Showing 69001 words to 72000 words out of 155423 words

Chapter 24 - A GARIN MU HAUSA NOVELS BY HAERMEEBRAERH.docx

26 Oct 2025

463

ci shi sun gama, amma me ke damun gudan jinin ta har jinin ta ya hau?

Cike da damuwa ta koma dakin, hawaye ta gani daga idon sultana ya na gangarewa a saman pillow duk da cewa  idanun nata na rufe ne.

Zama ta yi a gefen kan ta, tare da sanya hannu ta jaye gashin ta da ke gefen fuskar ta, ta shafa kan nata cikin kulawa da soyayya, irin ta uwa, cike da tausaya wa ta ce,

"Sulty Baby mi ka damun ki? Hawan jini? Mi ya maki zahi, da uwar ki da uban ki, ga dan uwan ki masu son ki? In akwai abinda ki ka so duniyar ga ki hwadi min ki na samun shi ko menene shi kuwa"

A wahalce Sultana ta daga ido ta kalli mahaifiyar ta, wadda take bata tsoro, tsoron gaske ma kuwa, dan bata san wanne ne halayen ta boyayyu ba kuma bayan wanda ta ji ta sani, cikin qunar rai ta ce,

"Kar ki damu,Wataqila wannan ciwon shi ne ajali na, wataqila kuma a hankali Allah ya yaye min, amma ku ba za ku iya min abinda nake so ba"

Cikin tsananin damuwa Hajiya Ikee ta sake mannewa a jikin Sultana, ta na jan ta jikin ta, da sigar lallashi, tausayi, soyayya, da tsantsar qauna,

"Habaaa Baby Sulty, wace irin magana ta wagga ki ke yi? Kin San dai ba abinda ki ke nema a duniyar nan ki rasa daga wajen mu, akan su wa muke fadi tashi dan mu tara abin duniya? Duk ba dan ku muke yi ba? Ki sanar da ni abinda ki ke so, yanzun nan zan sa a kawo maki shi"

"Hajiya kar ki damu, na fara lura da kuma sanin abinda za ki iya da wanda ba zaki iya ba, amma wannan kam na san ba zan same shi ba, Dan Allah ki bar wannan maganar ki tai an kusa sanar da sakamakon zabe"

"Rayuwar ki is more important to me, than anything else in the world my dear just tell me what you want and I will get it done for you yanzun ga"

Idanun sultana zafi suke kamar an zuba mata yaji, a hankali ta ware su a fuskar Hajiya Ikee wadda ta nuna tsantsar damuwa da gaskiyar maganar ta, na bawa sultana duk abinda take so.

"Auwal....Auwal shi ne abinda zuciya ta ka so, Auwal na ke so ku aura min, indai har da gaske ki ke za ki yi min duk abinda nake so, shi ne rayuwa ta, in ku ka hana ni auren shi Hajiya zan mutu"

Miqewa tsaye Hajiya Ikee ta yi tana kallon Sultana da wani irin kallon kan ki daya kuwa?

"Wane Auwal ki ke nufi? Lawwali driver? Ki na da hankali kuwa? Na haifi yarinya kamar ki, kyakkyawa, mai ilimin arabiyya da boko sannan ta b'ige da auren jahilin driver? Ki na hauka ne?"

"Hajiya ba fa jahili bane masanin qur'ani ne sosai, masanin qur'ani kuwa ai ba mai kira nai Jahili"

"Sai ni, ni zan kire shi jahili tunda banga alamar shi na aiki da shi ba, qur'ani ya hana neman ilimin boko ne? Namiji har namiji ace driving shikai? Ba da ni ba, kar ki bata min rai, ki nemi komai a waje na, amma banda wanga, yau ga zancen banza zancen yohi, to bari ki ji, kar ma ki kuskura ki wa mahaifin ku maganar ga, dan rai nai sai yahi nawa ɓaci, ba abinda ya tsana sama da talauci ga rayuwa tai, ba zai so ya miqa ki gidan wahala ba, na hwada maki tanadin da nake a kan ki, shi na ki ke debo min wahala? Sam ba zai yu ba,"

Ta na ta Masifa ta bar dakin, a qasan ran ta bata so suka rabu ta haka da diyar ta ta ba, musamman yanzu da bata da lafiya.

Sultana kuwa ko kukan ta kasa, tabbas sai yanzu ta fahimci me Auwal ke nufi,abinda babba ya hango dama an ce yaro ko ya hau rimi ba zai hango ba, ya riga ya fahimci ba za a bashi ita ba, ita kuma ta zaci son da iyayen ta ke mata zai taimake ta a bata wanda take so.

Ta na nan kwance ido biyu ta ji ana taken Nigeria, ana iface iface, a cikin gidan, rintse idanun ta tayi cikin qunar zuciya ta ce,

"Ban san sanda tallakan Nigeria zai bude ido nai ba, ban san sanda tallakan Nigeria zai fara addu'ar samun shugabanni wanda suka cancanta managarta ba, ba wanda suka so ba, ban san sanda tallakan Nigeria zai gyara tsakani nai da Allah ba, har Allah ya ji tausayin shi ya raba shi da shugabanni kamar su Daddy, ya Allah ka kawo mana qarshen wannan rayuwa mara aminci da muke ciki, ya Allah ka sa qasar mu Nigeria da duniya baki daya ta zama waje mai aminci ga bayin ka,"

"Ameeen Sulty Baby, ya jikin naki? Hajiya ta je ta na ta hwada, ban san akan mi take magana ba dai, amma na ji ta na akwai tanadin da ta yi akan ki, ko kin san akan mi taka magana?"

Murmushin da be kai ko ina ba ta yi wa Sultan da Ke bin ta da kallo, sannan ta ce,

"Ka manta mun je gidan dan takarar shugaban qasa?  To tun daga can ta fara ciniki na, ka shirya kaima za a yi naka kwanan nan, da ta samu wadda ta hito gidan kuddi za a saishe ka, Yah Sultan ina da wanda nika so, ta ce kar ma na bude baki na sanar da Daddy, sun gama maganar wanda za su bawa ni"

Hawaye ne suka fara tsartuwa daga idanun ta, ran Sultan ya ɓaci matuqa, zai d'auki komai akan shi, amma ba zai taba jure ganin Sultana cikin mummunan hali haka ba, nawa take har da za a ce hawan jini ya kama ta?

Cikin fushi ya bar d'akin, ta na ta kiran shi bai juya ba.

Ya na fita wayar ta na daukan ringing, da kyar ta janyo ta, ta na ganin sunan Auwal,  hannun ta ya d'au rawa, bakin ta na rawa saboda kukan da ya taso mata, ta na dauka kuwa ta fashe da kuka, Lawwali na jin kukan ta, ya ji wani abu mai qarfi ya daki zuciyar shi, ba ya son jin haka saboda ita, ba ya son jin damuwa da damuwar ta, amma ya kasa jurewa sai da ya tausasa murya ya ce,

"Ran ki shi dade ki yi min afuwa,na shiga matuqar busy ne, inda na tai ba network ,shi yasa ban dauka ba,amma ki yi hankuri, gani na dawo gida,dan Allah ki dena kukan"

Cikin shagwaba ta ce,

"In ka sake tafiya inda ba Network zan yi fushi da kai mai tsanani, ba zan sake kula ka ba"

Siririyar dariya ya yi, Sannan ya ce,

"A min ahuwa, in ki ka dena kula ni, ashe qarshen rayuwa ta ne ya zo, ba ke ba Mubaraka, lallai da zan zama kamar gunki, domin zan zam ba rayuwa a tare da ni"

Itan ma dariya ta saka, wadda ba zata iya tuna sanda ta yi dariya ba a ranar gaba daya.

"Na maka alqawarin sai ka mallake ni a matsayin matar ka, kuma sai mubaraka ta dawo gare mu lahiya"

Kalaman ta na qarshe ba karamin faranta ran shi suka yi ba,har ya ji sabon lamari game da ita...............

*Tambaya ta anan shi ne, Sultana da ke yi wa Lawwali alqawari, ta manta maganganun Hajiya ne?*

💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻

BY HAERMEEBRAERH

PAGE 34:

"Dakata min Sultan, kai har ka isa ka taho ka yi min titsiye? To bari ka ji, kai kan ka, ina nan na tanadar maka wadda za ka aura, lokaci nika jira, ta na kammala digirin ta ta dawo qasar ga za a daura muku aure, diya ce ga minister'n tsaro, kuma babbar diyar shi, na duba wayar ka tass na ga duk matan da ka ke mu'amala da su, duk ba ya wuce gaisuwa, Ita dai nigga ku na hira jefi jefi, tunda Allah ya sa hankalin ku ya gamu waje guda, Daddyn ku ya ma iyayen ta magana, kuma sun yi na'am, ka shirya, ana gama auren Sultana naka za a yi"

Baki Sultan ya sake kawai ya na mamaki, ya na namiji amma ana so a masa auren dole, to ba ma wannan ba, in an masa auren dole ya hakura tunda dama baida budurwar da ta kwanta masa ga rai, to ita sultana da ke son Lawwali fa?

"Hajiya na amince ku aura min duk wadda kuka so, amma fa ba zan amince ku aura wa sultana mutunin da bata qauna ba"

"To Uban mu, mun jiya, in an tashi auren sai ka hana,...dalla fita ka ban waje, yau so kuke sai kun batan duk wani farin ciki da nake ciki na ga alama"

Daddy ne ya shiga dakin bakin nan kamar gonar audiga, cikin, farin ciki ya ce ma Sultan,

"Ku shirya kai da qaunar ka gobe akwai party, around 1am, kwana za a yi ana murnar samun nasara, diyoyin gwamnoni ne suka partyn a Abuja, na san za ku buqaci kudi sosai, dan kusan kowa a wajen ya na taqama da uba nai, ga wannan, ku dauki duk nawa ya muku"

Wani dan kati ya miqa masa,wanda yake a matsayin makullin ma'ajiyar kudin Gwamnan, kallo kawai Sultan ya bisu da shi,ya kasa cewa komai, da kyar ya bude baki ya ce,

"Yaushe ku ka zama haka? Yaushe kuka dena damuwa da abinda muke so sai wanda kuke so? Yaushe za ku saki duniya, ku kama qiyama?"

Daddy bai fahimci ina Sultan ya dosa ba, ita da ta san akan me yake magana, tuni ta miqe, ta na son kawar da zancen Sultan ya sa kai ya bar dakin.

"Kwantar da hankalin ka ka jiya diyan ga in ka ce kabi nasu to fa ruwa ma sai an tauna musu an hadiye musu tsabar gata"

"Amma mi an kai mai ? Ban taba ganin Sultan ya yi hushi haka ba,mi kin kai mai? Ki hwadi min gaskiya ko inna bincika  na gano kin masa wani abu ran ki zai ɓaci, ban hada d'iya na  da kowa ba"

"Ni kuma ni na haihe su , har da ka ke hwadi min baka hada d'iyan ka da kowa ba, maganar wannan yaron driver ne taqi qarewa gidan ga, ya zo ya na wani hwadin magana yanda ya ga dama, to shi kan shi na sanar masa magana diyar Minister , shi na yake hushi "

Shiru ya yi bai ce komai ba, ya fita ya bar dakin, bai tsaya a ko ina ba sai dakin Sultana, ta na bathroom, ta na alwala, sai da ta gama ta fito taga wayar ta a hannun shi, ya na duddubawa, har ta isa gaban shi bai aje wayar ba sai da ya gama abinda yake.

"Sultana da dukkan alamu ki na son Lawwali, amma Sultana ki sani, ke baki san waye Lawwali ba, ni na san waye shi, ina mai baki shawara da ki hakura da shi, tun da wuri, tun lokaci bai qure miki ba"

"Daddy kenan, indai Hajiya ta ji ta gani, ta ke zaune da kai, banga dalilin da zai sa ni na kasa auren driver na ba"

Cikin rashin fahimta ya ce,

"Me ki ke nufi? Sultana yaushe kin ka hwara magana irin wannan? Me ki ke nufi da abinda kin ka hwadi yanzu?"

"Never mind Daddy, ina so nayi sallah, pls"

"Sultana ina son sanin damuwar ki, talk to ur Daddy Sulty Baby, ki sanar da ni mi ki ka so"

Cikin kuka ta ce,

"Daddy ka tambayi Hajiya, ta san komai, dan Allah ka barni na gana da Ubangiji na, shi ne kaɗai zai min maganin damuwa ta, Hajiya ta tabbatar min da ba zan samu me nake so wajen ku ba, yanzu ka tabbatar min da na hakura da farin ciki na, saboda bai muku ba, bai yi daidai da abinda kuke so ba, ni Auwal nike so, ba wani shugaban qasa ba,"

Daddyn su ne ya ja ta jikin shi ya na lallashi, a zuciyar shi kuwa ya na mamakin sanda ya yi sake Lawwali ya yi nasarar dasa soyayyar shi a zuciyar sultana haka, sai yanzu yake tunawa da alamomin da Hajiya ke sanar da shi, lallai ya yi sake, Lawwali na shirin yi masa babbar illa, indai har ta nan ya biyo.

"Ya isa kukan haka nan, zan yi tunani akan maganar, ki daina kuka"

Da sauri ta kalle shi, ta na son tabbtar da gaskiyar maganar shi, dan yanzu gaba daya ta cire yarda a tsakanin su, gani take komai nasu qarya ne.

Sai da ya ga ta daina kukan ya bar dakin, wajen Hajiya Ikee ya koma, ta na zaune ta zabga uban tagumi ta na tunanin yanda za ta raba tsakanin Lawwali da sultana.

"Ki na da gaskiya ashe da kin ka ce  na kori yaron nan daga gidan nan naqi ji, ashe ya min babbar illa ina zaune ba tare da na sani ba?"

Kamar an sosa mata inda ke mata qaiqayi haka ta miqe, kallon lokaci ta yi, ta ga ya tafi sosai, ta gaji tilis, kuma maganar nan na buqatar dogon nazari, ko kadan ba ta son batawa Sultana, amma dole ne ta raba tsakanin su da Lawwali.

"Wannan magana ta riga ta wuce, yanzu mafita za ka nemo mana, dan kuwa ba zan taba yarda diyar ciki na ta auri driver ba, yau ko min muqamin da za ka damqa masa a gwamnati walle ba ya hanawa a kire shi da driver, ba zan zama abin dariya cikin abukkai ba,dole ka dau mataki"

"Ba zaki gane ba, yanzu raba tsakanin sultana da Lawwali babbar musiba ce wallah, duk yanda zan miki bayanin yaron nan ba zaki gane ba, ni na san wane ne Lawwali,"

"Driver din? Me ye ba zan gane ba? Yau muke tare, ka kore shi kawai, shi bar gidan"

Bai ce mata komai ba ya fada bathroom.

Mita ta dunga yi tare da fadin ya sa yaron shi din nan da ke masa aiki, a sace Lawwalin ya bar doron qasa baki daya, Indai ze zame musu fitina akan dukkan tsarin su.

*************************

Sai guje guje suke abin su a katafaren tsakar gidan kakannin nasu, cike da nishad'i da jin dadi, ita kan ta Hajiyar Hansatu rabon ta da fitowa farfajiyar gidan haka ta manta, Hansatu na ta tuna yarintar ta, zaune suke a saman kujeru na qarfe masu matuqar kyau, gaban su table ne an aje fruits da abin sha, su na ta hira a tsakanin su, wanda ya san Hansatu sati Uku da suka wuce ya gan ta yanzu ba zai gane ta ba, ta ciko ta murmure, ga wani haske da ta yi, in ta saka riga da skirt sai ta cike su famm, ban taba zaton hansatu na da shape haka ba sai yanzu.

Hajiya ce ta kalle ta ta ce,

"Gaskiya ya kamata a sauya maki waya, yanzu da yar wayar nan ta zamani ake hira da miji, sai ku yi chatting din ku kamar ku na tare, haka naga Yayan ki na yi da waccan maras kunyar da ta qi dawowa, amma fa soyayya a waya kamar Juliet,"

"Hajiya wai mi an kai mata ne haka?"

"Wannan fa baki gane alqiblar ta, dan yanzu ko an ce mi yayi mata bata hwadi, ta na can qasar waje, da alama can taka so su koma da zama, tunda can ta yi rayuwar ta, ni kuwa ba me d'auke min yaro shi tai wata uwa duniya"

"Ohhh amma ko bata kyauta ba gaskiya, ai mace hankuri aka santa da shi a gidan miji, ba irin wanga hali ba"

"Haka ne, ita kam sam bata san wannan ba, komi so takai ayi yanda taka so, ba ko shi yiwa,"

"Allah to ya shirya ta, ya sa ta dawo su ci gaba da zaman su lahiya,"

"Ameen dai"

Su na tsaka da hira Hajiya ta dauki waya, ta kira Yayan Hansatu, tace ya aiko mata da waya mai kyau, kafin Hansatu ta wuce, amsawa ya yi, da toh, sanan suka yi sallama.

Hansatu bata koma gida ba kuwa sai da dalleliyar waya mai kyau, ba ta wani murna da wayar kawai dai ta nuna ta na murna ne, domin kuwa wanda ake mata kwadayin su yi hirar da shi, tunda ya tafi sai dai taji labari wajen Hajiya sun yi waya, amma baya kiran ta, balle ta samu No shi, kuma ita ba zata iya tambayar hajiyar ta No isah ba.

Ko a mota ajiye kwalin wayar kawai ta yi a cinyar ta ta na tunani, ga dai shi ya tafi, kuma ya fadawa Hajiya kasuwancin goro yayi albarka, amma ko sisi bai masu aike ba, bata san ranar dawowar shi ba.

A qofar gidan su motar ta tsaya, fitowa suka yi ita da yaran, kowa ya gan su ya ga jikokin masu azziqi, hatta da takalmin su yanzu mai tsada suke sakawa.

Ko kallon majalisar su 'yabbuga bata yi ba, ballantana ta ga yanda suka sanya mata ido su na gulmar ta.

Sallama ta yi da driver suka shige gida.

Can majalisar su Lamishi kuwa banda gulmar su ba abinda suka ke.

"Hummmm wagga ai ni zan baki labarin Hansatu ta sauya, bari dai, ai za su koma yar gidan jiya ne, ta na zuwa roqon abu zan mata kaca-kaca, yanzu ta koyi walaqanci,ko kallo bamu ishe ta ba,dan ta hwara daura suhwa, da holan, walle ta na barin shi"

"Ohhh ke kuwa me ya sa kin ka ce haka? Ai ba kin mata hwatan komawa gidan jiya ba, indai ta sha wahala yanda kun ka ce"

'Yabbuga ce ta kalli Asshibi a sheqe ta ce,

"Na hwadi, na ce na hwadi baki ganin wani kallon walaqanci da takai wa mutane?"

"Ai kuwa ko kallon wajen ga ma bata yi ba"

"Tauuu PA din Hansatu, ko zuwa zaki ki hwadi mata mi nicce?"

Lamishi da ta zabga tagumi ta na tunanin shin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login