Showing 201001 words to 204000 words out of 237912 words
Chapter 68 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt
Abinda kuma sukazo dashi sai faman ci suke har Inna ɗin dan tace raba mugu da makami ibada ne.. (😂🤣gaskiya kam aunty Asabe)
Shi Baba ma da amaryarsa dake jiyosu daga ƙofar ɗaki dariya suka basu, musamman Inna da baba yasan shegen kwaɗayinta bazai barta ta kasa cin abinda akazo da shi dinba koda kuwa tanaci tana kuka ne.
Washe gari da safe jikin Tinene ya ƙara tsananta, tun dare taketa kwara amai har safiya ta tashi a galabaice. Baba ya ce ta shirya suje asibi maybe dai typhoid ne ke damunta, dan itace kesa zazzaɓi mai zafi haka da naci. Amaryar baba ba sanin ciki tai ba sosai, Inna kuma idanunta ya rufe da damuwar ɗaukakar Zinneerah sam taƙi fahimtar halin da Tinene ke ciki. Su kuma su Karima tsoron faɗar abinda ransu ke raya musu inna ta hau tsinarsu sukeyi.
Ana haka sai ga Gwaggo Laritu tazo domin ai zaman raba alkairin da AK ya basu, bata jima da zama ba Yaya Gajeje ta iso itama. Cikinsu babu wanda yay magana akan shirin kai Tinene asibiti da baba ke shirin yi. Sai da Gwaggo Laritu tai wani tunani sannan tai magana.
“Niko Yaya nakega kai Tinene asibiti bazai jawo komai a garin nanba sai kace nace. Musamman ma daya kasance asibitin garin nan zakuje”.
Da mamaki baba yace, “Kace nace kuma Laritu, akan ciwon?”.
“Tabbas kuwa Yaya, dan banga amfanin aita ɓoye-ɓoye ba akan abinda kowa yasan dama wajib ne. Dan shi dai sharri ɗan aike ne dama shiyyasa ake nusar damu illarsa ga aikama kowa. Asabe tama Zinneerah fata kuma ALLAH ya karɓa mata, sai dai kuma ga sakamakon nan ya dawo ga Tinene. Dan babu wani taifot dake damunta ciki ne jikin wannan yarinyar wlhy”.
Ba baba da amaryarsaba hatta da Inna dake jiran Gwaggo Laritu takai ƙarshe ta sauke mata kwandunan bala'in da take Tattarowa a take ta saki robar ruwan wankan ƴar Karima data ɗauka zata sako ruwan zafi, ALLAH yasotama bata kai ga zubawarba.
Wani irin shuuu taji abu ya gitta mata cikin idanu da ƙwaƙwalwa saboda tsabar razani. Cikin rawar baki tace, “Munahika annamimiya, Laritu kirasa wanda zakima wannan sherin sai ɗiyar zumunki. To wlhy sai dai kiga ciki a jikin jikokinki, ALLAH ya isa kuma sherin da kikaima yarinyata”.
Murmushi kawai Gwaggo Laritu tayi. amma uffan bata sake cewa ba. sai Yaya Gajeje ce tace, “Inna ya kamata ki fahimci zancen Gwaggo, ku kuma nutsu wajen karantar Tinene wlhy cikine da yarinyar nan da gaske”.
Baki sake tabi Gajeje da kallo, sai jitai Atine tace, “Wlhy Inna da gaske ne, ki kalla Tinene da ƙyau zaki tabbatar”.
Tsitt gidan yayi saboda kakarin aman Tinene, Inna ta fashe da kuka jikinta na wani irin rawa lokacin da idonta ya sauka akan Tinene da har ciki ya fara tasawa sama kaɗan, da alama ma ya wuce watannin da suke hasashensa. Baba kansa baya yay sai da amaryarsa ta riƙosa jikinta na rawa itama dan batason damuwa sam, musamman ma yanzu data samu cikin nan. Kafin wani ya samu damar sake cewa uffan sukaji ana rangaɗa sallama daga waje. Da ƙyar baba ya iya amsawa da nufar hanyar ƙofar gidan domin duba wanene. Da Laminu ƙanin Babawo yaci karo, Laminu ya gaishesa da girmamawa yana miƙa masa takardar hannunsa da nuna masa kayan daya sauke a mashin ƙasa. “Baba Sule gashi inji Yayana Babawo, yace a bama Karima tare da waɗan nan kayan. Yace a sanar mata ta tuna yau saura sati biyu wa'adin da kotu ta bata na kai kuɗin sarƙar hajiyar data satamawa ya cika”.
Cikin rashin fahimta baba yace, “Laminu ban fahimcekaba nikam sam, amma kaga shigo daga ciki kai bayani agaban Karimar”.
Babu musu kuwa yabi baba ciki, bayanin daya zayyana masa shiya sake maimaitawa Karima.
Gani kawai sukai ta saki ƴar sai da Atine tai azamar tarota tana ambaton, “Na shiga uku Karima baki da hankaline?”.
Ina Karima ba saurarenta takeba, dan atakema gani sukai ta yanke jiki ta faɗi, Inna ma da tun fara bayanin garin ke juya mata da wata irin hajijiya sai tabi bayan Karima ta zube ƙasa.
Ƙarar da Atine da Sa'a suka ƙwalla na firgici ya saka amaryar baba dafe bango saboda wani irin murɗawa da mararta tayi alamar tahowar naƙuda.........
____________________
*_KANO_*
Bayan wucewar su mmn Halima
salla kawai Zinneerah ta samu tayi ta la'asar. Duk yanda taso daurewa da zazzaɓin daya rufeta kasawa tai, dole ta rrrafa saman gado ta kwanta dajan bargo ta lulluɓe tana rawar ɗari.
Cikin barcin daya ɗan fara figarta little ya faɗo mata a jiki yana faɗin, “Aunty!” cike da farin cikin ganinta. Buɗe idanu tayi da ƙyar tana kallon ƙyaƙyƙyawar fuskar yaron mai tsananin kama da mahaifinsa. Ta ɗan lumshe ta buɗe da ciro hannunta a bargon da ƙyar ta shafa kansa.
“Kaga ka tadani daga ɗan barcin dana fara sweetheart, waye ya kawoka?”.
“Abbana”.
Ya bata amsa kansa tsaye yana ƙara daka tsalle akanta.
“Wai ALLAH little karka ƙarasani dan ALLAH, ka tausaya mani”. Ta faɗa tana yunƙurin miƙewa zaune. Idontane suka sauka akan AK dake bakin ƙifa tsaye kawai yana binsu da kallo tamkar ya samu television.
“Barka da dawowa” tai maganar da maida idonta ƙasa. Batare daya amsaba ya tako ciki sosai, a kusa da ita ya zauna da kamo little dake ɗane mata wuya...........✍
*_Na gode da addu'oinku, na samu sauki Alhmdllh. Asha hutun weekend lafiya😘😍😍_*
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 61*
________________________
*_KAƊAN YA RAGE SU ƘARE_*
*_MATA ƴan ƙwalisa kuna ina za'aci kasuwar sama babu ku?. Mg's skincare ɗin fa na gab da ƙarewar kaya kuna nan sake da baki baku mallaki naku ba_*
_Mg's SKINCARE nagartattun kayan ne dake gyara jiki da fata cikin sauƙi, sunada inganci da rahusa dai-dai da aljihunku._
*Da kin fito a ringa ga tauraruwar taurarin nan mai fatar da babu kamarta tamkar dinare abin haske da walwali.*
*_Sabulunsu kawai kika ɗana sai kinsan kin kai kuɗinki inda babu asara balle dana sani_*
_A yanzu haka muna jerin kayayyaki da suka rage kamar haka_👇🏻
Available
_Akwai: herbal whitening black soap 3k_
Akwai: beauty kit 11k shi set ne yakunshi Abu 6
Soap
Body cream
Face cream
Body nd face scrub
Cleanser
Glow oil
Location
kaduna buh mn tura Kaya ko Ina saidai inmutum ya amshi kayanshi zebada kudin delivery
WhatsApp 08062991549
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
*_Karku bari ayi babu ku guys, siyan nagari maida kuɗi gida._*
________________________
*Page 61*
.............Hannunsa yasa a wuyanta bayan ya sauke little ɗin yana lallashi dan kuka yake nemanyi dan an saukesa a wuyan mamansa.
Tsatstsare ta da idanunsa masu tarin kwarjini yayi, cikin kulawa yace, “Zazzaɓin dai har yanzun?”.
Kanta taɗan jinjina masa batare data kallesaba. A mamakinsu sai gani sukai shima little dake jikinsa ya saka hannu a wuyanta kamar yanda AK yayi, yakuma kwaikwayi zancen daya faɗa. “Zazzaɓine har yanju?”.
Kallon juna sukai suka saki murmushi lokaci guda haƙoransu na bayyana a waje. dan yanda yaron yayi maganar cikin serious dolene kai dariya. Shiko da yayi ko'a jikinsa, dan saima ya miƙe saman gadon ya hau tsallensa.
AK daya samu ya danne dariyarsa da ƙyar sai murmushi ya kamo hannun Zinneerah daketa faman kare bakinta dan da gaske dariyar ke cinta itama amma dai taƙi yarda tayi sai murmushi. “Yaron nan wayonsa yayi yawa, minene sirrin?”.
Ƙoƙarin shanye dariyarta tai da faɗin, “Kawai dai danya tashi cikin yarane”.
“Uhmyim, su Sadiq sun iya raino kenan?”.
Ɗan kallonsa tai mamaki sosai a fuskarta, a tunaninta ina yasan su sadiq har haka. Murmushi yay mata cike da basarwa ya miƙe. Batare daya ƙara cewa komaiba ya fita a ɗakin, ajiyar zuciya kawai ta sauke da juyawa ta kalli little dake cigaba da tsalle-tsallensa hankali kwance. Sai kawai ta yaye bargon ta sauka baki ɗaya duk da kuwa dai tanajin zazzaɓin har yanzun.
Bata sake ganin AK ba sai da akai magriba, ta idar da salla kenan tana ninke sallaya, little na gefe zaune yana raira kukan makesa da tai saboda ɓarna da yake neman mata a mirror ta hanashi yaƙi hanuwa AK ya shigo. Kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa yana maidawa ga little ɗin. Wajensa ya nufa, ya kamashi ya ɗaga jikinsa yana murmushi, “Wai mi akaima sojan nan ne?”.
Zinneerah little ɗin dake cigaba da kukansa ya nuna. AK ya kalli Zinneerah ɗin shima, “Mami mi mukayi haka aka samu kuka?”.
Ɗan kallonsu tayi tana harar little ɗin, cikin muryarta datai sanyi saboda zazzaɓin da takeji tace, “Ɓarna zaimin nace ya bari yaƙiji shiyyasa na make hannun”.
Hannu yasa yana sharema little ɗin hawayen, “Handsome babu ƙyau a hana mutum abu ya ƙi bari, kaga Mami bata da lafiya ma uhmyim?. Ce mata sorry”. Yay maganar yana matsawa gabanta.
“Mami Shoyi”. Little ya faɗa jin AK ɗin ya kirata Mami.
Ɗan hararsa ta ƙarayi ta ɗauke kanta kawai. AK ya riƙo hannunta, dole ta sake ɗagowa ta dubesu. Sai dai narkakken kallon da yake mata yasata janye idanunta. Batare da ya damu da yanda tayinba yace, “Ai munce ayi haƙuri ko”.
“Nima na haƙura ai, zanje na kwantane sanyi nakeji Yayanmu”.
“A'a ba kwanciya zakiyiba, shirya asibiti zamuje”.
Kanta ta jinjina masa, dama jikinta doguwar riga ce da hijjab. Dan haka sai kawai taɗan ƙara turare a jikinta tabi bayansu dan shi harya fice ɗauke da little.
A general falo ta iskesu, batare da yayi maganaba ya nuna mata hanya alamar suje. Gaba tai ya bita a baya ɗauke da ɗansa. Shine ya rufe ƙofar sannan suka ƙarasa ga mota. Ganin little kamar zai takurasa a wajen tuƙin yasata miƙa masa hannu alamar yazo wajenta, amma sai ya noke.
Baki ta taɓe da hararsa ta ɗauke kanta. Sai da ya tada motar suka fice a gidan yay magana batare daya kalletaba. “Nikam wannan harar ɗan akemawa ko baban? Tunda shima mai laifine?”.
Gefe tai da kanta tana murmushi da faɗin, “Kai Yayanmu ni dai wlhy banceba”.
Shima murmushin yayi da sumbatar kan little dake cinyarsa suna tuƙin tare. Daga haka ya maida hankalinsa a tuƙinsa itako ta lafe cikin kujera ta lumshe idanu.
Sun isa Shira hospital inda suka samu ƙyaƙyƙyawar tarba ga ma'aikatan. Anata kallonsu cike da sha'awa da birgewa. Yayinda suke nuna son ɗaukar little amma sai yaƙi yana dai maƙale da babansa. A office ɗin Dr Mahmud suka yada zango, shima ya tarbesu cike da murna da girmamawa yanata tsokanar Zinneerah. Yayinda ya ɗauka little kuma da ƙyar.
“Ranka ya daɗe kune da dare haka? Lafiya dai ko?”.
“To da sauƙi dai madam ce babu lafiya”. AK ya faɗa yana duban Zinneerah da kanta ke ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.
“ALLAH ya ƙara lafiya, Ko gajiyar biki ce ƙanwarmu?”.
Murmushi kawai tai batace komaiba. Shima sai ya murmusa da mikama AK little. Kafin ya maida hankali wajen mata tambayoyi. Magunguna kawai ya rubuta musu yay kiran wata Nurse a waya ya bata ta sayo. Ganin an kira isha'i suka fita salla suka barta a office ɗin. Suna dawowa ko zama basuyiba AK yace ta tashi suwuce kar dare yayi.
Har wajen motarsu Dr Mahmud yayo musu rakiya, sai da yaga tafiyarsu sannan ya koma ciki.
Daga asibiti AK wani shagon sai da wayoyi ya kaisu, a mota ya barta suka shiga ciki shi da little. Babu jimawa kuwa sai gasu sun dawo ɗauke da leda. Daga haka gida suka nufa bayan ya sake tsayawa ya sai musu gasashshen kifi.
Sosai Zinneerah kejin barci lokacin da suka shigo gidan, fahimtar hakan da AK yayi ya sakashi dakatar da ita a falon farko na sashenta. Tsareta yay sukai zaman cin kifin tare, bama wani sosai taciba dan bakinta babu daɗi. Ya bata magungunanta ta sha taɗan tattare wajen ta shige. Shima sashensa ya nufa da little. Acan yay masa wanka, sai dai babu kayansa kuma balle na barci. Shaf yama manta da batun amso masa kaya. Pant dinsa kawai ya maida masa ya kwantar dashi a gadonsa dan sai hamma yake. Shima shirin barcin yayi sannan ya nufi sashen zinneerah. Isketa da yay har tayi barci ya sashi fitowa ya dawo sashensa. little ya ɗauka yaje can shima kawai suka saka yaronsu tsakkiya.
Zinneerah batasan da zamansu a ɗakin ba sai da asuba data farka, dan ta rigashi tashi. Ta jima tana kallonsa shi da little zuciyarta fal saƙe-saƙe iri-iri. daga ƙarshe dai ta mike ta shiga toilet. AK da shima ya jima da farkawa ya bata damar cigaba da kallon nasune tana shigewa ya miƙe. A bakin gadon ya zauna harta fito sanann. Ɗan kallonta yayi yana lumshe ido, muryarsa a dasashe irin ta wanda ya tashi barci yace, “Naje massallaci”.
Tace, “A dawo lafiya”.
__________________
AK bai dawo gidan ba sai da rana tai ɗan haske. Ya shigo ya iske Zinneerah nata aikin kimtsa gidan kamar ba itace mara lafiyaba. Har ƙasa takai ta gaidashi. Ya amsa mata da kulawa yana tambayarta yaya jikinta. “Alhmdllh naji sauƙi ai”. Ta faɗa a hankali.
“Masha ALLAH”. Shima ya amsa mata kafin yace, “Ina little?”. “Bai tashiba har yanzun”. “Okay bara to na watsa ruwa dan inason fita da wuri”.
Kanta kawai ta jinjina masa. shi kuma ya juya zuwa sashen sa inda ta fara gyarowa duk da ba wani datti baneba.
Tana kammalawa bedroom ta koma tai wanka. Kammala shiryawarta kenan little ya farka. Wankan shima tai masa, ta shafa masa mai tana tunanin yanda za'ayi akan kayan da zaisa.. A dai-dai lokacin ta jiyo ƙarar doorbell. Little ɗin ta sauke daga kujerar mirror da yake a tsaye tana faɗin. “Ka jirani, idan wani abuna yay motsi anan kaima saina motsa maka jikinka da duka”. Daga haka ta ɗauka gyale ta fice.
Khalipha ne da kansa ɗauke da kayan little da breakfast ɗinsu. Ta matsa ta bashi hanya tana gaishesa. Cike da fara'a ya amsa mata idonsa akan little da batasan ya biyo bayantaba. “Uhm my boy ashe anan ka kwana?”. Ya faɗa yana mika mata basket ɗin ya ɗauka little daya nufosa baki a washe. Dan shi indai mazane to baya jimawa yake sabo dasu. Shiyyasa ko a gidan da wuri ya gama haddace samarin gidan. Kai tsaye sashen AK ya nufa abinsa. Itama sai tai ƙoƙarin juyawa nata sashen.
Kamar jira tana shiga aka sake danna doorbell ɗin. Sake dawowa tai zata buɗe taci karo da Khalipha ya fito shima. Barinsa tai ya ƙarasa ita kuma ta tsaya jiran ganin wanene?.
Farah ce ta fara shigowa idanunta jajur alamar tasha kuka. Sai Aunty Zakiyya a bayanta, Mammah na biye dasu. Ba karamin bugawa zuciyar Zinneerah tayiba da cin karo da Farah, tai wani diri-diri da ita dan koba komai dole taji hakan tunda ta aure mata miji. Jin muryar Mammah datai ya sata sake duban bayan Farah ɗin duk da kuwa sau ɗaya ta taɓa ganin Mammah ɗin.
Wani irin mahaukacin bugu ƙirjin Zinneerah yayi ta zabura baya batare data saniba. Wani irin duban aunty Zakiyya da itama ɗin dai ita take kallo takeyi baki a hangame.
Har abada bazata manta da wannan fuskarba. Koda shakara ashirin tai kuwa balle uku kacal. “H....h...hajiya?!”.
Zinneerah ta faɗa cikin rawar baki matuƙa. Wanda hakan yay dai-dai da fitowar AK da yasan da zuwan su Mammah ɗin a yanzu-yanzu da Mahma ta kirasa take sanar masa nan suka taho batare da sanintaba. Yayi duk yanda zaiyi karya bari Zinneerah ta haɗu dasu. Sai dai kuma hakan bai yuwuba tunda aikin gama ya gama.
Ba shi da Khalipha ba, hatta Mammah da Farah kallon Zakiyya suke da mamaki ganin yanda tai wani diri-diri tana kallon Zinneerah ɗin itama. Dan da hasashe kawai take, amma muryar Zinneerah ɗin ta tabbatar mata da eh lallai itace duk da ta ƙara girma ta kuma