Showing 15001 words to 18000 words out of 86229 words
Chapter 6 - GIDAN MISBAHU COMPLETE BY SIDIYA SIDI .txt
fito a parlour suka taradda su daddy. Cike da k'warewar zamantakewar rayuwa na yau da kullum Haajar ta k'arasa tana fad'in_
_"Allah sarki Dan Allah kuyi hak'uri nasan kuna ta jira ,ni ban ma zata kun tashi bane"_
"Au to bari kar mu tashi ,tunda ana cin bacci a k'washi ne" inji Hajj Jamil kenan.
Shidai Daddy se dariya yake musu. D'an gurfa nawa Haajar tayi ta gaishe da Daddy ,fuska a sake ya amsata ,sannan ta gaishe da Hajj Jamil cike da girmama wa. Su suxee ma k'arasowa suka yi ,suka gaishe su a ladabce. Hajj Jamil janyo Auta yayi yana fad'in
"Autar daddy yaya? Kinsha bacci ko?"
Itadai auta se gyad'a masa kai take yi ,Dan tana da wani Abu d'aya ba ,matuqar tazo bak'on wuri koma wa take yadda kasan ruwa ya tafi da ita ,wannan kuma ba tarbiyyan kowa bane face Haseena, ba kuma wai Dan basu saba da Hajj Jamil bane ,har gidan shi suna zuwa lokaci bayan lokaci ,se dai basu tab'a zuwa sun kwana bane ,shiyasa suka kasa sabawa da gidan ,sannan da ace akwai qawance me k'arfi ne tsakanin kubra da Hajiya zaliha matar Hajj Jamil to da shak'uwar tafi yawa ,to kubra bata qawance se daidai da ita ,Hajiya zaliha bata cikin tsarin irin matan da ajin su yakai a wajen kubra, Hajj Jamil dai da daddy su suke Abokan tan su cike da nuna wa juna qauna, Dan da sun biye matan su ma baza su yi ba ,to se Allah yasa Abokan takan su bana yanzu bane ,Abotar su ta samu asali ne tun suna yara ,komai nasu tare suke yi ,har suka zama kamar 'yan uwan juna ,duk abunda ya shafi d'aya kamar ya shafi d'aya ne...
Su suxee kujera suka ja suka zauna ,inda Haajar ke serving d'in su ,su daddy ta fara zuba wa ,sannan ta zuba wasu haseena ,kowa yaci abincin se santi suke yi ,banda Auta da se wani cakalan abincin take yi, Haajar na lura da ita tace
"Auta ya ke bakya cin abincin?"
Cike da shagwab'a Auta tace
"Ni na k'oshi"
Karaf Haseena ta k'wace zancen "A-hap! Auta ce fa, ai wallahi baki ga komai ba indai wajen cin abinci ne ,haka take"
"A'a ba wani ,Ku dai bakwa mata yadda zata ci d'in ne." Cewar Haajar ,sannan taci gaba da cewa "Auta zaki sha chocolate? " da sauri Auta ta kad'a kai ,Dan an ambato mata favourite d'in ta.
Haajar taci gaba da cewa "yauwa to taso abinki kinji ,indai kika ci abinci sosai naga kinci ,to zan baki chocolate kisha kin ji".
Mak'e ka fad'a Auta tayi alamar rashin yadda. Wanda seda abun ya bama kusan kowa dake wurin dariya , itama Haajar d'in dariya take ,tashi tayi taje d'aki ,ta d'auko mata chocolate d'in tare da cewa " kin gani ko ,to zaki ci se in baki"
Ba musu Auta ta sauka kan carpet inda Haajar d'in ke zaune da plate d'in abinci. A baki tashiga bata ,har seda taci sosai ,sannan ta mik'a mata chocolate d'in. Kowa se jinjina lamarin yake ,yau Auta ce taci abinci sosai haka, Daddy kam abun ba k'aramin burge shi yayi ba ,dan yana matuqar son a nuna wa yaran shi kulawa...
Bayan sun kammala, Haajar da Suxee suka kwashe komai suka kai kitchen, haseena kuma ta tsaftace dinning area d'in. Daga nan daddy da Hajj Jamil suka koma parlour suna ta tattauna matsalolin yau da kullum, a inda su Haajar suka fara shirye-shiryen d'ora abincin rana.
A tattaunawan da Daddy keyi da Hajj Jamil ne yake sheda masa tafiyar zuwa kano. "To amma tafiyan Nada muhimmanci ne?" Hajj Jamil ya tambaye shi
Daddy yace "eh to Hajiya Gwaggo ce ke kirana ,kasan wancan zuwan Dana yi bata da lafiya an tafi da ita Sudan, to nasan baze wuce labarin auren khaltum da akayi bata nan ba"
Ajiyan zuciya Hajj Jamil ya sauke ,kafin yace "To ina ganin kaje kai kad'ai kabar su Hajiya k'arama anan ,Dan kar kaje dasu kuma Abu na babban gida ,se ya zama gutsiri tsoma, in yaso duk yadda kuka yi Seka sanar mun"
Cike dajin dad'i ,daddy yace
"To shikenan.
" kwana nawa zaka yi? Hajj Jamil ya tambaye shi
Daddy yace "Har wani kwana ki zan ke inyi ,inaga cikin ma nayi in kwana d'aya ko biyu".
" to ba damuwa ,Allah ya kaika lafiya ,ya kuma dawo dakai lafiya"
Daddy ya amsa da "Ameen"
Seda suka ci abincin rana ,Daddy ke sheda wa suxee tafiyan shi ,sosai taji dad'in daya ce ze bar su a gidan Hajj Jamil ,Dan dama abun da ke ranta kenan ,badan komai ba sedan Haajar ,lura akwai abubuwan k'aruwa sosai da baiwa a tattare da Haajar. Addu'a ta masa na Allah ya tsare.
Misalin k'arfe uku na rana Hajj Jamil yakai daddy Airport, tare da masa addu'an Allah yasa suji alkhairi, duk da a k'asan zuciyar Hajj Jamil yasan Abu ne me wuyan gaske ace Hajiya Gwaggo tayi wa mutum kiran azziki, amma ba yadda ya iya ,sedai yabi lamarin da Addu'a...
_GARIN KANO, HAD'EJA ROAD..._
MUJE ZUWAπ
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...βοΈ
[7/20, 2:45 PM] SIDIYA...βοΈ: π π *GIDAN MISBAHU*π π
π π π π π π
π π π π
π π
π
*_π (base on true life story)_*π
*_π INTELLIGENT WRITERS ASSOπ_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)βοΈ*
_BABI NA SHA HUD'U_
*__________________________*
_Daddy na isa kai tsaye sashen Hajiya Gwaggo ya nufa ,be ko yi tunanin fara ganin hajiyar shi ba ,Dan kuwa matuqar Hajiya Gwaggo ta samu labarin seda ya biya can kafin ya shigo wurin ta ,to fa jarabar duniya se Wanda ta manta ,kai bashi kad'ai ba hatta hajiyar tashi ya ja mata jangum. Gashi dai asalin mijin Hajiya Gwaggon ya rasu ,wato kakan daddy namiji ,amma bashi yasa Hajiya Gwaggo ta canza wasu halayen nata ba ,ita ke mulkin komai tun kakan daddy Nada rai ,ba Wanda ya isa ya d'aga d'an tsaya matuqar tana wuri ,da tace 'Eh' kuma ba a haifi Wanda ze ce a'ah ba, kishiyar ta Hajiya sakina ba k'aramin wahala tasha ba a hannun Hajiya Gwaggo ,musamman ita da yaran ta mata ne gaba d'aya ,bata tab'a haihuwan namiji ba ,ita ko Hajiya Gwaggo yaranta biyar maza ,kakan daddy shine Auta ,to fa se abunda ta b'ata, wannan yasa lokacin da me gidan ya rasu ,ta kame komai tayi kane -Kane ,rabon gado ma da akace za'ayi hana wa tayi ,daga k'arshe ma kawai se ta kuka ,wai dama so ake ya mutu aci gado ,to ba abunda ya isa matuqar tana da rai , ba yadda za'ayi da ita ,haka aka hak'ura aka k'yale ta ,haka dai kishiryar tata ke zaman hak'uri a gidan ,da Allah ya tashi nuna ikon shi ma ,gaba d'aya yaran Hajiya sakina biyar mata ,manya-manyan attajirai suka aura ,daga wacce ta aura mijin ta bako sisi ,suka kud'ance tare ,se wacce taje ta taradda azzikin, ba yadda basu yi ba akan ta koma d'aya daga cikin gidajen da aka Gina mata amma ina k'yameme Hajiya sakina tak'i ,saboda ta saba da zaman wannan family house d'in. Duk kuma lokacin da zasu zo da abun azziki ,ko da basu yi niyyar bawa Hajiya Gwaggo ba ,tilas Hajiya sakina ke matsa musu se sun je sun bata, saboda a zauna lafiya ,sannan rayuwar mu ba d'aya ba ,Hajiya sakina mace ce me sauqin hali da faranfaran da mutane ,ita ko Hajiya Gwaggo tak'adarin budurci ne ke yawo akanta sama da shekaru aru aru Ana Abu d'aya, da Allah ma yaso nuna mata ishara ,kaf a 'ya'yan ta mazan nan data ke tak'amar ta Haifa gwal ,Alhaji k'arami Baban Daddy shine kad'ai Wanda Allah ya d'aga a cikin su ,shiyasa komai nashi take ham-ham. Sannan kaf a sauran 'ya'yan daga Wanda yabar 'kasa zuwa Neman nakan shi ,se Wanda yana wani gari da iyalan sa ,Baban daddy ne kawai tayi wa kafi a kusa da ita. To sauqin suma tsufa daya kamata gadan-gadan ,ciwon yau daban na gobe daban. Wannan kenan..._
_Sallama yayi ,ba kowa a sashen duk mutanen gidan suna sashen Hajiya sakina ,Dan kusan kullum acan ake wuni. K'arasa wa yayi suka gaggaisa ,Hajiya sakina na tambayar shi iyalan sa ,yace duk suna lafiya. Ba wani jimawa yayi ba ,Dan yasan masifar kakar tashi ,yace wa Hajiya sakina_
"Bari inje mu gaisa da Hajiya Gwaggo"
Tace "To shikenan. Ga wannan hurar me sanyi kaje da ita kasha ,yanzu na gama damun ta kaga ludayi nan gashi, nasan an kwaso hanya" ta mik'awa daddy k'waryan furan ,daya ji kidirmo ,ga k'ank'ara an farfasa a ciki. Kai daga ganin furar nan zata yi dad'i musamman irin lokacin zafin nan...lolzπ
Godia Daddy ya mata sosai, sannan ya d'auka ya nufi sashen Hajiya Gwaggo, a lokacin ta fito daga ban d'aki. Har k'asa ya zube ya gaishe ta a ladabce kamar yadda ya saba. A yatsine ta amsa shi. Kafin ta soma halin nata
"Se yau kaga damar zuwa ,ko da yake inaga se yau uwar taka suwaiba ta baka izinin zuwa inajin ,wato ni ban isa ba ,ban kuma da muhimmanci a wajen Ku dahar zaku yi Abu ba tare da kun sanar dani ba ,tun ba yau ba ,na riga na gane dakai da uwar ka suwaiba so kuke in mutu, to wallahi ahir d'in Ku ,k'walelen kare da antar kura ,ni d'in nan da bakwasan gani wallahi se kun ganni.
To kunyi yadda kuke so ,yanzu nima zakaji nawa hukuncin ,saboda haka ka bud'e kunnuwan ka dakyau kaji ni. Kai bama zan fad'a a gaban ka kai kad'ai ba tashi muje ayi a gaban suwaibar".
Tana gama fad'in haka tayi gaba. Shidai daddy be ce mata ci kanki ba ,Dan Allah yayi mai sanyin hali ,girgiza kai kurum yayi sannan ya tashi yabi bayan ta.
A b'angaren hajiyar daddy ,tun da taji sallamar Hajiya Gwaggo gaban ta ya shiga dukan tara-tara ,Dan tasan azziki baya kawo ta se dai akasin shi. Tsaye ta tashi tana mata sannu da zuwa ,sallamar Daddy yasa ta maida duban ta gun k'ofar shigo wa ,a mamakin shine yaushe Daddy yazo? Kuma meya kawo shi a wannan lokacin? Gashi ta ganshi da Hajiya Gwaggo, tasan ko ba'a fad'a mata ba ita ta kira shi. Nan fa hankalin ta ya k'ara tashi ,Dan tasan wani matsalar ce zata kunno kai.
Daddy gaida Hajia yayi ,ta amsa fuska a sake. Bata ko zauna ba ,ta mike ta d'auko wa Hajiya Gwaggo ruwa ,taje a gaban ta
"Ba ruwan ki ya kawo ni ba ,ni za'a gaya wa ruwa ,nida keda ruwan tukunyar k'asa ta dauri ,masu k'ara lafiya. To ki saurare ni dakyau. Kunyi San ranku ,azzikin Ku d'aya da bana nan. Kinje kin nemo masa mata kin aura mata ,kuma 'yar wannan battalalliyar qawar taki, saboda kun ga jini na me kyau ne ,anga azziki ,shine Dan mugunta Dan kika nema masa aure, to bazan ce ya sake ta ba ,tunda an riga anyi ,amma ina me tabbatar miki ,Wani auren ze sake ,kuma nice nan zan sama masa mata 'yar azziki..."
Daddy ji yayi kamar an buga masa guduma... Hajiya ma haka taji abun kamar saukar aradu, wai Aure...
"Aure kuma???" Daddy ya furta ba tare dama yasan maganar ta fito fili ba
"Eh aure. Wannan umurni na ne ba shawara ba". Hajiya Gwaggo ta fad'a tana wani irin gimtse fuska ...
MUJE ZUWAπ
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...βοΈ
[7/21, 3:08 PM] SIDIYA...βοΈ: π π *GIDAN MISBAHU*π π
π π π π π π
π π π π
π π
π
*_π (base on true life story)_*π
*_π INTELLIGENT WRITERS ASSOπ_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)βοΈ*
_BABI NA GOMA SHA BIYAR_
*________________________*
_Magana daddy yaso yi amma Hajiyar shi ta katse shi. K'ak'aro murmushin dole tayi ,kafin tace "Hajiya Gwaggo insha Allahu zaki same mu masu yi miki biyayya, kada Allah ya kawo randa zaki yi magana ni suwaiba ince ba haka ba ,ki qaddara bani bace insha Allahu Rabbi. Aure kuma ba wai nayi wa Daddy shi akan wata manufa bane, nayi mishi ne ko Dan in Samar musu nutsuwa shi da iyalan shi. Amma Dan Allah kiyi hak'uri idan kina ganin an miki ba daidai ba"_
_tsabar jaraba irin na Hajiya Gwaggo duk lallamin nan da Hajiya tayi mata be yi nata ba ,a'a wai Dan me za'a ce mata idan tana ganin an mata lefi tayi hak'uri, nan fa ta fara zazzaga musu ,se abunda ta manta. " Nace dai ba ke kad'ai kike da iko dashi ba ,har wani wai idan an mun lefi in yi hak'uri, to bazan yi hak'urin ba da guntun tsugudidin ki, ba abunda ya kawo ni ba kenan. Kai kuma..."_ _ta fad'a tana nuna Daddy dake zaune ya sunkuyar dakai ,shi kad'ai yasan me yake ji a k'asan ran shi. D'an d'agowa yayi yana duban ta ,ai fa wannan be yi mata ba "Au bazaka iya amsawa ba ,kai kurma ne? To ka amsa ko kar ka amsa wannan matsalar ka ce"_
_Taci gaba da cewa " Yarinya dai ba wata bace in la wacce nasani kuka Sani ,yarinya 'yar gidan mutunci ,ga kamala da tsari. Sama da shekaru aru-aru da muke zaune a layin nan ban tab'a jin ance sunyi rigima da wuni ba, ba kowa bace illa LUBABATU... Kai idan baka sheda ta ba , ita suwaibar uwar ka ai ta Santa farin Sani ,balle ma baka isa kace baka gane wacce Lubabatun ba, saboda duk zuwan da kayi tana zuwa yi maka sannu da zuwa ,har ma tayo maka girki. Saboda haka na gama magana da iyayen ta ,se da nayi da gaske ma kafin suka amince ,mun kuma tsaida ranar biki ,nan da wata biyu me kamawa, se ka fara shirye-shirye ,ka kuma turo mana da isassun kud'i ,kar muji kunya ,kaji na gaya maka, kafin ka tafi se ka leqa Ku gaisa"_ _Hajiya Gwaggo ta k'arasa fad'a yayin da take barin d'akin..._
_Wani takaici ne ya tokare wa Daddy mak'oshi ,babu ma abunda yafi bak'an ta mishi rai ,irin da Hajiya Gwaggo ke cewa ,seda tayi da gaske sannan aka bata wannan auren ,kai kace saka ta yayi. Wani abun takaicin ma wai ya leqa ,kamar shi ,maimakon ma tace zan tura a kira maka ita ,shine zata ce ya leqa da girman shi"... Daddy ke ta zancen zucin shi shi kad'ai.
Ita dai Hajiyar Daddy kusan bugun zuciyar ta ne ya kusa tsayawa cak ,,,, Dan wannan ba k'aramin al-amari bane. Ta gane Lubabatun da ake magana ,se dai tana jin wasu rad'e-rad'in maganganu marasa dad'i akan gidan su ,ta kuma ji ance ta tab'a aure ,amma fa badan ta tabbatar ba. Wani gajeren ajiyan zuciya ta sauke ,tare da zuba wa Daddy ido, ita gaba d'aya ma wallahi tausayin shi take ji ,shi ba wani babba ba can amma duk an taru an kashe masa rayuwa da gurb'atattun mata marasa tsoron Allah. Gashi bata da wani abun yi daya wuce ta dage wajen gayawa Allah... Hajiya keta sak'e-sak'e a ranta. Kafin ta kira sunan daddy cikin Muryar lallashi.
"MISBAHU!!!" Da sauri Daddy ya d'ago ,Dan idan baze manta ba wannan shine karo na biyu da Hajiya ta kira sunan shi ,tun da kuwa yake da ita.
A sanyaye ta fara basa baki "Kayi hak'uri kuma ka d'auki abunda abunda yake faruwa dakai a matsayin qaddarar rayuwar ka. Allah na sane dakai ,be manta dakai ba. Cewar kawai kayi imani bashi ze sa Allah ya kasa jarabtar kaba, dole ne ayi maka gwaji ,musamman ma kai da Allah yayi wa bud'i. Menene Allah be baka ba na duniya? To se kuma kace a had'a maka dad'in duniya gaba d'aya? Baze yu ba ,Shiyasa Allah ya maka jarabawa da mafi girman jarabta, Dan mace qalubale ce ,kuma babbar jarabawa ce a rayuwa. Dan haka kayi k'ok'arin danne zuciyar ka wajen ganin ka ci wannan jarabawar. Sannan kar ka damu zanyi iya bakin k'ok'ari na wajen yin bincike akan ita wannan yarinya ,Addu'a kuma ba fasawa nayi ba koda yaushe albarka ta na tare dakai. Kar ka kuma yi mamakin wannan itace jarabawar ka ta k'arshe ,ta iya yuwa kuma a wannan karon kaji dad'in aure ina fatar hakan..." Shiru ne ya biyo baya nad'an wani lokaci kafin Hajiya ta tambaye shi "to yanzu ya zaman iyalan naka yake a can?"
A tunani na ko Daddy ze gayawa Hajiya duk abunda yake faruwa ,sedai Banyi mamakin jin be wani tsawaita zancen ba ,Dan Allah yayi Daddy wani mutum me matuqar zurfin ciki. A sanyaye yace
"Suna can lafiya qlau ,sedai zaman ba dad'i gaba d'ayan su ,Dan kusan duk wani Abu da kubra keyi shi khaltum ta koma yi ita ma ,duk dai abun se hamdala".
" Oh Allah! Ka kawo mana d'auki da sassauci acikin wannan al'amarin" cewar hajiyar Daddy.
Daddy yace "shiyasa naso ace da Hajiya Gwaggo zata bar maganan auren nan ,jna ga zefi sauqi ,wancan wutar ma dake gaba na se dad'a huruwa take ,balle kuma ace na kai wata ,Hajiya kar fa su kashe ni"
Murmushi irin nasu na manya Hajiya tayi tare da cewa "bame kashe wani se kwanan shi ya k'are ,rayuwar ka ba'a hannun su take ba ,a hannun Allah take, idan ma wannan bashi bane k'arshen