunanin yayma su Doctor Aysha sallama ya fito batare da ko office ɗinsa yay tunanin shiga ba. Amma duk da haka sai da Doctors ɗin dake matuƙar yinsa suka firfito suka gaishesa, sannan suka yo masa rakkiya zuwa wajen guards ɗinsa da basuyi tunanin fitowar tasa ba a yanzun. Dan Solomon suke ta bama labarin abubuwan da suka faru game da kama Nu'aymah da aka turosu yi.
Cike da farin ciki Solomon ke wata shegiyar dariya, ya ƙyalƙyale da ita yana faɗin, “Inason kafin kuje abuja da ita kuci ubanta a hanya ta ƙarasa da ƙafa ɗaya. Kai bama nason taje da numfashi gaba ɗaya. ku kaita da rabin rai yanda oga zai ƙarasata da kun isa, dan bana fatan kafin mu dawo Abuja boss yaji koda ɓurɓushin labarin abinda ya farune. Kunsansa ɗan hana ruwa gudu ne. Shi a dole masoyin ƙ..........”
Da sauri Solomon ya haɗiye sauran maganarsa jin ƙamshin turaren Dr Yoohan ya cika wajen. Yay azamar juyawa kamar yanda suma sauran duk suka juya a tsorace.
Ganin yana maganane da Doctors ɗin da sukai masa rakkiya ya sakasu sauke ajiyar zuciya. Dan sun tabbata baiji komaiba.
Dr Yoohan yay sallama da abokan aikinsa kafin ya shiga motar da aka buɗe masa yana nai ɗaga musu hannu hamar yanda suke ɗaga masa. A haka motocin suka fito daga cikin asibitin.
“Sir! Zamu koma airport ne?”. Cewar Solomon fuskarsa ɗauke da murmushin jin daɗin kama Nu'aymah da har yanzu ya gaza barin fuskarsa.
Shiru Yoohan ya musu tamkar bai jiba, yama maida hankalinsa kan files ɗin daya fiddo a jikkarsa yana dubawa. Sake maimaitawa Solo yayi.
Nanma sai da yaja wasu sakanni kafin yace, “Police station”.
Ji kake ƙiyyyyy!!! Driver ya taka wani uban birki a firgice, tare da haɗa baki shi da Solomon waje. faɗin, “Police station kuma sir?!”.
(🙄🙄😏An yanka ta tashi ko masu gadi?).
Idanu ya zuba musu na wasu sakanni fuska a matuƙar ɗaure. Sai kuma ya ɗauke kansa ya cigaba da abinda ya keyi. Ganin gaba ɗaya wutar kansu ta ɗauke a fusace ya sake kallonsu “Kona canja yaren da nai maganar da shi ne bakuji wannan ba?”.
Da sauri suka shiga bashi haƙuri, driver ya ƙarama mota gudu zufa na keto masa ta ko ina a sassan jikinsa. Kai kace motar babu ac. kallo ɗaya zaka fahimci tsagwaron tashin hankali da ɓacin rai tattare da su. Driver bashi da wata hanyar daya wuce ya ɗauki hanyar police station ɗin da suka bar Nu'aymah. Acan kuma ƙasan ransu shi da Solomon tunanin mafita sukeyi.
Sunci rabin tafiya wani dabara yazoma Solo a rai,