Showing 39001 words to 42000 words out of 114314 words

Chapter 14 - HAJAR Book Complete document by Feenerh_feeche .txt

09 Dec 2024

5292

ina kike?", tace "Maama ce ta aiken", ya kalli cikin idonta yace "nace daga ina kike?", ta murguɗa baki tace "to nace maka Maama ce ta aikeni gidan Balaraba..", gwaɓe mata bakin yayi har saida yayi jini yace "tin muna shaida juna ki gayamin daga gidan uban wa kike kafin na sumar dake", daddagewa tayi ta buɗe murya ta fara kiran Maama, afujajan Maama ta fito daga ɗakinta jin muryar shalelen ƴarta, Maama tace "Sa'adatun Maama kin dawo?", Sa'adatu ta ruga gabanta tace "Huzaifa ne", Maama ta kalli Huzaifa snn ta kalli Sa'adatu tace "me yayi miki?", Sa'adatu ta buga ƙafa a ƙasa tace "dukana yayi a baki, kuma Allah ya isana", Maama tace "duka kuma?, Akul Huzaifa karka sake taɓata", yace "ke ni kikewa Allah ya isa?, wllh saina kifar dake", Sa'adatu ta rakuɓe bayan Maama tace "Eh, mugu kawai". Maama tace "A'a Sa'adatun Maama yayanki ne fa banda rashin kunya", Sa'adatu ta cokalo baki snn ta shige ɗaki. Huzaifa ya sauke numfashi a hankali zuciyarsa na zafii. Maama tace "karka ɗauki halin Nasiru, ku ringa ririta ƴan ƙannenku, amma indai kuka haɗu dasu sai duka, haba don Allah..." ta juya ta koma ɗakinta. Washe gari tin ƙarfe takwas Huzaifa ya shirya komawa schl. ɗakin Baba ya shiga da ƴar jakarsa goye a baya yayi masa sallama, Baba yace "toh Allah ya kiyaye hanya, Allah yayi maka albarka", Huzaifa yace "Ameen Baba", Huzaifa ya fito daga ɗakin ya doshi na mahaifiyarsa, yana ƙoƙarin shiga ɗakin sai gata nan ta fito, ya durƙusa ya gaisheta yace "Maama ni zan koma", tace "Au kaima tafiya za kayi, jiya fa Naseer ya tafi", yace "lecture ta kankama ne", tace "toh, wai saura shekara nawa ne ka gama wnn jarababbiyar makarantar?", yace "saura shekara ɗaya insha Allah", tace "toh Allah ya bada Sa'a", yace "Ameen". Umma ta fito ɗakinta hannunta riƙe da tsintsiya da abin kwashe shara da ta share ɗaki, Huzaifa ya russunar da kai yace "Umma zan wuce", Umma tayi murmushi tace "Allah ya kiyaye hanya", yace "Ameen". Maama ta ƙunduma masa wani zagi tace "dalla malam fita". Huzaifa ya gyara zaman jakar bayansa snn ya fita. da yamma Umma ta fito ɗakinta tana zubawa wata yarinya da tazo siyan kulele, ta gama zuba kulelen a leda ta bawa yarinyar ta shiga ɗaki ɗakko mata canji, tana fitowa ta bawa yarinyar canji saiga dan Munkaila makwabcinsu nan ya shigo yace wai ana sallama a waje, Nabilah da take zaune tsakar gida tayi caraf tace "inji wa?", yaron yace "bari na tambayo" ya fita da gudu, ba jimawa sai gashi ya dawo yace "wai Nura ne". Nabilah tace "kace masa me za a basa", yaron ya juya kenan zai fita Mu'azzam ya fito daga ɗakinsu yace "tafi wasanka kaji", da sauri yaron ya fita Mu'azzam kuma yayi hanyar soro, Umma dai ta koma ɗaki. tare da Nura Mu'azzam ya dawo gidan, ɗakin Baba suka nufa. Nabilah ta taɓe baki tana kallon Nura sama da ƙasa. a hankali Nura ya cire takalmansa ya shiga ɗakin Baba da Mu'azzam ya yaye masa labule. ya durƙusa cike da ladabi kansa a ƙasa yace "Baba barka da yamma", Baba yace "barka dai samari", Nura yace "ya kufan jiki?", Baba yace "Alhmdllh", Nura yace "Allah ya ƙara afuwa", Baba yace "Ameen", Nura bai jima ba ya yiwa Baba sallama. wasu manyan ledoji da ya shigo dasu ya ajiye snn ya fita. tare da Mu'azzam suka fito. a soro suka tsaya Nura yace "Mu'azzam ka ƙi juyowa hadda ko?", Mu'azzam ya shafa kansa yace "A'a ya sayyadi haddar nan fa bazata shiga ba", Nura yayi murmushi yace "Allah ya ƙarawa Baba lfy", Mu'azzam yace "Ameen Ameen", Nura yace "toh sai anjima", Mu'azzam yace "A sauka lfy ya sayyadi". Nura ya wuce Mu'azzam kuma ya dawo gida. Maama da take rakuɓe jikin labulen ɗaki ta fito ta kalli Nabilah tace "wane wnn da naga ya shigo da manyan ledoji?", Nabilah tace "matsolon Hajara ne", Maama tace "ban gane ba?, wnn shine malamin naku?", Nabilah tace "malaminsu daii", Maama tace "Amma ku ka ce min faƙiri ne?, ji fa manyan ledojin da ya shigo dasu snn kuma ji suturar jikinsa", Nabilah tace "wllh faƙiri ne wani kuturun shagon chajin waya ne dashi fa, tsabar ƙanƙantar shagon mutum ɗaya yake ci, gashi kuma na katako, katakon ma duk ya ruɓe gara ta cinyesa tasss, gidansu ma ba kanta wllh, Babarsa ma ɗan wake take siyarwa", Maama ta sauke ajiyar zuciya har cikin ranta taji daɗi tace "Eh lallai uwarsa me siyar da ɗan wake ga uwar wacca zai aura me siyar da alalar gwangwani abincin yan wahala". Nabilah ta sheƙe da dariya tace "kai Maama", Maama ta gyaɗa kai tace "Allah kuwa". Sa'adatu ce ta fito tana latsa wayarta tace "Maama wai baki san Opay ba?", Maama tace "meye kuma Opay?", Sa'adatu tace "kayan haya mana, wnn kayan fa da kika ga ya saka ba nasa bane na aro ne, zuwa yayi aka ara masa don yazo yayi fafa, tin daga kan agogo takalmi hula da tsadaddiyar shaddar jikinsa wllh duk na aro ne", Maama ta sake sauke ajiyar zuciyar daɗi tace "nifa ince, ai daga gani ma kasan kayan na aro ne, ke har turaren ma da ya tsayamin a maƙogaro na aro ne koh?", Sa'adatu tace "kwarai ma kuwa". Maama tayi hanyar ɗakin Baba tace "bari naga wace tsiyar aka lafto a manyan ledojin", Sa'adatu tace "yawwa gano mana tsiyar". ba ko sallama Maama ta afka ɗakin, kallo ɗaya Baba yayi mata ya kauda kai. tamkar shege a rabon gado haka ta ringa kwalala ido har ta hango ledojin a gefe guda, a wulaƙance ta waftosu ta bankaɗa ta fara duba abinda yake ciki, saida numfashinta ya ɗauke ganin uban kayan, leda ɗaya fruits ne aciki harda Apple da pear, ɗayar ledar kuma kayan shayi. Baba baice mata komai ba ta gama bincika kayan snn ta miƙe ta fita zuciyarta na tafarfasa. Nabilah tace "Maama wace tsiyar ce aciki?", Maama tayi mata wani mugun kallo ta shige ɗakinta.


★A yammacin wannan rana Nurain ya fito daga room ɗinsa ya sakko down stairs zuwa part ɗin Mami, wata jumfa ya sanya coffee mai shegen kyau sai zuba ƙamshi yake, murɗa door handle yayi snn yayi sallama ya shiga, Mami na zaune tana shan red watermelon ita da Noor, Nurain yace "Mami zan je wajen Hajiya", Mami tace "Ohk, ka gaidamin ita da sauran mutan gidan", yace "tomm", Noor tace "yaya ka gaida Iron Lady", yace "Ohk". ya fita palour. katafaren compound ɗin gidansu ya fita, ya doshi parking space ya shiga motarsa, few minutes ya gama warming ya fita daga gidan bayan mai gadi ya buɗe masa gate yana ɗaga masa hannu. Slowly yake driving as usual yana sauraron qira'ar Sheikh Abdul Baseet. A ride of 15minutes ya isa gidan uncle ɗinsa Salisu, a bakin gate ya danna horn, parking motarsa yayi a harabar gidan snn ya nufi main building ɗin kansa tsaye. hannu ya kai ya danna bell ɗin door, babu jimawa mai aikin gidan ta buɗe masa, har ƙasa ta tsugunna ta gaishe sa, ya amsa ba tare da ya dubeta ba. da sauri ta shiga wata ƙofa dake palourn don sanar da ƴan gida. palourn ba kowa sai sanyin Ac da ƙamshin freshner mai daɗi. Nurain ya zauna a kan kujera ya ciro wayarsa a aljihu yana latsawa. few minutes kam saiga wata kyakkyawar mace nan ta fito sanye ta hijab har ƙasa, murmushi ne shimfiɗe a fuskarta tace "Nurain", Nurain ya mayar da wayarsa pocket ya russuna yace "ina yini Ummi", Ummi tace "lfy lou, yasu Maami da Noory?", yace "suna nan lfy", tace "toh madallah", yace "daman zuwa nayi na muku sallama jibi zan tafi India", tace "Au kuma ɗan uwanka na shirin dawowa next week kai kuma zaka tafi, toh Allah ya temaka ya bada abinda akaje nema", yace "Ameen, Hajiya fa?", Ummi tace "tana part ɗinta", yace "Ohk bari na shiga wajenta". ya tashi ya nufi ɗakin Hajiya........✍️


💛 HAJAR 💛
by Feenerh_feeche


{ 21..}
A hankali Nurain yayi knocking ƙofar ɗakin Hajiya, da ga cike akace "waye ne?". Nurain ya haɗe gira snn ya murɗa ya shiga. tinda ya shigo Hajiya da ke zaune bisa lallausar rug ɗin ɗakin take kallonsa har ya zauna a ɗaya daga cikin kujerun ɗakin. Hajiya ta gwalo ido cikin ƙwamemen glasses ɗinta tace "O oho ashe Usuman ne, ai daman tinda naga abu kamar fel waya nasan kaine, angona ba sangameme bane irinka, ni ko yaushe ma zai dawo daga ƙasar can mai ƙanƙanra karfa ya daskare na shiga uku....", Nurain yace "su duk mutanen da suke rayuwa a ƙasar basu daskare ba sai shi", tace "A'a bar wannan zance ai su daman can ƙanƙarar ta gama musu illa sun saba", yace "shima ya saba aii", tace "inafa zai saba, shi da ba jinsin su ba, mutane kamar an bursuna musu garin filawa, angona da yake baƙi ai sam ba gami tsakaninsu, da zan samu jirgin da zai kai masa saƙo ai da na bada maganin sanyi an kai masa..", Nurain yace "toh ki kwantar da hankalin ki next week zai dawo", ta kallesa ta saman glasses ɗinta tace "Au shi Umarun ne zai dawo?, eh ai gara ya dawo kar ya daskare gsky, to kai wa ya gaya maka zai dawo?", Nurain yace "A waya mu kay magana", tace "Oh ni, babu yadda banyi da yarinyar nan Shatu akan ta kira min shi ba amma ta ƙi, yaufa wajen wata guda kenan ina fama da ja'irar yarinyar nan, yanzu kam tinda kazo maza kamo min shi na gansa..", yace "ki bari nan da mako mai zuwa zaki gansa a zahiri yanzu dare ne a can", kafa masa dattijan idanunta tayi ta saman glasses tace "Auu, kaima ja'irin ne kenan?", hade gira yayi yana pointing kansa yace "nine ja'iri Hajiya?", tace "yo ba gashi na gani ba, nace ka kiramin mijina kace min wai dare yayi sbd ka iya lafto ƙarya, ga rana gatsal-gatsal amma kana kiran dare..", gyada kai yayi yace "toh shknn, ni daman zuwa nayi muyi sallama jibi zan bar ƙasar", zaro ido tayi tace "zaka bar ƙasar kamar ya?, kaima garin arnan zaka koma?", yace "Eh", tace "amma dai ban taɓa sanin notin kan Muntari ya kunce ba sai yanzu, shine ya barka ka koma ƙasar arnan, har itama Khadijan notin kanta ya kwance wllh. kamar abin arziƙi ka doshi hanyar zama cikakken mutum sai kuma ka koma baya, da tini kaima da iyalinka dan ma yarinyar ta kasa ka, au koda yake ba jikana ta kasa ba wllh kanta ta kasa, eh shegiya ita taga duhu wllh dan har abada ta rasa nagartacce kamar jikana....", Nurain ya haɗiyi wani yawu cause his wound is still fresh yace "bari na kira miki angon naki", wayarsa ya ciro daga pocket ya kunna data ya shiga kiran Farooq video call. ba ta daɗe tana ringing ba Farooq ya ɗaga. Nurain yayi waving hannunsa a screen ɗin wayar yace "ba fa na ganinka, ka kunna haske Iron Lady ke son magana da kai", Farooq yace "Ohh really, seee yaah My bride" ya miƙe daga kan table ɗin karatunsa ya kunna Light, fuskarsa ta bayyana raɗau sbd haske, yau ma dai jibgegiyar sweater ce ajikinsa, Farooq yace "tana ina?", Nurain ya haska masa fuskar Hajiya, Hajiya na ganin Farooq tace "innalillah wa'inna ilayhirraji'un me ya kumbura ka haka sai kace wanda aka buga masa iska?", Farooq yayi murmushi sbd ba abinda yake gani sai fuskarta da kantamemen glasses ɗinta sun cika screen ɗin wayar. Hajiya tace "ka yiwa Allah da manzon sa ka dawo gida", Farooq yace "next week zan dawo amaryata", tace "Atoh ya dai kamata wnn kumburi haka..", Farooq yace "ba fa kumbura nayi ba rigar sanyi ce, bari na cire ki ga", da sauri ta katsesa tace "A'a karka cire ka daskare, tinda dai baka kumbura ba shknn", Farooq yace "toh shknn". tace "kaga wnn fel wayar wai shima ƙasar arnan zai koma sbd shegiyar yarinyar da zai aura ta gudu ta barsa shine ba zai nemi wata ba", Farooq was shocked da abinda ta faɗa amma yace "ni kam ina dawowa zan miki kishiya", tace "Eh maza ka dawo kayi min ai kishiya alheri ce indai ta gari ce..", yace "Au ba kya kishi na kenan?", tace "kaji wani zance yo wnn ai shine kishin", Farooq ya murtuke fuska kamar gaske yace "ni bani ɗan uwana", Nurain ya karɓi wayar don yanajin komai da suke faɗa. Farooq yace "so that's why you said until your heart heal?", Nurain ya gyaɗa kai yace "sure, and now it's healing..", Farooq yace "wish you all the best bro", Nurain yace "thank you i will call you tomorrow" ya katse kiran. ganin magrib na dosowa yasa Nurain ya yiwa grandmother ɗin tasa sallama, Hajiya tace "toh yanzu sai yaushe Usuman?, kaima shekarun zaka ɗauka kamar Umaru ko?", yace "A'a Hajiya, wata takwas zan yi insha Allah na dawo gida", tace "O oho har wata takwas ɗan nan, Allah ya tsare...", ta miƙe tana dogara sandarta ta shiga bedroom ɗinta, bayan wani lokaci ta fito da ƴar leda tace "ungo na kane kai kaɗai, karka tsamma kowa", ya karbi ledar yana leƙa cikinta yace "wai har takwarar taki?", tace "A'a ni ba takwarata bace, ni ba sunana Noor ba", yace "ai ɓoyewa akai, to Hajiyarmu khairan", Hajiya ta fara matsar kwalla tace "to Usuman ka kula da addininka don Allah", yace "insha Allah" da haka ya nufi door ya fita, saida sukay sallama da Ummi snn ya wuce.


★Tin safe Hajar take neman hanyar da zata sanar da Anty zuwan Nura, sau biyu tana attempting amma saita kasa, a zaune take akan stairs ɗin varendern palour, wayarta ce ta fara ringing, yamutsa fuska tayi ganin numbern dake kiranta, a fili tace "na shiga uku wai wnn wane irin naci ne", tana kallon wayar har kiran ya katse wani ya sake shigowa, 20+ missed call yayi mata daga safe zuwa yanxu, da kyar ta ɗauka ta wani sha kunu, daga ɗaya ɓangaren Ahmad yace "Assalamu alaikum", a wani daƙile tace "wslm", yace "how are you?", tace "fine", yace "alhmdllh, Hajar plxx just give me a chance to show my feelings", tayi gathering courage tace "don't you have anything else better to do?, I'll pretend that I didn't hear that", ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace "you heard everything, you can't pretend that you didn't", ta ciji lower lip ɗinta painlessly dan sosai maganarsa ta shigeta, tace "i have to hang up....", pleadingly yace "plxx answer me before you hang up", kasa cewa komai tayi, shiru ne ya dauka har hakan yasa su ke jin breathing din juna, tayi twinking lulu eyes dinta tace "aiki nake yi", after few seconds yace "alright...", da sauri ta katse kiran ba ta jira sauran cewarsa ba. blocking numbernsa tayi snn ta goge call log ɗinsa gaba ɗaya, murya can ciki tace "Allah ya baka gaba Ahmad". bata da wani space a zuciyarta, Nura has already filled everywhere. knocking gate aka yi ta miƙe ta buɗe, su Hafsa ne suka dawo daga school, Hajar ta matsa musu hanya tace "barka da dawowa yan bokoko", Hafsa tace "na dai kusa gamawa", ƴar autar Anty kam tini ta wuce ciki tana fige hijab ɗinta. bayan Sallahr la'asar Hafsa ta shiga ɗakinsu tana dafe kai, Hajar da ke nannaɗe darduman da tayi sallah tace "lafiya?", Hafsa ta yamutsa fuska tace "kaina ke ciwo", Hajar tace "sannu kinsha magani?", Hafsa tace "A'a yanzu dai zan je wajen Anty na amso paracetamol", Hajar tace "okay, zauna na kama miki kan sai kuma kisha magana za kiji sauƙi sosai", Hafsa tace "tom" ta zaune gefen gado, gefenta Hajar ta tsaya snn ta fara kama mata kan tana hura mata addu'a, tana gamawa ta matsa thick vein ɗin goshin ta yarfe tace "toh ya kika ji?", Hafsa tace "wllh har ya lafa sosai" ta mike zata fita a ɗakin, Hajar tace "wajen Antyn zaki amso magani?", Hafsa ta gyaɗa mata kai, Hajar tace "dan Allah kice mata anjima zanyi baƙo", Hafsa tace "Au haba mutumin jiya ne zai zo?", Hajar tace "kinji ki da wani zance wai mutumin jiya toh bashi bane", Hafsa tace "toh waye?", twinking eyes Hajar tayi tace "Ya sayyadi na ne zai zo", Hafsa tace "wai daman har yanzu kuna tare da Nura?", Hajar tace "Eh, ai iyayensa ma sunje wajen Baba", Hafsa tace "kaiii amma shine baki fadamin ba, da yaushe zai zo?", Hajar tace "da yamma", Hafsa ta fita daga ɗakin ta shiga kitchen ta ɗauki pure water snn ta shiga room ɗin Anty, motsin ruwa taji a toilet, bedside drawer ta janyo ta fara neman Panadol tinda anan suke ajiye first aid drugs, ta dauke panadol ta ɓalli two tablets ta mayar da sachet ɗin. da kyar ta haɗiye maganin tana yamutsa fuska, Anty ta fito daga toilet tana gyara hular kanta tace "ku shirya ke da Hajar muje barkar Fauziyya", Hafsa tace "yanzu zamu?", Anty tace "Eh", Hafsa ta ɗaga ragowar pure watern da ta sha drug tace "Anty wllh kaina ke ciwo yanzu ma nasha magani, ko na bari ranar suna naje da yamma", Anty tace "tom shknn, kyaje ranar suna dama ba zuwa zanyi ba", Hafsa tace "tom, Hajar tace anjima za tay baƙo", Anty ta ciro kayan da zata saka daga wardrobe tace "ke ta aiko knn?", Hafsa tace "A'a wai bazata iya gaya miki ba", Anty tace "toh shknn, sai ta saukesa a sitting room, akwai semosa a fridge", Hafsa tace "tom" ta miƙe ta fita. Anty tana gama shiryawa ta ɗauki handbag dinta ta fita, ɗakinsu Hafsa ta shiga tace "toh sai Allah ya dawo dani", Hajar tace "Allah ya tsare", Hafsa tace "sai kin dawo". Biyar da rabi na yamma Hajar ta fito daga wanka, ta shafe jikinta da sabon cream ɗinta mai daɗin ƙamshi, riga da skirt ta saka na atamfa ta tsaya gaban mirror tana cakare ɗauri, Hafsa ta shigo tace "uhmm kinyi kyau, na gama soya semosan", Hajar na zizara kwalli a fatar manyan idanunta farare ƙal

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login