Showing 57001 words to 60000 words out of 86229 words
Chapter 20 - GIDAN MISBAHU COMPLETE BY SIDIYA SIDI .txt
yasa har ta yi sha'awar su had'a jini. Shine lokacin da Hajiya ta had'a auren daddy da Khaltum d'in.
Duk Wanda yaga Khaltum a wannan halin da ta take ciki a yanzu sai ya tausaya mata matuqa. Ga ta a kwance da ita da gawa ba su da banbanci ,ba um ba u'um.
Hajiya khairi na kuka ta shiga Neman yafiyar hajiya akan abubuwan da suka faru. Duk da hajiya na takaicin sanin hajiya khairi da ta yi. Be hana ta yafe mata ba. K'anwar mahaifin Khaltum da aka zo tare da ita ne ta dinga maidawa Hajiya khairi da martanin abubuwan da suka faru. Hajiyar daddy ta yi ta mata fad'a akan ya kamata su yadda da qaddara komai ya wuce. Mahaifin Khaltum har hawaye sai da ya zubar lokacin da ya halin da 'yar shi ke ciki. Da Hajiya khairi ta nema yafiyar sa ko kad'an bai yi qasa a guiwa ba wajen yafe ta ba saboda 'yar shi.
Dikkan su suna zaune kowa sai sannu yake wa Khaltum da bata San suna yi ba. A hankali Khaltum ta bud'e idon ta ta zuba su kan k'ofar shigowa. Hannu take k'ok'arin d'agawa tana nuna k'ofar ,amma ba su ga kowa ba. Jini ne ya shiga fito ma ta hanci da baki, a gefe d'aya kuma tana ci gaba da nuna k'ofa.
Da sauri Haajar ta je ta kira likitocin da ke kula da ita. Amma kafin su k'araso rai yayi halin shi. Dan kuwa Allah ya yiwa Khaltum rasuwa.
Hajiya khairi ta yi kuka kamar ba gobe. Kowa sai da ya tausaya mata. A ranar da jimamin abun su hajiya su ka koma gida. Washe gari aka wuce aka wuce da gawar Khaltum Dan ayi mata sutura akai ta gidan ta na gaskiya, Wanda tare da mahaifin Khaltum d'in aka wuce...
MUJE ZUWAπ
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA...βοΈ
[8/20, 12:19 PM] SIDIYA...βοΈ: π π *GIDAN MISBAHU*π π
π π π π π π
π π π π
π π
π
*_π (base on true life story)_*π
*_π INTELLIGENT WRITERS ASSOπ_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)βοΈ*
_BABI NA ARBA'IN DA UKU_
*___________________________*
Washe gari da yamma su Haajar na zaune a sashen Hajiya su na ta qara ji manta al-amarin da ya faru jiya a asibiti, sai ga wani al-amarin ya sake zuwa. Dan kuwa Barr Kabir ne ya zo musu da labarin cewa an yanke wa Lubabatu kisa ta hanyar rataya ,sakamakon kisan kai da ta yi har so biyu ta kuma yi yunqurin sake aikwatar da wani a karo na uku ,wannan ne yasa babu wani hukunci da alqalin ya ga yafi cancanta da Lubabatu bisa ga doka sama da rataye ta ,a hakan mai wai an yi mata da sauqi ne. Wannan labari shi ma ba kad'an ba ya sake d'aga hankalin su hajiya ,Haajar hadda zubar da 'yar k'walla saboda tausayi. Barr tambayar Hajiya ya yi akan ina Daddy? Hajiya tace "ai tun lokacin da komai ya warware Daddy ba ya zama Dan yanzu ma harkokin kasuwancin sai dad'a bud'e masa suke yi". Abu mai San yi Haajar ta kawo wa Barr tace wa hajiya " ni zan je in kwanta kai na ne ke d'an mun ciwo ". Hajiya tace " to Allah yasa kaffara ne. Ki tabbatar kin sha magani kafin ki kwantan. Tukunna ma kin ci abinci?" D'an sosa k'eya Haajar ta yi tare da cewa "Na sha shayi d'azu hajiya" hajiya tace "to ai ka ji shashanci. Wai shayi? Naga shayi ai ruwa ne ba abinci ba. Mutum yasan ba shi kad'ai ba amma sai sakaci. To maza kije ki nema abinci ki ci kafin ki fara aikin baccin". Murmushi Haajar ta yi tace " To insha Allahu zan ci hajiya". Hajiya tace "to ai shikenan. Sai kin fito" daga haka Haajar ta yi sallama da Barr ta wuce sashen ta. Kusan duk lokacin da Haajar za ta ji abunda ya d'aga mata hankali sai kan ta ya yi ciwo Wanda idan ba bacci ta samu ba bata samun sauqi, ita kuma da haka laulayin yazo mata.
Barr kafe Suxee da ido ya yi, da ke kwance tana aikin daddanna waya. Hajiya tace "tashi Hajiya k'arama ki canza mana tasha zuwa sunnah tv saboda k'aratowar magriba." Ta shi suxee ta yi ta canza tasha kamar yadda Hajiya tace sannan ta dawo ta kwanta. Barr yace "Hajiya na ji kince Hajiya k'arama? Ba dai ita bata wannan ta girma haka?" Murmushi Hajiya ta yi irin na su na manya tace "Yo kai da kabiru da wautar ka da wacece?" Yace "wallahi Hajiya ban d'auka ita bace ,saboda nasan ai ke d'in ta mutane ce ba'a raba ki da jama'a. Na ga ta girma ne sosai". Hajiya tace " Lallai kuwa ga ta nan dai. An gama makaranta tuni ,banda Hajiya Gwaggo ma ta hana da yanzu ta yi nisa a karatun jami'a. Ina ga ko dan ba'a k'asar ka ke zaune bane tun wancan lokacin shiyasa ,kuma kaga ba Ku tab'a had'u wa a kano waje na ba. Lokacin da zasu zo sai sun tafi da jimawa kai kuma sai ka zo."
Da mamaki Barr yace "wannan haka yake. Amma kuwa na ji kunya ,mutum da jinin shi ace ya kasa gane shi". Iya Murmushi kawai Hajiya ta yi. Barr yace " To ai ita d'in ne ma naga bata fiye magana ba". Hajiya tace "Ai haka ta ke Hajiya k'arama ba ta wani fiye magana ba musamman ma idan ba ta San mutum ba. Da dai marigayiya Haseena ce idan ka zo sai ka gaji da surutu" Barr yace "Allah sarki. Allah ya gafarta mata yasa ta huta. Hajiya ta amsa da " ameen". Daga haka tace "bari in shiga daga ciki kafin lokacin sallah ya k'arato." Har k'asa Barr ya zuqunna yace "a fito lafiya hajiya". Hajiya ta shige ,shi kuma ya koma ya zauna. Sun dad'e a zaune tsakanin shi da Suxee ba Wanda yace wa kowa komai ,ganin haka yasa ya kauda shirun da d'an d'auko wa Suxee hira. Sama sama dai suka d'an dinga hira anan har yake gaya mata yadda alaqar shi ta ke da Hajiya. Sai a lokacin ne ma suxee ta d'an sakar masa fuska. Ranar anan Barr ya ci abincin dare ,ya ta jiran daddy ya dawo su gaisa amma bai dawo da wuri ba ,ganin dare na yi yasa ya yi musu sallama ya tafi.
Wani daren asabar Haajar na zaune tare da daddy suna hira. Ya na bata labarin irin ci gaban da ya samu a harkar kasuwancin shi cikin d'an k'ank'anin lokaci, Wanda duk ya ta'allaqa samun nasarorin akan Haajar. Haajar ta nuna jin dad'in ta ma matuqa game da yabon da ta samu a wajen daddy tare da yi masa fatar samun nasorin da ya fi wannan.
Wani abunda mai karatu bai sani ba shine. Tun bayan lokacin da wancan al-amarin ya faru ,daddy bai sake kusantar Haajar ba, ba kuma Wani abun bane daban ,tsabar nauyin Haajar d'in yake ji ,ya ke kuma ganin idan ya nema ta kamar bai kyauta ba sakamakon abunda ya faru tsakani shi da ita a baya. Dukda kuwa yaji cewar a wancan lokacin duk Haajar d'in na a matsayin matar shi, amma ya kasa yafe wa kan shi. Tun Haajar na tunanin ko akwai wata matsalar ce a k'asa Wanda bata San da shi ba da yasa daddy ya k'i Neman ta a shimfid'a, har ta gano ba komai kawai nauyin ta daddy ke ji ba kuma Dan baya sha'awar ta ba ,kawai yana kai zuciyar shi nisa ne. Ganin haka yasa Haajar ta shirya tsaf Dan k'arawa kan ta daraja da k'ima a idon mijin ta. Washe gari da daddare bayan ta yi sallama da su Hajiya ta dawo sashen ta. Ta sake yin wani sabon girkin da ta San mijin ta ya fi son shi sama da kowani abinci. Bayan ta gama ta ci ado matakin k'arshe ,sannan ta zauna tana jiran dawowar farin cikin ta.
Sai wuraren goma na dare daddy ya shigo gida. Sashen hajiya ya fara zuwa ya taradda sun yi bacci, bai yi k'ok'arin ta shin su ba. Ya wuce zuwa sashen Haajar. Tun farkon shigar shi ya ga wasu sababbin sauyi. Da wani irin k'amshi mai matuqar sanyaya ruhi ya fara cin karo. Haajar ce ta fito cikin wasu k'ananan kaya Riga da wando masu matuqar d'aukar hankalin mai kallon ta. Wannan ya k'ara tabbatar wa daddy da cewa yau d'in na musamman ne. Wani salo na mai tafiyar da nutsuwa ta dinga yi masa. Ruwan wanka ta fara had'a nasa ,ta taimaka masa ya cire kayan sa. Daddy shi dai sai bin ta da ido ya ke yi yana kallon ikon Allah, Haajar d'in ce duk ta canza masa yau d'in kamar ba ita ba.
Wani abun mamakin ma bai wuce ta yaga alamar cewa tare take son suyi wankan ba. Dan bai tab'a ganin tsaraicin ta ba. Kullo band'akin tare da zare kayan da ke jikin ta d'aya bayan d'aya. Zaro ido daddy ya shiga yi yana mazurai kamar yau ne rana ta farko daya fara ganin tsaraicin mace. Kusan sumar tsaye ya yi lokacin da ya yi tozali da kyaky-kyawar surar jikin Haajar mai matuqar rikitarwa.
Salo ta dinga yi masa ko a wajen wankan ,da k'yar daddy ya iya k'arfin halin had'i yawun sa. Bayan sun fito ba shi wuri ta yi ya kimtsa ita kuma ta koma d'ayan d'akin ta shiryo cikin wasu kayan bacci masu masifar kyau ,Wanda kusan da su da babu ba suda banbanci. Abinci ta fara gaba to wa daddy. Da kanta ta dinga ba shi a baki ,daddy kuwa dak'yar abincin ke wuce masa a mak'oshi Dan kusan ma ko gard'in abincin baya ji saboda abun da yake gaban sa ya kauda duk wani d'and'ano dake bakin sa. Bai wani ci sosai ba sakamakon ya k'agu. Haajar kuwa da ta ga yana bakin hanya ,sai ruwan shagwab'a take zuba masa tana wani narke masa a jiki. Wannan yanayi da daddy ke ciki a yau sai yake jin kamar kar ya wuce. Iya soyayya, salo da k'arshen kissa da kisisi na irin na mu na manta wajen Jan hankalin namiji sai da Haajar ta baje shi a wannan Daren.
Daga nan ta ja su sai d'akin baccin su da ta k'awata da nau'in furai launin jajaye, ga wasu k'yandura a aka kunna suna fidda d'oruwar wuta. K'awa irin na masoya. Tsarin ya yi matuqar burge Daddy Wanda har sai da ya furta "ya yi kyau".
A wannan Daren saida Haajar ta tabbatar wa da daddy ita d'in ta musamman ce kamar yadda komai na ta yake na daban ko a cikin mata. Dan kusan ma sai ya ji ya fi jin ta gam fiye da wancan lokacin da ya yi mata shigar gangancin. Duk wani gudunmawa Haajar ta ba shi a wannan Daren Dan su mori rayuwar su yadda ya kamata. Ba kad'an ba daddy ya murji Haajar son ran shi ba gajiya balle k'orafi. Kusan wannan dare na daga cikin dare mafi soyuwa ga wa'yannan masoya.
Albarka sai kalan Wanda daddy ya manta ne bai saka wa Haajar ba a wannan Daren. Tun dare suke Abu d'aya, har wuraren asuba ,sannan su ka hak'ura ba Dan sun gaji da shak'ar d'umin junan su ba.
Washe gari tun bayan da su daddy su ka yi sallar asuba ,suka koma bacci ,ba su suka farka ba sai sha biyu na rana. Hajiya da suxee tun suna jiran fitowar su har suka cire rai. Su kan su masoyan irin baccin da su kayi ya d'aure musu kai.
Sai yanzu daddy ya k'ara tabbatar da abunda Hajj Jamil yake gaya masa na cewa matuqar yana tare da abunda ya ke so ,ya kuma samu yadda yake so, to ba shakka zai iya mantawa da komai".
Wanka suka yi suka shirya cikin wata had'ad'd'iyar shadda mai tsada da taji aikin wuta. A tare suka nufa shashen Hajiya. Haajar sai sunne kai k'asa take yi ,Dan gani take Hajiya zata gano abunda ya faru tsakanin su. Ba ta san tun lokacin da hajiya ta ga yanayin shigar su ba ,da kuma irin farin cikin da Daddy ke ciki a yau ,ya tabbatar mata da komai. Iya murmushin ta kawai ta yi irin na su na manya tare da saka musu albarka.
MUJE ZUWAπ
TAKU HAR KULLUM
SIDIYA....βοΈ
[8/22, 10:23 AM] SIDIYA...βοΈ: π π *GIDAN MISBAHU*π π
π π π π π π
π π π π
π π
π
*_π (base on true life story)_*π
*_π INTELLIGENT WRITERS ASSOπ_*
(On ward together)
*MALLAKAR:*
*SADIYA SIDI SAID (SIDIYA)βοΈ*
_BABI NA ARBA'IN DA HUD'U_
*____________________________*
Tun daga wannan lokacin Barr babu ranar da baya zuwa gidan daddy ba Dan kowa ba sai saboda Suxee. Dan shi har ga Allah yanayin nutsuwar ta da hankalin ta yasa ta yi matuqar kwanta masa a rai. Ya na ta Neman hanyar da ze yi ya sanar da Hajiya Dan yasan ina ce zata tsaya masa har abun nan ya yiwu. Bai San Hajiya mace bace mai matuqar karantar yanayin mutum ,ko ince ya Sani mantawa ya yi. Tun yana b'oye-b'oyen har ya fito garan da garan ya gayawa Suxee abunda ke ran shi. Bata nuna masa komai ba Dan haka ya lashi takobin Neman soyayyar ta ta duk yadda zai iya. A b'angare d'aya kuma ga Hajj Jamil da tun ba yau ba yake masifar qaunar Suxee, Wanda kusan za mu iya cewa tun tana k'arama yake d'awainiya da son ta ,har kawo yanzu da ta girma, Wanda daddy ba yada masaniyar hakan. In da matsalar ta ke kuma ko so d'aya bai tab'a furtawa suxeen cewa yana qaunar ta ba. Ba Dan komai ba Sai Dan Hajj Jamil mutum ne mai matuqar zurfin ciki da kawaici. Yana ganin kamar bai kyauta ba idan har ya ce zai auri 'yar daddy. Badan komai ba saidan daddy babban aminin shi ne na har abada Wanda ba ya da tamkar shi ,sannan kuma yana tare da daddy ne tun kafin ya auri Mahaifiyar Suxee wato kubra. Da wannan yake ganin ya zama wajibi ya lallashi zuciyar shi Dan ba ya so ya aikata wannan abun kunyar. Idan da kara ai Suxee 'yar shi ce, ko daddy baya raye shi zai zama uban ta, a gefe d'aya kuma idan ya tuna halaccin abun a addinance sai ya ji baze iya hak'ura ba ko nan da can. Ga shi a yanzu qaunar ta dad'a mamaye ko wani lungu da saqo na kafatanin jikin shi ta ke dad'a yi. Wasu lokuttan idan ya zauna sai ya ga zuciyar shi bata yi masa adalci ba ,ta rasa wacce za ta so sai 'yar shi , 'yar babban aminin shi. Duk da cewa ko a shekaru daddy ya girme masa nisa ba kusa ba. Sai dai ita soyayya ba ruwan ta da wannan. Halittar Allah ce da ke ratsa duk Wanda ta so a kuma lokacin da ta ga dama. Takan iya wa mutum mummunan kamu musamman idan Wanda ta yi wa wannan illar ya yi mata gurguwar fahimta. Son da hajj Jamil ke yiwa Suxee har ya kai ya kawo idan ya ganta baya iya samun sukuni ,zuciyar shi ta dinga bugawa kenan ,ji yake kamar ya ta shi yaje ya rungumo ta ,amma ba dama. Baya tab'a samun sukuni har sai ya d'aga daga inda take. Wannan dalilin ne ma yasa shi ya rage zuwa gidan daddy Dan dole ba Dan ya so ba, ga Hajiya ko da yaushe tambayar sa take akan mai yasa ya rage zuwa kamar da ,a tunanin ta gidan daddy ai kamar na shi ne ,ga shi shi Matar shi ba mazauniya bace, wannan yasa Hajiya ke yawan yi masa fad'a akan ya dena zama shi kad'ai saboda kad'aici ,ka da wani ciwon yaje ya kama shi.
Amma kuma duk randa abun ya tsikaro shi na son ganin Suxee ya zame masa wajibi sai ya je gidan ,ko da baze mata magana ba. Yau ma hakanne ya faru. Bayan ya dawo daga harkokin sa na kasuwanci kai tsaye gidan daddy ya nufa, tun bayan la'asar har kusan bayan isha yana tare da Hajiya su na ta hira. Rashin wurgawar Suxee ya sa duk ya shiga damuwa, sai waige-waige ya ke yaga ko zai gan ta ,amma shiru babu alamar ta. Har Hajiya ta d'ago shi tace masa ko wani abun yake nema? Amma sai yace a'ah. Yayin da ita kuma Suxee ta ke sashen Haajar tana bata labarin Barr Kabir da yadda yake matuqar qaunar ta. Wato wani abunda Haajar ta fahimta game da Suxee shine; Suxee na matuqar son mai nuna mata kulawa. Wannan ne yasa Barr bai sha wahala sosai wurin Neman soyayyar ta ba. Duk da cewar ita din tana da miskilanci amma hakan ba ya hana ta nuna jin d'ad'in ta a fili ga duk Wanda ya b'ata lokacin shi akan ta musamman ta fannin soyayya. Bayan ta gama zayyanawa Haajar komai ,Haajar ta fahimci cewa lallai fa Suxee ta fa d'a tarkon so kuma mai tsanani. Tace mata "Ni shawarar da zan baki shine ,ki yi a hankali Dan na fahimci ke baquwa ce ta wannan fannin. Ya na da kyau ki iya bambamce tsakanin SO da kuma QAUNA ,wannan ne zai taimaka miki wajen gane waya kamata ki so da