Showing 39001 words to 42000 words out of 98395 words

Chapter 14 - MI WASMITI Book Complet Document by Garkuwa .txt

da Yusuf do ya damqe
Shi kam Yusuf kallon shi kawai yakeyi
So ya yake yaji shi shima a mace ko zaiji wani a bu a ranshi ji yake dama haukacewa yayi
A hankali zuciyarsa ta fara tuno mai abinda kalaman baba Umar ke nufi a take Kuma Sai jikin shi ya rinqa karkarwa
A haka suka samu suka dauke gawar
Cikin kuka Adam yabi bayansu
Shi kam Yusuf a wurin ya zauna kamar dasashi akayi


Acan Kuma akayiwa gawar duk abin da ya kamata kafin ma gari ya waye anyi komai an gama


Washe gari da safe wannan lbrin ya iski Anuty Sadiya
Duk da mijinta ta ya ji dashi akayi komai Amman ya rasa ta INA zai fara kawo mata wannan zance
Sai da safen yace ta shirya suje gida
Su gaidasu
A mota ta kalli mijinta Cikin sanyi tace Abban Yumin.
Na,am ya amsa mata Cikin sanyi
Sai kuma tayi shiru gamida dafe qirjinta
Hannushi yasa ya kamo nata yace
Kin kirani kin Kuma yi shiru
Kai ta daqo ta kalleshi Cikin rawar murya da alamar kuka zatayi
Tace Abban Yumin
Zuciyata Na tsinkewa tsoro nakeji ban San meyasa ba tun jiya nakejin faduwar gaba
A hankali ya jawota ya manna ta a jikin shi cikin fargaba yace ki rinqa addu,a ki Kuma kasance mai yarda da gaddara
Dai dai nan yayi parking a farfajiyar gidan nasu
A hankali ta zame jikinta ta fito
Cikin tsoro da firgita ta bude idanta da kyau ganin gaba daya harabar gidan a cike yake da mutane a take qafarta ta fara rawa Cikin tsoro ta juyo gareshi tana Abban Yumin me ya faru me kake boye min
Hannushi ta riqe tana jijji gawa da qarfi tana ka fada min INA Abba ban ganshi anan ba
Allah sarki
ita Sam bata kai tunanin ta kan qaninta ta rasa ba
Rabi,u dake gefe ne yayi saurin isowa gareta durqushe wa yayi a gaban ta Cikin kuka yace Anuty Sadiya ya Ahmad ya tafi ya Ahmad ya tafi ya barmu
Ido ta zaro Cikin tsoro Sai kuma tayi Cikin gida kai tsaye dakin Nenne ta nufa
Can ta hango Ummi da sauri taje gaban ta ta fada Cikin kuka tace Ummi
Me nakeji Ummi meya samu Dan uwana wayyo Allah wayyo Dan uwana wayyo Nenne Na wayyo cikina Ummi shike nan Na rasa Dan uwa
Adam ne ya kamo hannuta Cikin kuka yace Anuty Sadiya mun rasa Ahmad Anuty Sadiya Ahmad ya tafi ya barmu
Gaba daya suka ruda parlon kakace ta tashi itama Cikin kuka ta kamo hannu Sadiya
Da Adam tayi Cikin daki dasu

Suna shiga Sadiya ta hango Yusuf Wanda tun jiyan bai tashi a wurin ba sai sallan asuba da ya tashi yayi da taimakon hydar
Tana hoggo shi ga Nenne a gefenshi
Tana riqe da hannushi tana fadin
Haba Yusuf kayi mgn mana Yusuf katashi kaje qun baqin da sukazo yi maka gaisuwa
Haba Yusuf fushi kakeyi da yin ubangiji ne
Shin ase bazaka rungumi qaddara ba
Yusufa mufa musul Maine
Shi kam Yusuf ido ya zubawa Anuty Sadiya
Ita Kuma gabanshi tazo ta durqusa ta kamo hannushi ta kifa kanta kan cinyarsa ta saki wani kuka mai ban tausayi
Tana kuka tana fadin Yusuf ya zamuyi Allah shi yabamu Ahmad Kuma shi ya dauke shi
Dama kullum haka Ahmad ke gayamin ai Wanda ya Baku ni yaga fiku sona Anuty Sadiya ki dena damuwa da halin da nake ciki ase Ahmad duk maganganu da yakejin wasiyace


A hankali ya daura nashi kan kan kafadarta
Yasa hannushi ya riqe nata Sai ya kuma kura mata ido
Yana jujjuya kai
A hankali tace Yusuf kayi min mgn ma ko zanji sanyi a raina dama kullum Ahmad cemin yake ko ya mutum kar Na damu gaka ga Adam da Abubakar duk abin da nake so zaku min
Kai ta juya cikin kuka tace Ummi INA Abba Ummi a wane hali Abba yake ?


Cikin duseshewar murya tace Sadiya
Abba tun a Daren jiya ya tafi Abuja shida Hydar Kuma yau dinnan zasu wuce India
A Dan tsorace tace Ummi Abba ne ba lfy ko ehh Sadiya abbanku baya Cikin hayya cin sa
Hawan jinisa ne ya tashi
Sai hawayen ke bin fuskar ta


Adam ne ya kalleta Cikin sanyi yace anty sadiya ko zakizo kije dakin Ummi ki zauna da su Maryam da Aysha da Amira suna can Sai kuka sukayi ba mai lallashin wani
Cikin sanyin jiki ta nufi dakin Ummin


Ayyah Maryam da aysha suna zaune tun jiya da Aysha ta farfado suke ta kuka abin tausayi Aysha abin ya hadu mata jiya tasan ba ummi
bace mahaifiyar ta kuma a jiya ta rasa ya Ahmad dinta Kuma a jiya tasan mahaifiyata ta rasu a lkcin aihuwarta
Ganin Sadiya yasa ta fada jikinta tai ta wani sabon kuka
Ta ruggumi meta nan sukayi ta kukansu
Da dyar dai suka samu suka tsagaita
Da kukan


Rayuwar gidan ya canja musu gidan ya koma tamkar ba kowa Sai masu zuwa gaisu da zaran bakin suntafi kuma to shike nan gidan yayi shiru
Rayuwar Yusuf ta sauya ta koma abin tausayi baya mgn da kowa komai za acemai da kai ko ido yake bada amasa duk masifar Na ta Yusuf da bala,I da mishkilanci yanxu babu su
Ya koma abin tausayi Baya iya mgn 5 lafiyeyyu
Komai ya rigada ya gama sauyawa
Aysha kam ko yaushe Sai ta shiga toilet tayi ta kukanta Sai fuska ta kumbura Maryam Kuma yanxu bata iya kukan ya rigada zuciyata ta bushe






Yau ne akayi sadakan 7 gaba daya baqi sun waste su Bappa Yaya ne kadai suka rege basu tafi ba


Yau kwana 10 da rasuwar Kuma yaune su Bappa Yaya ya zasu koma
Shiyasa da safe ya Tara zuriyar tasa
Bayan ya gama musu nasiha
Ya kalli Yusuf da Adam yace
Dudabe
Na,am ya amsa cikin
sanyi
Ido ya zuba mai cikin tausayawa yace
Yanxu me kakeyi a qasarnan ?
Kai ya sunkuyar gami da cije lips enshi yace me zanyi Kuma a qasarnan bani da abin da zanyi
Toh ka shirya kaida matarka Ku koma kaje kaci gaba da kara tunka
Aysha dake takure a jikin Nenne Cikin kuka tace Dan Allah Bappa Yaya Ku barni ni bana son komawa can
To me zaki zauna kiyi a nandin ?


Ni dai banson komawa canne
Ta bashi amsa Cikin kuka
Shi dai Yusuf shiru yayi Dan yanxu qoqolwarsa bata fiye gane me ake yiba


Haka kuwa akayi randa akayi kwana 15 da rasuwar a ranar baba bello ya kamma lawa su Yusuf shirin tafiyar su
A Kuma ranar ✈ jirginsu zai tashi


A hankali suke fitowa daga parlon suna zuwa harabar gidan
Bayan su Rabi,u sun gama Sa musu kayansu a but


Cikin sanyi Yusuf yaje ya durqusa gaban baba bello murya Na rawa yace baba zan tafi
Kanshi ya dafe Cikin qarfafa mai guiwa yace Allah ya kaiku lfy Yusuf
amin yace
Gami da miqewa yaje gaban Nenne itama ta mai addu,a
A hankali ya qarisa gaban umminshi
Ya durqusa guiwa bibbiyu yace Ummi zan tafi Amman bazan sake zuwa qasarnan da wuriba


Cikin
ajiyar hrt
Ta kamo shi ta tsaida shi
A hankali taja hannu Aysha ta samai Cikin nasa tace to ga amanar da Dan uwanka ya baka
Yana Cikin qabarinshi
mu kuwa mune masu ganin irin yadda zaka riqe amanar da ya baka a dai dai lkcin da ransa yake fita a jikin shi


Hannu yasa ya kamo Na Ayshan ya juya Cikin Rashin sanin me zaiyi
Ya jata
Suka qarisa gaban Adam ya ruggume juna sukayi musabaha
Ya kalleshi Cikin sanyi yace biyaye Allah ta sadamu kan alkhairi
Amin yace dai 2 lkcin da suka shiga mota


Usmanne da Rabi,u suka kaisu airport


3:37 pm jirginsu ya tashi




By garkuwan Fulani
[4/9, 2:25 PM] β€ͺ+234 909 785 3276‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡


NAYI NADAMA
πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»
MI,WASMITI page 7⃣4⃣to7⃣5⃣ Na Aysha s Garkuwa
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡


Allah sarki rayuwa mai juyawa
A
cikin jirgi
Yusuf ya zauna kan kuje rarsa ta number 24 yayinda Aysha Kuma nata number 23 ne
Nata kujerar itace kusa da window jirgin
A hankali Yusuf yake takawa har ya isa wurin zaman nasu
Jiki a sanyaye ya zauna
Gamida yin taqumi da hannushi daya ya Sada kanshi qasa
Bai tuno komai Sai ran da suka dawo India a lokcin da suka kamma la kara tunsu
A wannan jirgin suka dawo a wadannan kujerun suka zauna inda ya ke zaune anan ya zauna a wancan lkcin Na gefenshi Kuma biyayenshi ne
A hankali ya zubawa sit din ido
Zuciyarsa Na suya
Sai cije lebenshi yakeyi sabida kuka yake son yi Amman kuma ya kasa samun kukan


Yana Cikin wannan halin
Yaji abi Na diga kan wuyanshi
Hannushi yasa ya shafo wurin kamar ruwa yaji
Kai ya dago ya zubawa Aysha dake tsaye a gefenshi dafe da kan kuje ranshi
Hawaye wannan Na koran wancan
Kallonta yayi Cikin shawa,a
A ranshi yake cewa
Kinji dadi da kika samu kina kuka kina zubda qollah😭 nasan koba komai zakiji sauqi a ranki


Sanarwan da akeyi Na koma ya koma gun zamansa jirgi zai tashi shine ya dawo dashi daga tunanin da yakeyi
Ido ya sake zuba mata
A hankali ya daqo
Hannushi ya kamo nata
Ya jawota
Gami da Dan Jan qafafunshi
Dan ta samu gun wucewa
Kan sit din gefenshi ya yaja hannuta ya zaunar da ita


Ita kam Aysha ido cike da qollah😭 ta bi fuskar shi da kallo
Lkci guda Kuma ta tuno
Lkcin da zasu tafi wancan karon
Da ta tsaya a kanshi haka tana kuka
Cikin masifa ya rinqa surface mata bala,I harda yarfa mata mari yana mayya kawai kin wani tasa mutane a gaba kina kuka toh kanki zakici ai tunda kikayi kuskuren yadda kika biyoni toh wlh baqin jaki Sai ya fiki jin dadi
Cikin tsawa ya jawota ya tura a wancan lkcin


Tana Cikin tunanin taji jishi
Cikin wani irin voice yace
Kija bel dinnan ki saka
Kai ta sunkuyar Cikin zubar qollah😭
A hankali
Jirgin ya rinqa
Qugi da Dan diri
Cikin tafiya a hankali ya rinqa Dan tashi sama
A hankali Yusuf ya maida kanshi jikin sit din ya lumshe idansa jikin jin wani irin azaba a karo Na forko da yaji yana qaunar barin qasarsa ta aihuwa
A karo Na forko da yaji ya qagu ya daina shaqar iskar qasar
A ranshi yakeji to me y rege masa a qasar nan
Babu ya fada a bayyane
Gami da bude idanshi da jin zafi a ransa
Ita kam Aysha ta window take yiwa qasar ta wani irin kallo da jirgin ya gama tashi sama
Ta kifa kanta jikin window ta saki kuka mai ban tausayi


Ido ya zuba mata gami da jinjina kai
A ranshi Kuma cewa yayi kuka ma Rahama ne bazan hanaki ba


A haka Cikin kukan bacci ya debeta
Yayinda shi Kuma Sai ajiyar hrt da yake tayi
9:00 Am agogon Nigeria
Dai2 da 11:00Am saudiya


Jirginsu ✈yayi landing Cikin birnin Madina
A hankali fasinjoji suka rinqa fita
Ido Yusuf ya rufe a sannu Kuma ya budesu
Kan fuskar amanar Ahmad dinshi
Cikin sanyin murya yace
Ke
Ke tashi mun iso
Kamar a mafarki taji muryar shi


Sai kuma taji tsoro Dan tuna wancan Zuwan nasu inda ya rinqa zuba mata mari Cikin fushi yace ko ki taso ko Na tafi Na barki
Bira alaqaqai kawai
Banza mayya..a wancan lkcin

A hankali ya katse mata tunani da takeyi
Muryar shi ta kumaji
Cikin Dan kauri yace
Ke INA mgn kinyi shiru
A hankali ta miqe
Tabi bayan shi
Har inda aka ta naji motici Dan ma tafiya wani ma aikaci Na biye dasu riqe da jakarsu
Har zuwa gun motar
Suka shiga suka tafi


A dai dai harabar wani qaton gida mai kama da ma aikata part part sun kusa 7


Abakin qofar su direban ya tsaya dai2 bakin qofar shiga
Suna fita
Yaja motarsa ya tafi
Jakar ta ya zubawa ido Cikin ranshi yasan bazata iya dagawa ba Amman kuma shima ga nashi
Sai kuma ya kalli inda take ta tsaya Sai rawan sanyi take Dan daga dukkan alamu anyi ruwan samane ya dauke Sai walqiya akeyi da iska mai sanyi da take kadawa
Hannu yasa ya dauki jakar tata yasa qafa ya tura mata nasa


Ya juya yayi gaba a hankali tabi bayan shi


A parlo ya ajiye mata nata ya karbi tasa ya juya yabi Cikin Dan koridon da zai Sa dashi da parlon shi
Yana shiga ya fada kan 3 str Cikin
Yanayin shi da yafi kama da maraya
Ido ya lumshe ba tare da yayi bacci ba zafi yakeji sasoi a rayuwarsa
A hankali ya daqo phone dinshi Nenne ya kira
Tana dagawa tace Yusuf kun isako ? ehh yace mata
Gamida cewa ki gaida baba Sai da safe
Toh Allah ya bamu alkhairi tace dashi gamida katse woyar
Shi kuwa a nashi gefen kashe phone din nashi yayi gaba daya


Ita kuwa Aysha da qyer taja jikinta ta tafi bedroom dinta
Kan gado ta fada Cikin kuka a haka a ranan ta kwana kuka
Shi kuwa Yusuf kukan ya nema ya rasa shiya sa ya tashi Cikin rawan jiki yaje yayi alwala yazo ya rinqa nafilfili
Idan yayi sujjada ba abin da yakeyi Sai nemawa Dan uwan shi gafara


Washe gari da safe
Abokan Yusuf laraba suka rinqa zuwa mai taziya da dama daga cikinsa sun San Ahmad
Wasu sunsu Kuma insun zo kuka sukayi kamar zasu suma


Akwai wasu abo kansu su 2 Sulaiman da Bashir Wanda tare sukayi karatu a inda
Kuma suma yanxu suna Jami,atul madinan ne suna kara ilimi
Bashir Dan Katsina ne Kuma tare da matarsa sukazo
Mai suna Zakiya
Tunda sukazo
Sulaiman yake kuka kamar mace dan shi ya shaqu da Ahmad sosai kusan halin su iri daya
Bashirne ya rinqa Dan bashi baki yayinda dashi ma yake ta sharar qollah😭
Shi kam Yusuf Sai cije lebe da yakeyi
Cikin daburcewar murya yace Zakiya ki isa gun qaunar Ahmad tana ciki
Ku gaisa
Toh tace mai gami da miqewa
Tayi candin
A hankali tayi SLM Cikin parlon ba kowa
Ido ta Dan bude Cikin zubar hawaye tana kallon parlon a shirya yake tsafta ba datti ko kadan komai Na parlon farine da jaa gashi labulayen suna sasake shiyasa Sai parlon yayi dubu kamar dare
SLM ta kumayi gamida zuwa jikin gini ta kunna wutan tsakiyar parlon
Ba kowa har ta juya zata fita Sai kuma taji sautin kukan a cin bedroom din
Juyawa tayi ta shiga dakin
Kan gado ta hangota tayi rufa da ciki Sai kuka takeyi tana
Ayyah ya Ahmad yanxu mun rabu kenan bazan Kuma ganin ka ba
Zuwa tayi ta zauna gefen ta Cikin sanyin murya
Da qoqarin danne nata kukan tace
Kiyi haquri Aysha ki daina bin Dan uwanka da kuka kiyi ta masa addu ,a shi yafi buqata a gareku ba hawayen ki ba
Dagowa tayi tana kallonta Cikin rashin Sani
Fahimtar hakan da Zakiya tayi shiyasa ta kamo hannuta
Tace
Ni suna Zakiya ni matar abokin Yusuf ne sunan mijinta Bashir
Muma muna qasar nan Kuma tare muke da mijina yana can gun Yusuf dinne .


Allah sarki Aysha rashin Dan uwa shiyasa a take taji zaki tamkar Maryam da Amira
Cikin hawayen tace kinsan ya Ahmad dinako ?
Eh Na sanshi Aysha
!
Ayyah to shinefa ya rasu.
ehh Na Sani Aysha
Kibar kukan Dan Allah
Wlh nima zaki Sani kuka
Kai ta jinji na gami da share hawayen ta tace
Ni ma banson yi mishi kukan kasawa nake in banyi kukan ba ji nake kamar zan mutu
Cikin tausa yawa tace ki rinqa addu,a kinji ko Aysha
Toh tace Cikin goge qollah😭
Haka dai Zakiya tayi ta lallashinta
Har ta samu ta jawota suka shiga kitchen
Suka danti girki mai Dan sauki
Dan dama ba abin da babu a cikin kitchen din
Ita ta dauka ta kaiwa su Yusuf
T juya zata tafi Bashir yace in kin gama kizo mu tafi
Toh tace Cikin sanyi Dan tanajin tausayin yadda Yusuf da Aysha zasu kasance su kadai


A
Parlon ta zuba abinci ta matso ayshi cin lallashi tace
Ayyah Aysha ki matso kici abinci kinji ko
Kai ta girgiza tace bazan iyaba bakina daci nakeji
Ta Dan sunkuyar d kai tace Aysha bakya son nazo gobe ko ?
Da sauri tace a a wlh inaso
To kici abinci
Ayyah Zakiya nima ina son ci bazan iya bane shi yasa
Miqewa tayi gamida yin Cikin kitchen din furts ta dauko ta kawo mata
tace gashi ki daure kici koda inabinnan da Dan dabino ga Apple
Karba tayi ta danci
Sannan sukayi sallan insha


A parlon Yusuf Kuma shi da sulamai sun kasa cinnkomai shima Bashir sai dan tea ya Dan Sha


Bashir dinne ya miqe gami da kallon Yusuf
Cikin sanyi yace
Yusuf zamu tafi Sai gobe in Allah ya kaimu insha Allah zamuzo
Amman dan Allah Yusuf ka rinqa Sa dauriya a ranka Yusuf ka rege tunani Dan Allah kar ya maka illa
Kasan kana da matsalan zuciya
Kai ya sunkuyar Cikin ceje lips dinshi da gaba daya yanxu sun kubbura sunyi jazur sabida rashin kukan da bai samu yayinba
Sai yayi ta cizon lips din nashi
Haka dai Bashir ya rinqa bashi baki
Sannan suka wuce parlon Aysha


Sulaiman kam yana ganin ta Sai hawaye Dan shi yasan irin son da Ahmad yake mata
Kuma itama tasan Sulaimanu
Durqusawa tayi a gabanshi tana zubda qollah😭 Cikin rawan murya yace
Sannu Aysha sannu da rashi Allah ya jiqanshi da Rahama


Amin ya rabbi ta fada Cikin kuka shima Bashir ya gaida ta sannan suka fita suka tafi


Shi kam Yusuf parlon shi ya koma Cikin kuncin zuciya
Yadda ya kwana jiya hakama ya kwana yau
Washe gari da safe Bashir da Sulaiman sukazo Zakiya kuwa sai da ta tsaya tayi musu girki sannan ta taho
Daga ranan haka sukayi tayi Sai randa suka cika kwana 7 da dawowa sannan suka daina zuwa
Su wuni Sai dai duk da haka kullum zakiya ke musu girki ta bawa Bashir ya kawo musu duk da baci sukayi ba yadda Bashir ke kawo shi haka yake zuwa ya
dau keshi


Sannu a hankali yau watansu daya da dawowa
Rayuwa ta juya ta canxa
Yusuf Dan qolisan nan gaba daya ya zama abin tausayi banda wonka ba abinda yakeyi ko mai bai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login