Showing 183001 words to 186000 words out of 237912 words

Chapter 62 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt

27 Nov 2024

23430

kan ɗaya ya jingina da kujera ya lumshe idanunsa, yayinda Farah ta kafesa da ido zuciyarta na harbawa da sauri-sauri akan yanayinsa. “Mammah waini Abdul-Mutallab zai jefa ubana da kalmar suna bunsuru!”.
A kusan tare Mammah da Mahma sukace, “Bunsuru kuma?”.
“Ai gashi nan ku tambayesa mana”. Ta sake faɗa tana fashewa da kuka.
Ganin ko motsi baiyiba yasa Mahma kallonsa da ƙyau tace, “Abdul-Mutallab!”.
Idanunsa ya buɗe a hankali ya kalleta batare daya motsa ba. “Miya kaika wannan zance haka babu daɗin ji? Zakiyya ba yayarka bace?”.
Murmushi ya saki mai ƙayatarwa a karon farko da ɗan yamutsa fuska, kansa tsaye yace, “Mahma ni ƙarya takemin, ita da bakinta ta kirashi hakan”.
Ba mahma ba har Farah sai da ta maida kallonta ga Aunty Zakiyyan da tace, “Kaji munafiki, dagafa na masa magana akan ƙara aurensa nace miyasa zaita tara mata kamar wani bunsuru shine yace wai masu mata huɗu da ƙwarƙwara fa? Kenan yana nufin Abbanmu ko?”.
“To ke miya kaiki faɗa masa haka Zakiyya da girmanki? Aure ba ALLAH ya halasta ayisa ba? Taya za'a danganta wanda yay koyi da MANZON ALLAH (S.A.W) da wannan mummunar kalmar domin ALLAH idan ba neman tada zaune tsaye ba? Dan ALLAH ku ringa sassautama kanku, rayuwarma duka nawa take ALLAH natuba. Kai kuma Abdul-Mutallab baka ƙyautaba daka bata wannan amsar, saika fahimtar da ita kuskurenta ko kai mata shiru”.
“Am sorry Mahma” ya fa ɗa batare da nuna nadamar abinda yay ma aunty Zakiyya ba. Mammah kuwa kasa cewa uffan tayi. Zakiyya ma ƙin cema Mahma komai tayi, dan kai tsaye ta fassara abinda Mahma tayi da son kai. Duk da Mahma ta fahimceta batabi dakantaba ta fara musu nasiha su duka. Sai da ta gama AK ya samu damar gaishesu.
Rai ɓace Mammah tace, “Sai yanzu muke ganinka a gidan? Bayan kasan matarka na cikin halin rashin lafiya, Abdul-Mutallab! Abdul-Mutallab! kana shigarmin hanci fa da yawa”.
Murmushi yayi yana gyara zamansa. Cike da girmamawar da yake bata yace, “To yi haƙuri karki fyatoni Mammah, ba gani nazoba yanzu kuma nama ganta ragal”.
Harara Mammah ta zuba masa kawai dan takaici, zata ƙara magana Mahma tai saurin katseta da faɗin, “Tunda ya nema afuwa basai a sarara masaba a kama wata tashar kuma”.
Dole Mammah ta haɗiye maganar tana marairaice fuska. “Ke kam Addah bakison ace yayi abu saiki fara karesa, to naji yanzu sai ya nema mana ticket ɗin tafiya Morocco”.
“Morocco kuma Mammah? Mizakuyi acan a irin wannan lokacin daba komai akeyi ba?”.
“Eh to lallai ubanmu, sai ana wani abu zamuje tushen uwarmu kenan? To Farah zamu kai ta ƙarasa rainon cikinta acan har sai ta haihu.”
“Kaji kuma wani abu, to banda abinki Mammah sai kace mai cikin fari? sannan wancan karonma bacan tajeba har ya zama sanadin fitar cikin? Ni wannan karonma na yanke shawarar a Nigeria zata haihu babu inda zataj......”
Tassss!!! kakejin sautin fashewar kofin hannun Farah da take shan tea tun shigowarsa. aunty Zakiyya kam a bazata tace, “What!”. Mammah kuma ta ɗan zabura jikin kujera da faɗin, “Baka isaba ko!”.
Yanda sukai ɗin ba ƙaramin mamaki ya bama Mahma ba, shiko sai yay wani shegen murmushi da komawa ya lafe jikin kujera yana zuƙar sassanyan numfashi da iskar ac ke busowa.
Mahma tace, “To minenen abin razana anan? Dan kawai yace a Nigeria matarsa zata haihu? Ai hakan da yay shine dai-dai, kuma shine zai ƙara kawo dai-daito tsakaninta Farah da ƴan uwansa ko?”.
“Adda bazai yuwuba wlhy, karma ki goya bayansa a wannan gaɓar dan tafiya da Farah kamar nayi na gama ne, sannan maganar yarinyar dake gidanka yaya muke ciki?”.
“Ki tayamu addu'a kawai Mammah”. Ya faɗa kansa tsaye.
“Uban addu'a zan tayaku ba addu'a ba Abdul-Mutallab, ni kake gayama na tayaka addu'a akan wannan figaggiyar yarinyar da'a haihuwar kaji ka isa haifarta, to wlhy tunma muna shaida juna ka sakar musu yarinya ko na ɓata maka ranka”..
“To amma Mammah baƙya ganin idan na aikata hakan shima Baffah zai ɓata ran nawa? Kiyi haƙuri kawai kamar yanda nai biyya a zaɓinki shima nayi biyayya anasa. sannan kuma idan ina sonta kuma fa....”
Kafinma ya rufe baki Farah ta fashe da wani irin razanannen kuka sai da Mahma ta daka mata tsawa tasa hannu ta toshe bakinta tana faɗawa kan Mammah.
A zafafe aunty Zakiyya tace, “Wlhy inma baka saketaba da ƙafarta saita bar gidan”.
Banza yay kamar bai jitaba, zata sake magana Mahma ta harareta dole tai shiru tana ƙunƙuni. Cikin rawar murya na alamar jin zafi Mammah tace, “Abdul-Mutallab na rantse zan iya tsine maka akan auren yarinyarnan. Dan haka na baka kwanaki bakwai kacal ka sallameta. Idan kuma ka kuskura ko ɗan yatsanta ka taɓa ALLAH ya is......”
Da sauri yace, “Oh Mammah Please!.....”
Yanda yay maganar cike da ƙosawa ya sata dakatawa tana kallonsa. Cikin ƙunar da zuciyarsa ke masa yace, “Bama sai kinyi wani ALLAH ya isaba haba sweetheart, nifa wasa nake miki kawai dan naga yaya ƴarki zatayi? Tana sona har yanzu kokuwa?, indai nine ki bani wata ɗaya kacal zanyi komai a tsare yanda shima Baffah bazaiga na masa tsageranci ba harya canja wata hanyar da ni dake zamu gaza ganewa kuma ok?”.
A yanda yay maganar seriously yasata yarda dashi, dan tasan halinsa bayason dukkan abinda zai ɓata mata rai, cikin gamsuwa tace, “Idan ka saɓamin alƙawari Abdul-Mutallab bazan maka da sauƙiba fa”.
“Karki wani damu kanki Noorunnisa, sai dai ga shawara, dan akwai abinda naɗan hango idan akace na saketa yanzun, kiɗan sassauta kinsan shima Baffah akwai taurin kai, idan wata ɗaya bataiba zan iya kaiwa biyu ko uku haka, dan dole na haɗa da Granny, kinga hakan na nufin kenan gara ayi sakin cikin hikima yanda zan ɗaura laifin akan wani abu taimin ita yarinyar bawai kece kika saniba. Dan wlhy yanda Baffah ya fusata nace zan saki yarinyarnan yanzu to kuwa zai auramin mata uku rana ɗaya, ya kuma kafamin sharuɗɗan masu tsauri da bazan iya yin wani abuba, kinga kema yaci galaba a kanki kenan, amma idan cikin hikima mukai komai sai a rabu lafiya. Taɓa yarinya kuwa ki ɗauka ko kallo bata ishi Abdul-Mutallab ɗinki ba, na Farah ɗinkine kawai har a aljanna”.
Karan farko ta saki tattausan murmushi da cewa, “To ALLAH yay maka albarka, naɗan gamsu da bayaninka danni shaidace akan Kabeer da halayensa, amma kamar yanda ka faɗa ta wannan hanyarne kawai zamuyi maganinsa da wannan kakar taku sarkin iko wa ƴaƴan wasu”.
“Amin sweet Mammah”. Ya faɗa yana wani shegen murmushi daya zafafa zuciyar aunty Zakiyya ta miƙe fuuu ta shige. dan itakam tsaf ta fahimci shirya rainama uwar tasa hankali yayi kawai.
Mahma kuwa murmushi tayi itama da cewar “Nasan zaka iya Abdul-Mutallab, kamar yanda Hindatu ta faɗa haka mukeson kayi, abinda yasa zan goya bayanka kamar nan da wata ukun saboda dalilan daka faɗa suna akan hanya”.
“Nagode Mahma” ya faɗa yana wani lumshe idanu da komawa jikin kujera ya lafe abinsa.
Sosai dariya kecin zuciyar Mahma tanata ƙoƙarin danneta, a ransa kuwa tanata saka masa albarka da ƙarajin ƙaunar AK ɗin har cikin ranta. A kullum ƙoƙarin sa yaga ya kauce ɓacin ran mahaifiyarsa koda ace ya fita gaskiya, irin wannan ƴaƴan sune abin buƙatar kowa, dan suna ƙoƙarin kiyayewa daga fushin mahaifiya, su kuma kautar da ita faɗawa halaka itama dake zuwa akan dokin fushi kona son zuciya.
Farah ma tashi tai ta shige ɗaki tana rusar kuka. Hakan yasa AK miƙewa yabi bayanta. Mammah zata bisu Mahma ta dakatar da ita.
“Kinga barsu ya lallashi abarsa da kansa. Babu ruwanki a wannan sabgar tunda kinji daɗi yace zai miki abinda kika buƙata saboda ƴar so ɗin taki”.
Ƙaramar dariya kawai Mammah tayi da komawa ta zauna. “Oh Addah kemafa kina bayanmu wannan karon bare kimana wa'azi”.
“Ai nabi bayankunne kawai saboda farin cikinki, sannan nima matar tasa bataminba tayi ƙarama da yawa”.
“To kema dai ƙya faɗa Addah, bandama namiji baida kunya ba, ta ina zai fara nuna wannan ƴar ficilar yarinya matsayin matarsa”.
Dariya sosai Mahma tayi abinta.


AK da Farah kam kusan tare suka shiga ɗakin, ta faɗa saman gado tana sake fashewa da kuka mai cin rai. Shiko yana shigowa ya ɗaure fuskarsa tamau da murzawa ƙofar key sannan ya ƙaraso gaban gadon cikin takun izza da bayyanar ɗacin da zuciyarsa ke masa ƙuru-ƙuru akan fuskarsa. Cikin tsananin kaushin murya yace, “K tashi zaune!”.
Sosai yanda taji muryarsa ya ƙara razanata. Dole ta miƙe zaunen dayace tana kallonsa idanunta cike da tsoronsa. Ƙafarsa ɗaya ya ɗora saman gadon ɗayar na ƙasa yana binta da wani shegen kallo daya saka jikinta fara tsuma tana girgiza masa kanta hawaye na rige-rigen fitowa.
“Share waɗan nan hawayen, kuma ki nutsumin wlhy kona karyaki a ɗakin nan na karya banza”. yay maganar yana matsar da fuskarsa gab da tata da nunata da ɗan yatsansa cikin gargaɗi. Hannu tasa da sauri ta goge hawayen tana magana cikin rawar murya, “Yah Abdul-Mutallab wlhy ba laifina bane, ni bani nace zanzo nan ba, tashi kawai nayi na ganni anan gidan”.
“Bashi na tambayekiba, dan matdalarkice ba tawaba wannan”. Ya katseta a kausashe.
“Dan ALLAH kayi haƙuri, wlhy banason kishiya, zan iya mutuwa ka taimakeni ka barni ni kaɗai, na rantse da ALLAH zan dinga maka duk abinda kake so daga yanzun”.
“Daga baya kenan yarinya. ai kin makaro kuma, dan na baki damammaki bama damaba amma kika cigaba da ɗaukata ɗan iska ko maijin tsoronki ma. Dama na tabbatar miki a randa yaran nan sukaje London inhar kika sakamin ciwon kai sai na baki na zuciya. Koda yake wannan duk bashine a gabanaba yanzu, dan idan na tafi kema kinsan bana waiwaye. Gargaɗi zan miki idan kinbi kin huta, idan kinmin taurin kai da shirya samun ciwon kai wlhy sai na saka miki na jini bayan na zuciyar da kika samu yanzun, kindai sanni sarai. Koda ban miki gargaɗin nanba nasan baki da wata dama ta sake barin ƙasar nan yanzu, amma dole zan miki. Kiyi duk yanda zakiyi ki tabbatarma da Mammah zaki haihu a Nigeria, inba hakaba wlhy ki kuka da kanki, dan inhar ta ɓata ranta a kaina toke zuciyarki da kamanninki zan ɓata gaba ɗaya a rasa ganeki. Ki kuma nutsu akan wannan haukar sumar da kuka da kikema mutane, bake kika jawa kanki kishiyar ba, saurama biyu zan ƙaro bayan wannan shashasha kawai”.
Ya ƙare maganar da sauke ƙafarsa ƙasa yana binta da wasu shegun looks masu riƙe maƙoshi da ƙahon zuciya.
Sai da yaje gab da ƙofa ya juyo cikin wani gargaɗin yace, daga nan zuwa kwana biyu ki dawo inda na ajiyeki, na baki kwana biyunne ma dan banason takurar kowa a cikinsu, idan kuma kin fita yanzu ki sanar musu duk abinda mukai a ɗakin nan, ni kuma na tabbatar miki sunana Abdul-Mutallab Kabeer Shira”.
Daga haka yay ficewarsa. Koda ya fito falon babu wata alamar akan fuskarsa dazai nuna ba lallashin Farah yayba da gaske. Bai zaunaba yay musu sallama akan yana son yin wani uziri ƙilama ya wuce Jigawa duba masu aiki.
Mammah ce ta kallesa cikin harara, “Ban gane zaka wuce Jigawa ba tickets ɗinmu fa?”.
“Oh GOD, Mammah Please kibar maganar zuwa Morocco ɗin nan dan babu ita, idan haihuwarta a london ne baƙyaso nace miki zata haihu anan ne. Zaku iya barmata Mahma su zauna tare kokuma a samo tsohuwa daga Morocco ɗin ta zauna da ita, ke kanki akwai maganar business da nakeson nayi dake wani abokina yanason kaya naga kuma kina dasu. Bye bye ana jirana nikam”.
Daga haka ya fice abinsa dan baiso ta ƙara tofa komai................✍





*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍








*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*


*_TYPING📲_*




*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*




_________________________




*Page 56*


..........Sai da ya tsaya yay sallar azhar a hanya sannan ya ƙarasa gidan. Tun daga falon farko yake jiyo dariyar su Meenal da Jamal. Ya ɗanyi shiru na wasu sakanni a wajen amma baiji muryar Zinneerah ba ko sau ɗaya, firar tasu kuma dukta makaranta ce Nawaf na basu labarin makarantarsu ta Turkey shima. Kamar zai nufi can sai kuma ya fasa ya ɗauka hanyar sashensa.
Khalipha dake zaune yana kallon television a falon nasa ya ɗago yana amsa masa sallamar da yayi. Cikin falon ya ƙaraso yana faɗin, “Am sorry besty na barka jira ko?”.
“No babu damuwa Yayanmu, nima ban wani jima da zuwanba sai da na biya ta asibiti”.
“Thanks”.
Yace masa kawai yana nufar hanyar bedroom ɗinsa. Kusan mintuna goma sai gashi ya fito sanye da ƙananun kaya da alama waɗan can ɗin sun damesa. Yana zama Khalipha ya miƙe ya buɗe fridge ya ɗakko masa ruwa.
“Thanks Darling”.
Murmushi Khalipha yay kawai ya koma wajen da yake ya sake zauma. Sai da AK yasha ruwan sosai dan ƙishirwar yakeji dama. Kofin ya ajiye yana gyara zamansa ƙafa ɗaya kan ɗaya ya ƙara komawa serious.
“Khalipha akan maganar da muka farone ranar, inason ka amsa min wasu tambayoyi”.
“Okay Yayanmu kaimin, inhar na sani zan baka amsa insha ALLAH ”.
Kansa ya jinjina masa da kai hannu yaɗan shafo sajensa zuwa gemu. “Yanzu idan nace kamin bayani akan dashen cikin gaba ɗayansa zaka iya?”.
“Zan iya Yayanmu, sai dai zai cimana lokaci matuƙa, kai kuma nasan bakason a cinye maka lokutanka”.
Sassanyan murmushi yayi yana ɗauke kansa daga Khalipha ɗin. “Ai wannan nine na bashi lokacin da kaina, sai dai kuma barsa kawai muje ga tambayoyin zasu wadatar dani insha ALLAH ”.
“Okay Yayanmu ina saurarenka to”.
Ɗan jimm yayi na wani ɗan lokaci kamar mai nazari, kafin ya duba Khalipha da ƙyau, “Bani bayani a taƙaice ta yanda za'a iya dashen cikin?”.
Zama sosai Khalipha ya gyara da nutsuwa. “Abunda kake magana ana ce mishi artificial insemination Yayanmu. Ana daukar maniyyi namiji (semen) a tace, a ɗauki sperms sai a haɗa da Kwan mace (ovum). Shi Kwan mace sai an shirya ake ɗaukan shi shima, anabada magunguna kafin ayi hakan, sannan ba haka kawai ake ɗauka ba sai an duba lokacin da matar take ovulation, ma'ana Kwan yayi girma sai ayi amfani da na'urar scanning a ɗauka. Ta Mara ake ɗauka bata al'aura ba, sai a haɗa a Laboratory (invitro fertilization). Idan anyi sa'a an samu fertilization sai a ɗauki abunda ake cewa fertilized ovum kamar guda biyu a sa a mahaifar matar wannan ta vagina ɗinta za'a saka sai a jira a gani idan dashen ya kama. Idan ban mantaba kuma na fahimci tambayarka wannan itace amsar”.
Sosai AK ke ɗan jinjina kansa yana taunar lip ɗinsa na ƙasa a hankali da haƙiri. “Okay Thanks. Next, za'a iya ɗaukar sperm daga wani ƙasa a kawo wani ƙasa batare daya lalace ba?. Misali kamar daga london zuwa Nigeria?”..
“Eh to Yayanmu za'a iya ɗaukar semen akai wani wuri, amma gaskiya yanada matuƙar wahala saboda sai an sashi a ma'adani na musamman (Google: transport sperm from one place to another). ba kowanne likita banema zai iya maka wannan juriyar kai tsaye”.
“Lallai kam. To amma za'a iya ɗaukar sperm ɗin namiji bada saninsaba aje a aikata dashen?”.
“Yayanmu idan na fahimceka kamar ace matarsa ta ɗauka a ɓoye bada saninsa ba? Dan ko likita sai dai ya saka a kawo, bawai ya ɗiba kai tsaye ba tunda ba kamar jini bane ko fitsari

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login