Showing 150001 words to 153000 words out of 237912 words
Chapter 51 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt
zuwa Gozarki. A Gozarki muka kwana dan maraice ya rufa lokacin. Washe gari tunda farar safiya muka tafi inda ake hawa mota muka shiga motar Katsina da naji ana faɗi a wajen. Nasha mamaki amma a raina ina ɗoki zanje katsina da nakeji a labari. Koda muka isa Katsina an saukemu a wani waje mai tarin jama'a, mudai muka shiɗa a motar kamar yanda tace mana. Daga nan an ɗibemu a napep zuwa wani waje da naji hajja Lanti ta kira da suna anguwar yari.
Kamar yanda ƴan uwan tafiyata basa gane komai a wannan tafiya nima dai ba ganewa nakeba. Sai dai ina lure da komai da akeyi. Kamar sunayen wajajen da muka sauka da inda muke tafiya. Mun isa anguwar yari da tace a kaimu. Inda aka saukemu a wani gida mai matsakaicin ƙyau da girma.
Koda muka shiga cikin gidan mun samu kusan mutane goma a cikinsa, Sai wata dattijuwar mata da tafi hajja Lanti shekaru dajin daɗi. Yanda ta tarbemu ne yasa naji ɗan dadi ga raina. Sai dai yanda maza da mata ke shiga da fita gidan baiminba a rai. Mun jima zaune suna hira kafin a kawo mana abinci muci, bayan mun koshi aka haɗamu da wata a gidan mai suna Sadiya. Itace ta kaimu wani ɗaki wai anan zamu zauna. Nidai kallon kowa nake da mamaki da tunanin mi mukazoyi nan? Miyasa Inna tace na biyo wannan matar nan batare da Baba ma ya sani ba?. Banda mai bani amsa, shiyyasa naja bakina na tsuke. Daga wannan lokaci ban sake ganin hajja Lanti ba a gidan, ban kawo komai a rainaba sai tunanin ko taje wani wajene ta dawo tazo mu dawo gida. Amma sai naji shiru har tsayin kwana biyu. Duk da ana bamu abinci muci mu ƙoshi, ga television muna kallo hakan baisa hankalina ya kwantaba, sai dai inajin tsoron na tambayi wani ina hajja Lanti take?. A randa muka cika kwanaki uku a gidan naga an kwashi abokan tafiyata su uku aka fita dasu a gidan, daga haka ban sake ganinsuba suma. Hankalina ya tashi na shiga yi musu kuka akan nidai su maidani garinmu, danni na ɗauka kodai ƴan yankan kai ne ma. Ranar naga ruwan masifa wajen matar nan, dan kamar zata dakani a turmi saboda masufar data dinga min. Dolena shanye kukana saboda tsoronta. Da maraice aka sake kwashe sauran abokan tafiyata su biyu da suka rage aka barni ni kaɗai sai waɗanda na samu a gidan. Ranarma nayi kuka har takaini gayin masassara.
Magani kawai suka bani nasha, daga haka babu wanda ya sake bi takaina, sai ma da daddare kusan ƙarfe takwas hajiyar tace a tasoni zamu fita. Ina jinta daga ɗaki danba barci nakeba, tunanin asibiti zata kaini yasa ban kawo komai a rainaba na tashi na fito bayan na saka hijjab ɗina. Tsaye na sameta a tsakar gida cikin gayu, na gaisheta jikina duk a sanyaye saboda zazzaɓi dake cina. Gaba tai na bita baya batare damin maganaba. Muna fitowa ƙofar gida muka iske mota mai ƙyau.
Motarnan muka shiga, gabana nata faɗuwa nidai inata tunanin lokacin yanke nawa kan yayi. Dan haka naita addu'a kala-kala ina sharar hawaye a ɓoye da roƙon gafarar babana a zuciya, a haka muka iso wata babbar anguwa dabansan sunantaba, sai dai yanda ko'ina ke ƙwanyar da hasken lantarki zai tabbatar maka da anguwar masu kuɗice. Katafaren gida mai blue gate aka buɗe mana muka shiga, kasancewar darene bazan iya banbance tsarin gidanba, sai dai lallai ya haɗu matuƙa. Koda muka fito a motar hajiya ce ta kama hannuna muka shiga ciki. Anan ne na sake tabbatar da gidan ya haɗu, masu shi kuma sunada kuɗi.
Waɗanda muka samu a falon ne sukai mana iso zuwa ciki bayan mun gaisa, an sake kaimu wani falon, inda muka zauna zaman jiran matar gidan. Munfi ƙarfin awa ɗaya zaune kafin ta fito, ƙyaƙyƙyawa ce sosai baƙa, daka ganta kaga bafulatanar bakatsiniya, dan ƙyawun nata ya fita sosai masha ALLAH. Sai da ta gama mana kallon tsaf kafin ta amsa mana gaisuwa tana sake ƙaremin kallo, cikin maganar daban ganeba hajiya tace, “Ranki ya daɗe ga wata ki duba ko zata iya, yau kwana uku da kawomin su daga wani ƙauye”.
Kallona ta sakeyi sama da ƙasa tana ɗan yamutsa fusaka. Ta ɗage kafaɗunta cike da isa tana faɗin, “Uhm babu laifi kam, dan tafi waccan komai, girma kawai waccan zata fita. Amma ina zuwa”. Tai maganar tana miƙewa, fita tai, babu jimawa sai gata ta dawo ɗauke da waya, batare da tayimana maganaba ta shiga haskani da hasken wayarta daban fahimci ma'anarsaba a wancan karon, sai dai a yanzu inaji a raina camara ne. Bayan ta gama kuma ta fara waya, da turanci take magana shiyyasa banji komaiba, bansan dai ga hajiya ba. Ta ɗauki lokaci mai tsaho tanayi kafin ta ajiye ta dubi hajiyar, “Ba damuwa zamu gwada mu gani, bara na ɗakko miki sauran saƙonki ko, idan akwai wani matsala zan nemiki daga baya kafin ki wuce, namafison sai mun kammala komai mun fara wucewa kafin taki tafiya”.
Baki a washe Hajiya tace, “Ato babu damuwa ranki ya daɗe, ni bani da matsala duk yanda kukeso sai ayi, fatana dai ALLAH yasa a dace akumayi nasara”.
Cike da yanga ta amsa da amin. Daga haka taje ta kawo mata saƙon da tace. Inaji ina gani hajiya ta miƙe tana faɗamin aini nan zata barni, nanne zanyi nawa aikin, dan haka sai nayi biyayya, yi nayi bari na bari.
Sosai na fara hawayen fili saɓanin na zuci, yanda zuciyata kemin zugi da zafi ya hanani yin magana harta fice ta tafi bayan ta bani ɗari biyar a kuɗin danaga an bata masu yawa, itama haijiyar gidan ta shige batare damin maganaba. Da wannan damar nai zaman kuka na kusan awa ɗaya kafin wata tazo cikin wanda muka fara tararwa a falon farko ta kama hannuna muka fice.
In taƙaita miki Granny tun daga ranar zazzaɓina ya ƙaru, inaga ganin yanda nake galabaita yasa Hajiyarnan ɗaukata a washe gari takaini wani asibiti mai ƙyau da alama na kuɗine. Anan aka bani gado. Sosai likitan yaytamin tambayoyi harnaji nama ƙosa dashi, amma na daure dan lafiyata nake nema ai. Kwanana shidda a asibitin nan na warke sarai aka sallamoni, sai dai kuma hajiya ta kaini wani gida ba nata da aka fara kainiba, naji tsoro sosai, dan can babu kowa sai wata dattijiwar mata mai suna Harirah.
Ɗaki guda aka bani a gidan, wanda yaji duka kayan more rayuwa, ni harma abin ya ban mamaki amma sai ban tambayaba tunda dai ance aiki nazoyi. Komai na nema ina samu a gidan, amma sai dai a tsorace nake, dan haka kawai na kasa yarda da sakin jiki da baba harirah, sai dai kullum sai ta shigo ɗakina ita ta sakani shan magungunana na asibiti da aka bani. Hajiyar kuma ban sake ganintaba sai bayan kwanaki sai gata. Cataimin na shirya muje asibiti likita ya sake dubani, ban kawo komai a raiba na shirya na bita zuciyata fal fargaba. Munje likita ya sakemin gwaje-gwaje, sai yace wai akwai wani ciwo dake damuna zasu ban magani. Daga wannan maganar aka kaini wani ɗaki, tunda akaimin wata allura ban sake sanin inda nakeba sai a gida. Ni kuma tunda na farka sai tsoro ya kamani ganin ko baba harirah ɗinma yanzu babu, sai wani gardi abin tsoro dake a waje. Hankalina ya tashi, da ƙyar na samu nai wanka nayi salla. ina idarwa na saka kayan danazo dasu daga gidan hajiyar farko da aka kaini, ALLAH ya taimakeni na silalo na fito daga gidan, ɗari biyar ɗin da hajiyar ta bani da zata tafi lokacin data kaini can gidan itace ta taimaka mani na koma Danya. Koda na koma kuma saina kasa bama kowa labarin abinda ya faru har Babana, duk da inason na faɗa masa kodan kalmar iskanci da Inna ke dangantani da shi sai dai inajin tsorone”.
Shiru hajiya iya kawai tai tana kallon Zinneerah kamar mai karanto komai akan fuskarta, sai dai wani irin tausayin yarinyar da ƙaunarta na sake shigarta. Dan yanda take bata labarin a nutse sai take ƙara godema ALLAH da samunta matsayin matar jikanta mafi soyuwa a ranta. Ta ɗan murmusa cike da basarwa tana faɗin, “Uhmm lallai dole ki kasa mantawa da birnin katsina. To amma ita hajiyar data kaiki gidan baki koma gidantaba bayan kin baro can?”.
“Wai Granny sokike na koma ta sake maidani, nifa wlhy haka kawai naji banason hajiyarnan data kaini asibiti, ta cika tsare gida da mulkin tsiya kamar sarki”.
A karon farko Hajiya iya tai dariya da juyawa tana kallon AK datun fara maganarta da Zinneerah ya shigo ɗakin, sai dai jin labarin da Zinneerah ta fara badawa ya sakashi dakatawa batare daya shigoba. Yanda ya kafe Zinneerah da idanu yana ma labarin nata fashin baƙi da nazartarsa yasa hajiya iya faɗin, “Amma baki taɓa gamo da maikama da wancan mutumin a katsina ɗinba?”.
Sai a lokacin Zinneerah ta farga da AK, duk da ta jima tanajin ƙamshinsa a hancinta bata kawo shi baneba. Kallo ɗaya tai masa tai saurin maida kanta ƙasa saboda yanda kwarjininsa ke cika mata idanu da zuciya. Cikin girgiza kai tace, “A'a Granny, anan na fara ganinsa nikam”.
“Inno bafa wasa nakeba”.
Da iya gaskiyarta tace, “Wlhy kuwa Granny”.
Hajiya iya zata sake magana AK ya katseta da faɗin, “Kin shirya ne na kaiki gidan Gwaggon?”. (mmn sadiq).
Tsaf hajiya iya ta fahimci dalilinsa na katseta, dan haka tai guntun murmushi da cewa, “Eh bara na kimtsa, ai hada Inno ma zamuje saimu barta acan dan da safe idan ALLAH ya kaimu zata dawo akwai inda zan turata”.
Baice komaiba sai duban Zinneerah ɗin datai ƙasa da kanta yaɗanyi, ya ɗauke idanunsa ya juya ya fice.
Binsa da kallo Zinneerah tayi, tana ganin ya fice ta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya da har sai da hajiya iya tai murmushi.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_________________________
*Page 47*
...........Cike da ɗokin zuwa ganin mmn sadiq dasu Aliyu Zinneerah ta shirya cikin wando da riga na parkistan red and white, sai gyale red data naɗa a kanta wanda ya fiddo mata ƙyawun da fuskrta ta ƙara. Kayan sun zauna mata ɗas a jiki kasancewarta mace mai mulmulallan jiki da ƙyawun surarta ta ƙuruciya. Babu wani kwalliya a fuskarta, amma ta saka lipstick kaɗan da yayma lips ɗinta ƙyau, dan tanada lips masu ƙyau da tsarinsu ya fita sosai yanda suke ɗaukar jambaki kamar wata babyn roba. Takalmi tasa mai ɗan tudu da igiya, sai side bag ɗinta ƙarama. A yanda tai ƙyau dolene ka kalleta ka sake kallo, ga ƙamshi tana bazawa dan Zinneerah gwanace wajen ɓarnar turare, idan ta samu batai masa da sauƙi. Ƴar jikkar data zuba kayanta kala biyu da tsarabar chocolates ɗin su Abdul ta ɗauka, dama hajiya iya ta fice ita tana falo tuni.
Hajiya iya kawai ta samu a falon itama tana ƙoƙarin fita, samarin gidan tun bayan breakfast suka fice, hakama ƴammatan, su Jamal kuwa batasan ina suka dosaba. Hajiya iya dake ƙoƙarin fita tace, “Inno kashe tvn nan ki taho nasan Moddibo nacan ya cika da hasahinmu”.
Da to Zinneerah ta amsa tana ɗaukar remote, bayan ta kashe tvn ta gyara labulolin sannan ta fito, ƙofar ta rufe dan masu aikin Hajiya iya basu dawoba, maybe sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Tafiya ta fara cikin nutauwarta tana ƙoƙarin ɗaura agogo data ɗakko a tsintsiyar hannunta da dosar inda ta hango Hajiya iya da Mommy tsaye da alama harda ita zasuje. Idonta bai lura da AK ba sai da tazo dab dasu tana ɗagowa da shi ta fara tozali yana ɓullowa daga ta gaban motar waya a kunnensa alamar magana yakeyi.
Kallon nata yayi dai-dai da saukar nasa idanun a kanta. A take ƴar sakewar data hango akan fuskar tasa ta ɓace ɓat, ya tsuke fuska yana mata kallon data nema kifawa saboda harɗewa da ƙafafunta suka shigayi. Saurin maida kanta tai ƙasa tana cigaba da takowa ranta fal nauyinsa da kwarjini, sai mita take a ranta kuwa. (Haka kawai bakama mutum komaiba yayta hararka, shi wai baya ganin waɗanan idanun nasa manya da ƙarfinsu yay yawa suna tsorata mutane).......
Da wannan tunanin ta ƙaraso Mommy dake kallonta tana ambaton, “Masha ALLAH ɗiyata irin wannan ƙyau haka”.
Ƙasa Zinneerah ta ƙarayi da kanta tana murmushi, hakama Hajiya iya murmushi take tana kallonta itama. A bazata sukaji AK ya saki tsaki, cikin faɗa-faɗa yace, “K! Koma kisa hijjab”.
Ba Zinneerah ba hatta su Mommy sai da suka dubesa, shiko ya fuske ya buɗe murfin motar ma a fusace ya shige abinsa. A sanyaye Zinneerah ta juya zata koma dan shi ba abin wasanta bane, waɗandama suka girmeta da shekaru masu yawa a gidan sunabin dukkan dokarsa balle ita ƴar jiya. Dakatar da ita Hajiya iya tayi ganin yanda tai ƙwalƙwal da idanu kamar zatai kuka, ta kamo hanunta tana matsawa saitin driver da yake zaune. “Haba Moddibo aimata haƙuri tunda ta rigada ta fito, ai kaga gyalen ya rufe mata jiki, kuma naga daga mota sai gida”.
Shiru yay kamar baiji mi Granny ta fadaba, sai da ta ƙara leƙasa tana faɗin, “Oh nima yarfin daka iya zakamin?”.
Idanunsa da suka canja launi ya ɗago ya dubi Hajiya iyan, “Amma Granny .......”
“Dan ALLAH ai nace”. Tai saurin katsesa dan tasan shegen taurin kansa da dagiya akan abinda duk ya kafama sharaɗi. Badan yasoba ya ɗauke kai daga kallonta yan yima motar key. Murmushi Hajiya iya tayi da duban Zinneerah. “Kinga zagaya can kusa dashi ki zauna Inno, mu saimu zauna baya da Mommynku”.
Kamar Zinneerah ta fasa ihu taji, dan yanda taga fuskarsa batai zaton ya haƙuraba, kawai dai yayi shirune dan Granny ɗin. Amma yata iya, dole ta zagaya tabi umarni. Zama tai maƙure jikin murfin mota, zuciyarta na mata hasashen ko ina little yake? Dan tayi tsammanin dashi zasuje itakam. Yanda AK ya figa motar da ɗan ƙarfi yasata saurin dubansa, sai dai da sauri ta ɗauke idonta ganin wani shegen harara daya watso mata laɓɓansa na motsawa tamkar mai magana komai son cewa wani abu amma ya gagara furtawa.
“Kai malam wlhy karka zubar damu, dan idan ka kasheni banga sake ganin ɗan inno ba ALLAH ya isa mai kishin tsiya”. Hajiya iya ta faɗa da iya gaskiyarta tana zazzagama AK masifa. Dariya Mommy ta sanya ganin yanda AK ɗin ya hararo Hajiya iya ta mirror.
Zinneerah kanta sai da zancen hajiya iya ya bata dariya, amma sai tai murmushi kawai tana kauda kanta gefe, dan zuwa yanzu ta fahimci Yayansu da Granny ba'a haɗuwa ba'ai faɗa ba. Kuma itace mai takalar faɗan shi kuma yayta mazurai, idan kuma ya magantu ya rama sau ɗaya yay mata banza.
A nutse yake tuƙin cike da ƙwarewa da bin dokoki, sai da suka hau titi sosai ya fara amsama Mommy maganar da take masa daga can baya, hajiya iya na tayata. Zinneerah dai bakinta gum, sai strawberry sweet ɗin dake bakinta take ta faman juyawa tana kallon hanya, tana jiran taji ya tambayeta ina suka dosa taga ya ɗau hanyar anguwar kai tsaye. Mamakine ya kamata sai dai babu damar magana, sunyi kusan rabin tafiya taga ya gangara dasu wani super market, sai da ya samu waje yay fakin sannan yay magana batare da ya kalli kowa a cikinsu ba. “Mommy muna zuwa Please”.
Cike dajin daɗi tace, “A fito lafiya”.
Hajiya iya kam baki ta taɓe da ɗauke kai tana maganar da su dake gaba ba jinta sukeba. “Muje”. Ya faɗa yana buɗe murfin ya fice. Zinneerah bata fahimci da ita yakeba sai da Mommy tace, “Ɗiyata fita kuje ku dawo kinji”.
Sai da Zinni taɗan waro idanunta waje, tace, “Mommy amma.....”
“Maza kije karyayi faɗa”.
Mommy ta katseta kafinma tace komai. Dole Zinneerah ta yunƙura ta fita zuciyarta na dukan goma-goma. Idanunta kuwa harsun tara ruwa. Ina ita ina shiga irin wannan wajen da Yayansu, itakam yau tana cikin abba-tuwa, shikenan ya samu damar dazai cimata uwa akan ƙin bin maganarsa na saka hijjab duk da Granny ce tai bell nata dai.
Koda ta fito da birkitattun idanunsa ta