Showing 204001 words to 207000 words out of 237912 words

Chapter 69 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt

27 Nov 2024

23426

canja sosai.
“Kin santa ne?”.
AK ya faɗa idonsa akan Zinneerah. Kanta ta shiga jinjina masa, kafin tace, “Itace Hajiyar nan ta katsina da aka kaini gidanta”.
“What!!” AK ya faɗa duk da kuwa dama aunty Zakiyya suke zargi.
Mammah da abun ya harzuƙata ta dakama Zinneerah tsawa. “K!! Shashasha daga ganinmu sai kice wani itace hajiyar da aka kaiki katsina wajenta. To aka kaiki kikai ubanmi acan?”.
Kafin Zinneerah tace wani abu AK yace, “Mammah kwantar da hankalinki Please. Inaga ai magana ta ƙare kawai. Khalipha kira Faisal kace ya kai matan nan gidan Baffah gamu nan zamu samesu acan”.
“Abdul-Mutallab banson iskanci, ya ana wata maganar kana ɗakko wata kuma?”.
“Nace ki kwantar da hankalinki Mammah, kumuje can gidan kawai, dan akan wannan sanin junan da sukai akwai magana”.
“Magana!?” Mammah ta faɗa tana kallon aunty Zakiyya da sai yanzu ta samu bakin cewa wani abu.
A firgice tace, “Magana! Dawa za'ai maganar?. Dan kawai ta kirani da hajiya sai kace wani akwai magana. Ke dan ubanki a inama kika sanni dazaki wani kirani da hajiya?”.
Mamaki ƙarara a fuskar Zinneerah tace, “Hajiya kin manta dani? Nicefa wadda wata hajiya Haule mai jiki ta taɓa kai miki har bani da lafiya kikaita kaini asibiti ana dubani, nikuma tsoro ya sani gudowa bayan na warke dan canake gidan yankan kai kika kaini”.
Zinneerah ta kara maganar kanta a ƙasa tana tuno komai a ranta tamkar yanzu yake faruwa.
Baki Zakiyya ta buɗe zata sake magana AK ya dakatar da ita. “Please kunga ya isa haka, kumuje can gidan tunda dama ai akwai maganar da akace za'ai bayan gama taron nan”.
Mammah ta kallesa, dan harga ALLAH ita tama kasa fahimtar ina suka dosa kai tsaye. Ta buɗe baki zatai magana sai ga Mahma data biyo bayansu, sallamar da tayi ya sakasu juyawa su duka suna kallonta.
Ganin yanda sukai cirko-cirko yasa Mahma faɗin, “Lafiya? Mike faruwa anan?”.
Mammah da dama magana ke bakinta tace, “Wlhy Addah nima da nake tare dasu anan na kasa fahimta, waifa muna shihowa gidan nan sai yarinyarnan mara kunya take kiran Zakiyya wai da hajiyar da aka kaita gidanta a katsina”. Tai maganar tana nuna Zinneerah da al'amarin masu ya ɗaurema kai itama. Dan harga ALLAH ita bataga wani abun tada jijiyar wuya anan ba. Daga ta nuna ta santa ai bai kai ya zama tashin hankaliba.....
Mahma data ɗauke kanta daga kallon Zinneerah da Mammah ke nuna mata ta maida ga AK, kai ya jinjina mata kawai. Hakan ya sata fara maganar data katsema Zinneerah tunanin da tatafi.
“Kunga duk a ajiye wannan shirmen nake ga. kuzo muje can gidan dama Kabeer ne ya kirani wai yanason magana damu akan Adilah”.
Tuni Mammah ta saki batun aunty Zakiyya da Zinneerah ta maida hankalinta ga Mahma wajen faɗin, “What!. Mi kuma yake nufi da zancen Adilah? To wlhy Addah wannan karon duk abinda zanyi karki tsayar dani, dan dama yau-yau ɗinnan nai niyyar zuwa har gidan na tarkatota itama gobe zamu wuce Morocco”.
Mahma ma nuna ɓacin ranta tai ta hanyar cewa, “Nima ai shiyyasa na biyoku nan ɗin, dan a wannan karon ba ɗagama Kabeer ƙafa zanyiba kuwa koda na mintuna ɗaya ne. Ku muje can, idan an gama mazo ayi wannan batun nasu Zakiyya ɗin”.
Kafinma Mahma ta rufe baki Mammah takai ƙofar fita, aunty Zakiyya da gaba ɗaya take a harmutse tai saurin fara magana cikin borin kunya. “Kuje, ni dai zan wuce katsina idan kun gama kwa sameni acan”.
AK daya saki wani murmushin mugunta yace, “Ai hardake za'aje hajjaju, dan maganace data shafi family, idan kuma kin fidda kanki a cikinmu sai muji”.
Wani shegen kallo ta bisa da shi mai kama da ruɗani da tsana, ta buɗe baki zatai magana Mahma ta katseta. “Kunga nifa banason wannan fitinar taku, ke Zakiyya wuce muje, da an gama maganar ai baki ɗaya zamu wuce komai dare”.
Badan Zakiyya taso ba tabisu, Farah dai ko motsi bataiba dan da ido AK yay mata gargaɗin tsayawa. Khalipha kuwa dama tuni ya fice shi da Little.
Sai da AK yaji fitar motarsu daga gidan sannan ya kalli Farah da Zinneerah ɗin. “Kuma kuje ku shirya zamu bisu”.
Jiki a sanyaye Zinneerah ta kaɗa masa kanta, sashenta ta nufa zuciyarta duk babu daɗi da abinda ya faru. Duk da dai tasan ita mai laifice kodan gudowar da tai bada sanin hajiya ba batai tunanin abin zaiyi girman haka ba tunda da ya wuce kusan shekara huɗu fa kenan.


Zinneerah na shigewa Farah tai saurin bin bayan AK, kusan a tare suka shiga falonsa. babu zaton tana biye da shi yaji ta rungumesa ta baya tana sakin kuka. Shiru yay kawai yana saurarenta dan yasan kukan mi takeyi, shi shaidane akan kishin Farah, amma yana ƙara hauhawane bisa karatun Mammah da Zakiyya.
Dalilin dayasa kuwa ta dawo gidan a yau Mahma ta sanar masa jiya ta zaunar da ita tai mata nasiha mai ratsa jiki, tare da tuna mata abubuwa masu yawan gaske waɗanda suka tada mata hankali, tun a daren tace zata taho nan gidan shine aunty Zakiyya ta rufeta da masifa. Ta ringa zaginta ta uwa ta uba daya kai har Farah kiran Abbansu ta sanar masa. Shine ya buƙaci ta haɗashi da Mahma suyi magana. Itako Mahma bata ɓoye masa komai dake faruwaba harma wanda su su Farah basu san ta saniba. Ya nuna matuƙar tashin hankali saboda shi mutumne nagartacce, ko zaman Farah a hannunsu dan anfi karfinsane kawai, amma duk sauran yayunta suna tare da shi sai dai irinsu Zakiyya da sukai aure. A yanzu hakama soyake yay murabus a ɗora babban yayansu Farah ɗin a karagar mulki. Zantukan da Mahma ta sanar masa ɗinne ya sashi sanar dasu yau zaizo kano, Farah kuma ta tabbatar ya sameta a gidan mijinta inba hakaba wlhy sai ya saka AK ya saketa saki uku, kuma ta dawo zaman Nigeria cikin masarauta.
Itako a duniya ta tsani zaman masarautarsu saboda yanda ake komai a takure, ga matan babansu sam basa ƙaunarsu saboda son da baban ke nuna musu a dalilin rashin mahaifiya. Dama can kuma yaso mahaifiyarsu sosai dan tunkan tabar duniya matan sun mugun tsanarta itama. Abu na biyu maganar sakin da yace zaisa AK ya mata. Tasan Abbansu sarai, wlhy zai iya sakawa AK ɗin ya saketa dan kaɗan daga aikinsa. Shima murɗaɗɗen mutumne mai tsayawa akan gaskiya duk ɗacinta.
A hankali AK ya janyeta daga jikinsa yana zagayo da ita gabansa. Ƙyawawan idanunsa masu cikar kamala da kwarjini ya zuba mata hannayenta duka biyu riƙe a cikin nasa. Sake fashe masa da kuka tayi kishinsa mai tsanani yana taso mata, amma tanata ƙoƙarin ganin ta danne dan duk runtsi bata iya rabuwa da shiba saboda tana sonshi.
Karan farko AK ya saki murmushi da kai hannu ya share mata hawayen dake sauka a fuskarta. “Nifa kinsan banason kuka ko?”. Ya faɗa yana rungumota jikinsa dan shima yanason kayarsa.
Ƙanƙamesa tai tana sake fashewa da wani kukan, “Dan ALLAH Yah Abdul-Mutallab kayi haƙuri wlhy Abbah zai iya rabamu, ka taimakeni karka faɗa masa na tuba”.
“Toni dama miya haɗamu da har zan sanar masa?”. Ya faɗa yana ɗago fuskarta. Cigaba yay da faɗin, “Kece kike biyema su Mammah ai dama, suna amfani dake wajen biyan buƙatunsu batare da kin fahimtaba. Sannan kina barin kishinki na rinjayar tunaninki bayan kinsan ina sonki. Sokike ne na dinga binki kamar wani sakarai dan kawai ki tabbatar ina sonki? Ko sokike nabar mahaifina da ƴan uwana dan kawai ina sonki Farah? Wannan abun shina dinga tsoratar miki dama. Randa zan iya ƙosawa da halayarki na fara tunanin ƙara aure. Iyayena da baki ragamawa suma su bani goyon bayan yin. Amma sai kika kasa fahimta, ke ga mai Mammah da aunty Zakiyya ko?. Gashi nan duk yanda nake ɓoyema Maimartaba halayyarki sai da takai kin tonama kanki asiri da kanki”.
“Na tuba wlhy, dan ALLAH ka taimaka karka faɗa masa yanzuma, dan wlhy yace yana hanyar zuwa kano. Na rantse yana tambayarka ka faɗa masa sai ya raba aurenmu kasan halinsa”.
“Idan kinmin alƙawarin zaki nutsu, ki komamin Farah dana sani a baya, mai tattalina da ƙaunata bazan faɗa masaba. Sannan duk abinda za'a tattauna a gidanmu yanzu zaki faɗi gaskiyar abinda kika sani bazan taɓa yarda a rabamuba koda kuwa zan hukuntaki da laifinki ne”.
Batare data nutsu ta tace zantukansa ba tace, “Na amince wlhy Yah Mutallab”.
Idanunsa ya ɗan lumshe ya buɗe a kanta, tare da sunbatar goshinta da laɓɓanta. A dai-dai lokacin da Zinneerah ta shigo falon da sallama, hannunta ɗauke da basket ɗin da Khalipha ya kawo musu breakfast. Dan harta fito saita tuna ko karyawa basuyiba. Shine tai tunanin kawo masa koshi zaici dan ita kam bazata iya shan ko shayi ba.
Wani irin bugawa ƙirjinta yayi, tai saurin ja da baya jikinta na rawa, dan shigowar tata yayi dai-dai da ɗaura lips ɗinsa akan na Farah, itako ta cafke tana kara rungumesa kamar yanda shima ya sake rungume abarsa.
Jin basket ɗin hannunta zai faɗi ya sakata saurin ajiyewa a ƙasa ta juya da sauri ta fita dama a farkon shigowa take.................✍




*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍




*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*


*_TYPING📲_*




*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 62*
________________________




*_KAƊAN YA RAGE SU ƘARE_*




*_MATA ƴan ƙwalisa kuna ina za'aci kasuwar sama babu ku?. Mg's skincare ɗin fa na gab da ƙarewar kaya kuna nan sake da baki baku mallaki naku ba_*




_Mg's SKINCARE nagartattun kayan ne dake gyara jiki da fata cikin sauƙi, sunada inganci da rahusa dai-dai da aljihunku._


*Da kin fito a ringa ga tauraruwar taurarin nan mai fatar da babu kamarta tamkar dinare abin haske da walwali.*


*_Sabulunsu kawai kika ɗana sai kinsan kin kai kuɗinki inda babu asara balle dana sani_*


_A yanzu haka muna jerin kayayyaki da suka rage kamar haka_👇🏻


Available


_Akwai: herbal whitening black soap 3k_
Akwai: beauty kit 11k shi set ne yakunshi Abu 6
Soap
Body cream
Face cream
Body nd face scrub
Cleanser
Glow oil


Location
kaduna buh mn tura Kaya ko Ina saidai inmutum ya amshi kayanshi zebada kudin delivery


WhatsApp 08062991549
Call 08064532391


Instagram:glow_with_mgs


Facebook:mg's skincare


*_Karku bari ayi babu ku guys, siyan nagari maida kuɗi gida._*


________________________




*Page 62*


.........Kawai jitai hawaye sun ɓalle mata babu gaira babu dalili, ta zube a farkon kujerar shiga falonta na farko ta cigaba da zirarwa batare datayi yunƙurin sharesuba ko sau ɗaya. Har cikin ranta tanajin nadamar shigar masa ɗaki kai tsaye ba tare da jiran izini ba, sai dai ALLAH shine shaidarta batai tunanin matarsa na cikiba, dan duk tunaninta sashenta itama ta nufa.
Zumbur ta miƙe da saka bakin gyalenta tana share hawayenta saboda jin takun tahowarsa, tai saurin nufar ƙofar itama dan bata buƙatar ma ya shigo ya sameta. Kusan cin karo sukai yaja da baya itama taja tana ambaton, “Sorry bansan ka tahoba”.
Yanda yaji muryarta a shaƙene ya sakashi kallonta da ƙyau batare da ya amsaba. Abinda kawai zuciyarsa ta bashi akan maganarsu aunty Zakiyya ne, dan haka ƙarasa shigowa da jawota jikinsa kawai yay ya rungume. Wani irin sabon kuka ne taji ya taho mata dan haka ta sakeshi dan duk yanda taso riƙesa ta kasa. Ba komai ya sata gagara riƙewarba kuma sai ƙamshin turaren aunty Farah da taji jikinsa nayi. Ƙoƙarin janye jikinta tayi ba tare da shi ya ɗagotaba. Tai saurin nufar ƙofar fita tana share hawayen da mayafinta.
Da mamaki yaɗan bita da kallo zuciyarsa na raya masa ‘Anya kuwa zancen su aunty Zakiyyar ne kawai. Dan idan bai mantaba yaga basket a ƙofar falonsa da ƙamshin turarenta. Kafin ya shigo nan din yayi tunanin ko Khalipha ne daya shiga ɗazu ya ajiye dan lokacin da yazo a bedroom ya samesa, kamshin turarenta kuma ya barsa akan kawai dan ya shaƙane sanda suna tare a falon.
Kansa kawai ya ɗan girgiza dayin murmushi, a kan laɓɓansa ya furta, ‘Oh mata kenan’ dan yanzu ya gama da Farah itama, koda ya rakata mota ma ya bartane tana kukan.
Bayan Zinneerah ɗin ya bi, sai ya isketa a general falo tsaye. Tana ganin fitowarsa tai saurin ficewa baki ɗaya kuma. ‘Tofa babbar magana’ ya faɗa a fili murmushi na suɓuce masa.
Shi ya rufe ƙofar sannan ya iso wajen motar inda Zinneerah tai tsaye bata shigaba. Fuskarsa ya daidaita da ƙyau yana isowa, batare daya kalletaba yace, “Shiga muje”. Yay maganar yana buɗe mata baya. Ganin yanda yay kicin-kicin da fuska dama kuma ba wasan yake da itaba yasata shiga babu musu, sai da ta zauna ya gyara mata mayafinta daya fito sannan ya zagaya ya shiga shima mazaunin driver, Farah na gefensa itama ta cika tai fam.
Har zai sama motar key sai ya fasa, Kallon Farah yay sannan ya juya ya ɗan kalli Zinneerah. “Kun gaisa da juna?”. Ya faɗa a dake.
Kusan a tare sukace masa a'a. Sai Zinneerah kuma tace, “Aunty Ina kwana”. Kamar Farah zata share saita motsa laɓɓanta ciki-ciki tace, “Lafiya” saboda hararan da AK ya zubo mata.
Daga haka motar ta ɗauka shiru. Shima bai sake cewa komaiba yay mata key da harbata gaban gate. Ficewa yay kai tsaye dan dama maigadi ya buɗe masa tun ganin sun fito sun shiga.


Shaiɗan ɗin daya fahimci yana kai kawo a zukatan matan nasa ya sakashi saka karatun alkur'ani a motar, a ransa yana nema musu sassauci ga ALLAH dan shima yasan zafin kishi tunda yana dashi. Lokaci-lokaci yakan kalli Farah ya duba Zinneerah kuma ta mirror. Ganin yanda duk suka maida fuskoki gefe sai suka bashi dariya amma ya gimtse baiyi a fili ba sai a ransa. Harko suka iso gidan nasu daga Farah har Zinneerah babu wanda yayi ko tari. Bayan ya gaisa da maigadi ya ida shiga cikin gidan ransa fal mamakin ganin motoci da yawa a harabar gidan kamar har yanzu bikin sukeyi basu gamaba danma babbace.
Babu wacce ta motsa a cikinsu, dan haka shima sai bai tanka musuba ya buɗe motar ya fita. Ganin haka yasa suma duk suka fito kusan lokaci guda. Kallon juna sukai, sai kuma kowacce ta ɗauke kanta. Farah tazo ta gitta Zinneerah ɗin tanabin bayan AK da yay gaba abinsa ya barsu a wajen, dan harga ALLAH idan ya cigaba da zama yana kallonsu dariya zata iya kufce masa. Dan tsaf ya fahimci itama Zinneerah ɗin A ce a fannin kishi kenan. Koba komai kishin nata a karo na biyu ya tabbatar masa da shima ya samu karɓuwa a gareta, miskilancine kawai ya hana ta bayyana kamar yanda ya buƙata.
Sashen Hajiya iya suka nufa kai tsaye, inda sukaci karo da tarin takalma kala-kala ajiye, da alama baƙin da suka tara waɗan nan motocin duk sune anan ɗin.
Cikin nutsuwarsa da sallama ɗauke a bakinsa ya shiga, Farah na biye dashi Zinneerah a bayanta. Da sauri Farah ta nema komawa da baya saboda cin karo da fuskar mahaifinta da tai hakimce cikin kujera. AK yay saurin riƙo hannunta yana magana ƙasa-ƙasa. “Malama ki nutsu mana” Ya faɗa yana duban Zinneerah datai musu kallo ɗaya ta ɗauke idonta.
Kai Farah ta ɗaga masa idanunta cike da ƙwalla. Ya nuna musu hanya alamar su wuce. Babu musu suka nufi ƙarasawa cikin falon ran Farah fal mamakin zuwan Abban nata babu dogari ko ɗaya, sai ƙannensa biyu Matawalle da waziri, da babban amininsa da kowa ya sansu tare wanda ƙanine a wajensa shima amma kusan tare sukai rayuwarsu, sai dai ba mahaifinsu ɗaya ba.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login