Showing 219001 words to 222000 words out of 237912 words

Chapter 74 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt

27 Nov 2024

23396

abinci, sai da ya kammala yaje sallar magrib da isha'i ya dawo sunyi zaman kallon labaran dare ya tambayeta. Da farko tata noƙewa akan ƙin faɗa ya nuna ɓacin ransa.
Kuka ta fashe masa da shi ta shiga basa labarin abinda duk ya faru. Shima yaji daɗin abinda maimartaba yayi. yakuma taya baba murnar samun ƙaruwa. Tare da jajanta abinda ke faruwa ga Inna da ƴaƴanta. Sannan ya ɗaura da lallashin matarsa ta hanyar daya dace.


Kwana biyu dayin wannan maganar Zinneerah ta kira taima Baba barka da tashin baƙi dajin yaya jikin Inna yake sanar mata ai jiya AK ya aika Khalipha danya. Yanzu haka Inna na asibitin katsina yau da safe aka wuce da ita. Ya kuma biya kuɗin sarƙar Karima ɗin.
Wannan zance ya saka Zinneerah matuƙar farin ciki dajin ƙaunar mijinta kuma Yayanta. Yana shigowa gidan tai masa ƙyaƙyƙyawar tarbar da bai taɓa samu daga garetaba. Dan yau fidda kunya tai abinta ta manne bakinta da nashi ta shiga masa salo akan karatun da yay mata. Wannan al'amari ya gigita AK musamman daya kasance ta cuɗe jikinta da turarukan dake neman zauta masa tunani. Yako zage wajen bata haɗin kai har sai da ta koma masa raki.
Sai da ya kai boader ya koma mata dariya da tambayarta wai minene sirrin?. Baki ta dinga tura masa tana zuba masa shagwaɓa. Sai da suka tsaftace jikinsu ta zaman masa godiya. Nuna mata yay shi baima san anyi hakaba. Maybe Khalipha ne yayi kawai.
Tasan sarai yayi hakane dan ya goce, bawai dan abinda ya faɗa gaskiya bane.


Haka rayuwar waɗanan ma'aurata ta cigaba da tafiya cikin aminci da kwanciyar hankali, duk da dai wataran saɓani kan gifta musu har rai ya ɓaci. Musamman daya zamto halinsu na kamanceceniya da juna wajen miskilancun tsiya. Little kan leƙosu kwana ɗaya biyu ya tafi, wani lokacin yana gidansu Granny wani lokacin yana gidansu mmn sadiq. Khalipha kuma kanje Danya shi da Dr Mahmud daya fola Sa'a tun a wajen biki batare da sanin su AK ba.
Sunata shirye-shiryen bikin ƴammatan gidan daketa gabatowa. Adilah ma na Nigeria bata komaba su Mammah ne kawai suka tafi.


Bukatar komawa ganin likitan Granny yasa AK shirya musu tafiya harda little. Dan yanason zuwa shima yaɗanyi wasu abubuwa acan kafin su dawo wajen biki kuma.
Zinneerah batasan da wannan shiri nasaba sai ana saura kwana biyu ya ɗauketa suka nufi Danya shi da ita da little. Wani irin farin cikine ya baibayeta ganin inda suka nufa. Ta kwanto jikin hannunsa da faɗin, “Oh oh thanks you so much Yayanmu”.
Murmushi ya ɗanyi yana sake maida hankalinsa ga tuƙi. Yace, “Yayansu dai, dan kekam kin gama gane Yaya ciki dabai yarinya”.
Kunyace ta kamata, ta maida kanta gefe tana ƙyalƙyala dariya. Little dake baya yanata harkokinsa da game da Khalipha ya saya masa shima jin dariyarta ya sashi ƙyalƙyalewa da tasa. Dariya suka shigayi saboda yanda yay dariyar abin dariya.
Tarbar data bama Zinneerah ɗunbin mamaki suka samu a garin Danya, dan bama ƴan gidansu ba hatta da maƙwafta shigowa suketayi. Itako cikin mutunci taketa gaida kowa. Suka dinga daukar little zukatansu fal mamakin yanda aka samar dashi. Tausayin Tinene ya kamata saboda itama ta ɗanɗana rainon cikin nan taji yanda yake musamman a irin wannan yanayin da mutane ke tsanarka da ƙinjin tausayinka. Dan Tinene dukta rame ta lalace cikin na bata wahala. Yayinda ta ɗauka ƴan biyun amaryar babansu kuwa sai daɗi ya kanainayeta ta dinga samusu albarka. Cikin tsokana amaryar Baba ke faɗin. “Ai saura ke ɗiyata, dan wannan ƙyawun da kika ƙara ai in kaji gangami da labari”.
“Kai Mama ni ALLAH bani da komai, kawai dai idanunki ne”.
Yaya Gajeje dake bama little abinci tace, “Haba Zinni ai duk wanda ya dubeki yasan kinada ciki, fatanmu dai ALLAH ya raba lafiya muje musha shagalin suna kamar na aure”.
Cikin shagwaɓa tace, “Kai Yaya Gajeje nifa banda komai”. Dariya suka sanya mata harda Karima da a yanzu take jin wani son Zinneerah ɗin, dan badan mijintaba lallai da yanzu tana birsin. Yanzu ɗinma a zuwansun nan sai da taje tai masa godiya ta musamman harda kukanta.
AK yace karta damu, shi komai zai iya musu akan Zinneerah. Fatansa dai ALLAH ya kiyaye na gaba kuma. Baba ma ya masa godiya sosai. Sukaje kuma har gidan maigari ya gaishesa tare da su Baba Sabi'u.
A firarta da Yaya Sa'a takejin batunta da Dr Mahmud. Taji daɗi tayi farin ciki. ta kuma taya Yaya Sa'a murna duk da Dr Mahmud nada mata da yara biyu. To amma tasan shi mutumin kirkine, dan haka ta taya ƴar uwarta farin ciki da wannan abun arziƙi.
Inna na asibiti har yanzu tare da wata kanwarta dake jinyarta. Suma sai lokaci-lokaci suke zuwa su dubata su dawo. Zinneerah taso lallaɓa AK suje ta dubata itama amma tanajin tsoro, dan dataje kai masa abinci take roƙonsa ko zasu ƙarasa katsina su gaida Aunty Farah wani shegen harara daya kaɗa hanjin cikinta yay mata. Dole ta fito sim-sim tana dana sanin yin maganar. Itako tayine saboda sanin har yanzu Yayan nasu na ƙaunar matarsa. Yana dannewane kawai saboda fushin laifin da suka aikata masa. Amma Sometimes idan suna fira zakaji yakan sakkota koyin misali da wani abunta yace Farah kaza Farah kaza. Tanajin zafin hakan sabida kishi, amma bata ganin laifinsa. dan tasan soyayyar da yake nunawa ga aunty Farah itama ko aure ya ƙara zai iya nunawa gareta bazai wulakantataba. Dan tunda suke bai taɓa kushe Farah a gabantaba, bai kuma taɓa yimata wani zancen halinta mara ƙyau ba indai kaji zancen Farah a bakinsa to alkairintane.
Yini guda sukai a Danya, dan basu tahoba sai gabannin magriba. Lokacin da suka shigo garin kano ana sallar isha'i.
Washe gari kuwa nan ma da kansa ya kaita gidan Mmn Sadiq danta yini. Sunyi farin cikin ganin juna itada mamanta da yan uwanta matuƙa. Duk da kuwa a yanzu tana waya dasu a koda yaushe. Hakama mmn halima da Abbah tare da ƴan biyun mmn Halima da suka fara zama ƴan mata. Dan jira kawai suke a kauda Sakina da miji ya gagara samuwa suma su ƙara zabgewa.
Nanma yini tai zur dan sai dare ya aika Khalipha ya ɗakkota saboda shi ya tafi wata sabgar shi da Dr Mahmud.


A ranar da daddare yake sanar mata gobe idan ALLAH ya kaimu zasu wuce london su da Granny. Bazasu dawoba sai bikin su Safiyya daya gabato gab danma ɗagashi da akayi saboda na Adilah daya shiga ai da wannan watanne za'ayisa.
Jin harda Granny za'a tafi yasata nuna jin daɗinta sosai. dan ita dai duk da Mammah ta nuna ƙaunarta daga baya tana shakkar matar har cikin ranta. Sai dai taso ace harda su Bahijja ma a wannan karon amma yaya zatai tunda aure take yanzu. Ga ssce exams ɗinsu zasu fara batasan yaya yake nufiba, amma dai bazatai maganaba tunda tasan ya fita sanin muhimmancin karatun ai. Suma kuma su Bahijjan zaman yaran Uncle Ahmad a gidan yanzu ya ɗebe musu kewarta sosai. Danfa Granny ta kafa ta tsare ta hanashi komawa. Dan kuwa dai bai shirya kara aure ba. Matarsa taci kuka harta gode ALLAH ta haƙura. Dan harma yaje ya tattaro musu duk abubuwansu masu muhimmanci da yoma yaransa transfer ɗin makaranta zuwa Nigeria. Manyan ne kawai dake jami'a zasu koma su ƙarasa.............✍




*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍






*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*


*_TYPING📲_*




*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*




_______________________






*Page 66*


............Washe gari da yammaci jirginsu ya ɗaga zuwa Birtaniya. Inda al'amari yaso ƙwaɓema Zinneerah. Dan tamkar jira jirginsu na ɗagawa amai ya ringa taso mata. Ganin yanda taketa rintse ido da yamutse fuska yasa AK taɓata. Ido ta buɗe da ƙyar tana dubansa. “Lafiya dai?”. Ya tambaya cikin kulawa.
“Yayanmu amai nakeji wlhy”. Ta faɗa da ƙyar tana danne bakinta da hannu. Cikin mamaki yace, “Amai kuma?”. Kanta ta ɗaga masa tana miƙewa da sauri domin zuwa toilet. Dole shima ya miƙe yabi bayanta, Hajiya Iya na tambayarsu ko lafiya ma basu jitaba.
Sosai ta jigatu wajen yin aman, sai da ya taimaka matama sannan suka fito. Ganin yanda duk ta jigata hajiya iya ta shiga salati. “Inno baki da lafiyane dama aka ƙirƙiri wannan tafiyar dake haka?”.
Kanta taɗan jujjuya mata da ƙyar, murya a sanyaye tace, “A'a Granny lafiyata lau, kawai yanzu ne dai na dinga jin aman”.
Khalipha dake mata kallon tsaf ya ɗauke kansa yana murmushi da gyarama little dake jikinsa yana barci zama. Hajiya iyama kallon tsaf takema Zinneerah ɗin har wasu mintuna. Kafin tai murmushi da faɗin, “To ALLAH ya rabaku lafiya, ya inganta kuma”.
“Amin” Khalipha ya amsa mata. AK da duk bai fahimcesu ba ya kalli hajiya iyan sai dai baice komaiba. Harara ta zuba masa tana mita. “Ka wani tsareni da ido minaci ban bakaba to?”.
Ƙara tsuke fuskarsa yay yana ɗauke kai gefe batare daya tanka mataba. Sai dai har cikin ransa waswasin maganar tata yakeyi. Ya kwantar da Zinneerah jikin kafaɗarsa yana gyara mata mayafinta. Cikin ƙanƙanin lokaci sai ga barci yay awan gaba da ita. Itace bata farkaba sai gab da zasu sauka.


Abin mamaki sai ga Mammah tazo da kanta ɗaukarsu. Cikin girmamawa kuma ta gaida Hajiya iya tare da rungume Zinneerah da duk alamun rashin lafiya ya bayyana gareta. Khalipha ma cike da kulawa ta amsa masa gaisuwarsa tana dungure kan little da yaƙi zuwa wajenta ya maƙale Khalipha ɗin.
Har cikin rai AK yaji daɗin canjawar mahaifiyar tasa. Sai dai bai nunaba ko'a fuska. Tunda ya gaishetama sai ya ɗauke kansa ya maida ga waya.
Sun iso gidansu da suka samu ƙal an gyara, ya kuma san aikin Mammah ne da Mahma. Nanma yaji daɗi. Hajiya iya ɗakin data zauna wancan karon ta sauka. Khalipha ɗakinsa. AK da Zinneerah ɗakinsa. Dan ɗakin Farah ma a rufe yake bai kuma nuna alamun son a buɗeba.
Wanka ya taimakawa Zinneerah tayi ta kwanta dan zazzaɓi ne rijif a jikinta. Ga yunwa na cinta dan bataci komai a jirgi ba. Hakan yasa AK tsareta taci abincin da Mammah ɗin ta kawo musu. Da ƙyar tai lauma uku, sai gata hanyar toilet da gudu. Duk binta sukai da kallon tausayi, AK idonsa ya kaɗa yay jajur, dan shi ya rasa wannan amai na minene?. Bayan ya taimaka mata ta fito ya kwantar da ita sannan yazo falo yana cema Khalipha yazo suje asibiti dan shi wannan amai ya rasa na miye ko wani abu taci ya bata mata ciki.
Dariya ta kusa suɓucema Khalipha akan wannan zance, a ranaa yace, (Waken daka batane Yayanmu ya bayyana kansa) a fili kam sai yace, “Uhm ai Yayanmu bara dai na duba mata wani magani kozai taimaketa, amma wannan amai ai na farin cikine bana ɓacin ciki ba”.
Fuska ya ɗaure tamau yana hararsa, “Shi aman har abin sone?”.
Mammah da itama dariya ke cinta tace, “Barma yarona mazurai malam, ai gaskiya ya faɗa wannan amai abin so ne, dan kuwa dai na rabone sai dai muyi fatan ALLAH ya sauketa kafiya”.
Karon farko AK ya ƙwalalo idanu waje yana kallon Hajiya Iya da Mammah dake dariya, ya maida ga Khalipha daketa ƙoƙarin ɓoye tashi. “Nikam ku fiddani a duhu, kuna nufin ciki ne da ita komi?”.
“Tabbas hakane Yayanmu, Congratulations”.
Kasa motsi AK yayi dan alja'ab ko ruɗani zai ce. Sai gani kawai sukai yakai gwiyawunsa ƙasa yay sujuda ga UBANGIJIN talikai mai badawa ga wanda yaso a kuma lokacin da yaso, kafin ya koma gaban Hajiya iya ya rungumeta, ya saketa itama Mammah ya rungumeta, kafin ya koma kan Khalipha.
Yana sakinsa ɗakinsa ya nufa cikin sassarfa, cikin barci Zinneerah taji an mata wata lafiyayyar runguma ana sakar mata kissis tako ina a jikinta. Ta buɗe idanu da ƙyar tana kallonsa. Jin godiya da kirarin da yake jerama UBANGIJI tare da addu'ar ALLAH ya sauketa lafiya ya sata fahimtar lallai zancem su Yaya gajeje ya tabbata cikine da ita, hawayene suka silalo mata na jin daɗi da tausayin kai. Tayi farin ciki dan tasan koba komai mutane da yawa zasuyi farin ciki ta silar wannan cikin, sannan ta tausayama kanta dan tasan da wahala karatunta bai salwantaba.
Aman daya taso matane ya sakata samu AK ya saketa ta nufi toilet da gudu. Wani irin tausayinta da ƙaunartane ya kamashi ya dafe kansa yana mai jin kamar inama ace zai iya rage mata wani yanki na raɗaɗin da takeji.


Khalipha ne ya fita dole ya samoma Zinneerah maganin dazai taimaketa ta ɗan huta da aman duk da dai yasan baizama lallai ta daina duka ba. Cikin amincin ALLAH kuwa tana sha sai barci. Daga haka suka cigaba da farin cikinsu, yayinda labari har ya kaima ƴan Nigeria.
Zo kaga murna wajensu Meenal da dariyar mugunta wai su Zinneerah an cika zalama, daga shiga harta ƙumso. Sunji inama zasu iya samun wayarta su baɗaɗeta da sheri.
Mammah ma cikin farin ciki ta komawa Mahma da wannan daddaɗan labari. Sosai itama tai farin ciki da shiga jerama Zinneerah addu'ar lafiya mai inganci. ta sake ɗorawa da yima Mammah nasiha kamar yanda takeyi kullum yanzu tunda suka dawo. Hakkanne ma ya ƙara sakama Mammah nutsuwar zuciya da sake duƙufa neman gafarar ALLAH.

Sabon tattali Zinneerah ta fara gani a london hannun AK da mahaifiyarsa da Mahma. Hajiya iyama duk da tana ƙarƙashin kulawar likita tana binta da addu'a da dabarunsu na tsoffi. Dama little tun kwana biyu da zuwansu ya koma gidansu Mammah ɗan gata. Hakan yasa AK samun damar baje sharafin soyayyarsa a cikin gidannan. Dan Khalipha na musu kawaici da basu fili yaje yay zamansa wajen Hajiya iya susha hira.
Ita kanta Zinneerah ɗin shegen ƙwaɗayin da cikin yazo mata da shi yasata sake nanuƙema AK, dan babu abinda tafi ƙauna daso kamar ƙamshin turarensa da kasancewa dashi. Randa tai waya dasu Bahijja tasha Sheri, hakama su Sa'a nata tsokanarta.
Ita dai babu baki dan ya mutu murus. Suna cikin sati na uku da zuwa jikinta yay ɗan mata ƙarfi irin na mai ciki, yau lafiya gobe jangal. Gyaran ɗakin nasa ko nace nasu tai ƙoƙarin yi, tanayi tana ɗan hutawa harta ga yay mata ƙal. Tana cikin gyaran ne sai ga idonta takai kan tsohuwar wayarta da aka sace a ɗakin hajiya iya. Mamaki yasata jujjuya wayar tana kallo dason tunani yanda akai tazo London, london ɗinma ɗakin Yayansu.


“Malama miya kai idonki nan?”. Taji an faɗa a bayanta cikin dakakkiyar murya. Tasan Yayansu ne, dan haka ta juya fuska a ƙwaɓe tana kallonsa da cigaba da juya wayar a hannunta. Takowa ya ƙarasa yi cikin ɗakin yasa hannu ya amshe wayar fuska a tamke. Ya ɗaga ƙafa zai juya ta riƙo hannunsa da faɗin, “Wai Yayanmu dama kaine ka sacemin waya?”.
Harga ALLAH yanda tai maganarne yay matuƙar bashi dariya, duk yanda yaso cigaba da pretending ɗin mazuran nasa sai gashi ya saki murmushi da hararta. Ya dungure mata kai yana cije lip ɗinsa na ƙasa.
“Yarinyarnan kin fara rainani ALLAH. Ni nema ɓarawo ko?”.
Hannu tasa ta rufe fuskarta tana murmushi. “Nidai bance dakai barawo ba. Amma idan ta gaskiya za' sace wayarnan akai na nemeta na rasa”.
Cak ya ɗagata da ƙasa yay saman gado da ita yana faɗin, “To bara na nuna miki ba satar waya kaɗai na iyaba yarinya”. Ya ƙare maganar da tura hannu cikin ƴar fingilar rigar jikinta da iyakarta cinya. dama ta sakatane dantayi aikin a sake babu takura. Dariya ta shiga ƙyalƙyalewa tana faɗin, “Na tuba wasa nakeyi ALLAH”.
Kobi takanta baiyiba ya lula da ita duniyar kodumo, dama ita kam duk sanda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login