Showing 111001 words to 114000 words out of 237912 words
Chapter 38 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt
fitaba ganin har wannan lokacin bai fitoba. Bayan kuma nasansa shi baya saɓa lokaci”.
Kallonsa ya maida ga Hajiya Iyan tare da jan kujerar kusa da ita ya zauna. “Yau meeting kawai nake da shi Granny shiyyasa na koma barci bayan sallar asuba. Ina fatan kin tashi lafiya?”.
“Lafiya lau na tashi, sai dai waɗanan akkunayen da suka cikani da surutu jiya”.
“Ai kece kika gayyatosu”. Ya bata amsa idonsa na sauka akan Zinneerah dake facing kujerar daya zauna. Tun zuwansa wajen tai ƙasa da kanta tana juya cokalin hannunta cikin abincin da sam ba daɗi yake mataba, wai a hakanma sai da Khalipha ya zaɓo musu wanda yasan zasu iyaci suji daɗinsa tunda ba sabawa sukai da abincin nan ba.
Janye idanun yayi cike da basarwa yana ɗaukar tea ɗin Hajiya iya ya fara sha. Hakanne ya bama Jamal damar fara gaidashi. Sai Meenal ma ta gaisheshi. Itama Bahijja haka. Zinneerah ce ƙarshen gaishesan batare data yarda ta kalli inda yakeba.
Dukansu amsa musu yay kamar yanda ya saba cike da rashin sakewa. Hakan da yayi yayma Farah dake bayansa tsaye daɗi, tai wani ƙasaitaccan murmushi da ɗora hannunta kan kafaɗarsa tana sake matsowa jikinsa. Cike da yanga da ƙasaita tace, “Za kaci wani abune anan ɗin?”.
“No, shayin Granny kawai ya isheni”. Daga haka ya maida hankalinsa kan hajiya iya ya fara magana ƙasa-ƙasa batare da kowansu yaji mi yake faɗa ba. Hakan kuma sai ya soki zuciyar Farah tabar wajen fuska a haɗe. Khalipha ya danne dariyarsa da ƙyar yana binta da kallo, tana gab da shigewa yace, “Kunga nikam bara na wuce school zanyi latti”.
Ɗagowa AK yayi ya dubesa. “No ka jira na kammala mu wuce tare kusa da school ɗinku zanje nima”. “Okay thanks you Yayanmu”. Khalipha ya faɗa yana jan kujerar data rage ta dining ɗin ya zauna.
Farah ko dake ƙoƙarin shigewa ɗakin jin zancen nasu ya sakata dakatawa. Kamar zata juyo sai kuma mita tuna oho mata ta cigaba da tafiya harta shige ɗakinta tana taunar lip ɗinta na ƙasa da ƙarfi.
Sosai zamansa shi da Khalipha a wajen ya saka Zinneerah shiga takura, garama Khalipha tana ɗan sakewa da shi. Amma wannan shugaban tsare gidan da ƙasaitar gaba ɗaya tare mata iska yake idan yana a waje. Sai dai kuma takan tsinci kanta cikin jin daɗi dan tana kallon little ɗinta tattare da shi. Yanzunma murmushi ta sake a bazata saboda faɗo mata a rai da Little yayi, dan hutun nan na kwanaki huɗu da tayi ba ƙaramin shaƙuwace ta sake shiga tsakaninta da yaron ba. Har takai tanajin kamar ta ɗakkosa su taho tare.
AK da sarai yaga murmushin nata ya ɗan kafeta da kallon sakanni a kaikaice ya ɗauke kansa, a ransa kuwa tambaya yake komi ya bata suga?. Baida mai bashi amsa dan haka ya miƙe dayin ɗan hugging Hajiya iya ta gefe ya sumbaci hannunta daya kamo. “Kimin addu'ar cin nasara, dan zamane mai muhimmanci zanje Granny”. Ya ƙare maganar idanunsa na faɗawa cikin na Zinneerah data ɗago a bazata. Yanda ya juya idanun da wani salo ya sakata saurin maida nata ƙasa ta risinar zuciyarta na matuƙar harbawa.
Kasancewar babu wanda ya lura da abinda ya faru suka rakashi da addu'ar samun nasara harsu Jamal. Zinneerah dai akan laɓɓa ta fisgo tata addu'ar da ƙyar ta furta. Hayanr fita ya nufa yana saka rigar sanyinsa a saman suit ɗinsa fuska ɗauke da wani ɓoyayyan munafikin murmushi.
Suna ficewa Zinneerah ta saki ajiyar zuciya. A take su Jamal duk suka kalleta. Hajiya iya kuwa ta saki wata ƴar dariyar data basu mamaki itama, sai dai koda suka maida dubansu gareta sai ta basar. Babu wanda ya sake magana dan dokace hakan ga Granny indai anacin abinci. Sai da suka gama ita dasu Bahijja suka gyara wajen domin taimakawa mai aikin da suke ganin kamar aikin gidan ya mata yawa saboda ƙaruwarsu.
Yau ma dai hirarsu suka sha tare da kakarsu. Daga ƙarshe Zinneerah ta bama Hajiya iya tsarabar mmn sadiq tare da saƙon zungureriyar wasiƙa da batasan ta micece ba itama. Hasalima sai yanzu da ake buɗe kayan duk suka gani. Jamal ya ɗauka zai buɗe Hajiya iya ta girgiza masa kai da amsa.
Babu musu ya bata. Koda ta amsa itama sai ta miƙe taje ta adanata dan tanaji a ranta abune mai muhimmanci a ciki mmn sadiq ɗin ta rubuto, dan dama ɗazun da sukai waya da Baffah yake sanar mata Abbansu Sadiq ya sanar masa yanason ya bashi lokaci zaije har gida suyi wata magana mai muhimmanci. Amma shi yanata juya abin a ransa da tunanin wace maganace haka? Shiyyasama ya sanar mata.
To a yanzu ganin wannan wasiƙar ya sakata jin maganar da Abban zai faɗama Baffah lallai tanada alaƙa da takardar kenan. Wannan hasashen ya sakata adana takardar sai ta nutsu sannan ta duba dan itama tayi karatun boko duk da bamai tsaho bane a wancan lokacin iyakartama firamare aji biyar aka aurar da ita...............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 33*
___________________
_*LAVENDER RESTAURANT..*_
_(Palace of mouthwatering food/delicacies)_
_IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_
_*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE.._*
_*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.._*
_*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283 akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021 to 3/10/2021 Nigeria @ 61_*
_*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU._*
_*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN. _*
_*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇🏾RIGIJI GABJI_*
_*Nigeria @ 61 _*
_*COOKING COMPETITION!!!_*
_*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine da wasu prize suma saura kuwa zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar_*
_*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA_*
____________________
*Page 33*
............A ɓangaren Farah kuwa tabbas a cikin tsananin tashin hankali take. Tana ƙoƙarin dannewa ne kar a samu matsala. Amma lallai zuwan waɗannan yaran gidan nan bazai haifar da ɗa mai ido a gareta ba, dan bawai zuwan nasu bane kaɗai matsalarta. Wannan itace dai-dai gaɓar da zata nisanci gidan nata da mijin ma ta koma zaman Morocco saboda killace ɓoyayyen sirrinsu, dama shirin yanda zasu saka AK maida Hajiya iya Nigeria sukeyi da zaran Mammah ta dawo daga China, sai gashi kuma wasu sun ƙaru. Gashi batama san iya adadin kwanakin da zasuyi ba. bata kuma san randa itama Mammah zata dawo ba.
A take hawaye masu zafi suka silalo mata. Ta jawo wayarta domin ƙara gwada kiran Aunty Zakiyya. Tun jiya take nemanta amma wayan yaƙi tafiya. Ta tura mata saƙo babu reply. Yanzunma dai switch off.
‘Na shiga uku ni Farah, aunty ina kika shigane dan ALLAH?’. Ta faɗa a fili hankalinta na sake tashi. Har zatai wurgi da wayar sai wani tunani yazo mata. Cikin hanzari ta shiga fara neman babbar ɗiyar aunty Zakiyya. Cikin sa'a kuwa sai ga tata ta shiga. A take bakinta ya washe da murmushi, taja wani dogon numfashi ta fesar da ƙarfi.
Ana ɗaga wayar ko amsa sallamar yarinyar batayiba tace, “Ameera ina aunty?”.
Cike da shagwaɓa Ameera tace, “Aunty tana ɗaki, yanzu suka dawo daga Niger ita da Daddy”.
“Niger kuma? Kinga kaimata wayar”.
Ameera ta nufi ɗakin mamanta tana cigaba dama Farah surutun da ba fahimta takeba sam, burinta kawai taji muryar Aunty......
“Assalamu alaiki auta”.
Muryan Aunty Zakiyya ta katse mata tunaninta. Batare data amsa sallamarba ta fara magana, “Aunty ina kika shiga kwana biyu, damuwa na nan zata kasheni lokacin mutuwata baiyiba. Wlhy akwai matsala babba aunt, muna kukan targaɗe ga kuma karaya ta samu”.
Babu shiri aunty dake kwance tana hutun gajiyar da suka kwaso a hanyar Niger ta miƙe zumbur tanama Ameera nuni data je. Koda Ameera ta fita ƙofar ɗakin ta murzama key kafin tace, “Auta miya faru?, kinsa zuciyata na neman bugawa wlhy”.
“Wlhy aunty ni tawama saura ƙiris ta buga. Muda muke burin tafiyar tsohuwarnan jiya sai ga wasu huɗun sun ƙaru, harda shegiyar yarinyarnan data tureni naji ciwo, aunty kinsanfa wannan watanne ya kamata na taho nan ko naje Morocco.......”
“Kinga nutsu kimin bayani yanda zan fahimta Farah, wai ƴan gidansu ne suka sake zuwa nan london ɗin?”.
“Eh”. Ta bata amsa tana jan numfashin kuka. Kafin ta faɗa mata duk yanda sukai dashi akan zuwan su Zinneerah.
Itama kanta Auntyn hankali tashe tace, “Aiko bazai yuwuba Farah, kinsan dai wannan shine wata na biyar da samuwar cikinki, ya kuma zama dole kibar London dan Abdul-Mutallab ba mahaukaci bane ba. Yanzu babbar matsalarmu da Mammah bata nan, amma na tabbata itama ai lissafin cikin naki na'a ranta bazata wuce satin nanba zata komo nan london ɗin, ki kwantar da hankalinki karki ja ya fahimci wani abu. ko ita tsohuwar ta fahimta”.
“Aunty taya zan kwantar da hankalina. Wlhy na mugun tsanar yarinyarnan da har yanzu bansan alaƙarsu ba. Dan inaji a jikina akwai aure a tsakaninta da shi, n.......”
“K dalla rufama mutane baki, wai ke Farah wace irin banzar yarinyace. Ana ga yaƙi kina ga ƙura. Ki fuskanci abinda keda muhimmanci a gareki kin wani zauna tunanin kishin banza da wofi akan yarinyar da ƙilama bata ishesa kallo ba, cayay miki yana sonta ne? Haba dan ALLAH, kishin nan duk muna dashi muma dan ya zame mana tamkar gado, amma ke kam naki ya fara zama na hauka dan kina gaurayashi da zargi. Inda Abdul-Mutallab zai ƙara aure na tabbatar da tun sanda ake dabin ya ƙara tunda baƙya haihuwa daya ƙara ai. Amma yanzu ki maida hankali wajen abinda zai kawo miki mafita kinama mutane shirme bayan ke da bakinki kince yarinyar bama ta wuce shekara sha bakwai ba. Ubanmi zaiyi da sa'ar Ameera shida ke da ke mtsoww, ni kinma bani haushi wlhy sai anjima”. Ta ƙare maganar da yanke wayar.
A fusace itama Farah tai wurgi da wayar tata zuciyarta na mata zafi da maganganun auntyn ta. Miye laifinta idan tayi kishin mijinta? Ta yaya zata kasa fahimtarta bayan tasan ƙudirin waɗan nan mutanen akanta, ƙilama da biyu suka ɗakko yarinyar suka ajiye saboda mijin nata. Su dan basusan halin wannan munafukar tsohuwar dake nuna kamar bata gane komai amma tsaf idonta buɗe yake. Ita zama ta iya cewa a wajenta AK ya gado nuna halin ko in kula akan abu koda kuwa yana sane.
Haka ta cigaba da kai kawo a ɗakin har tsahon lokaci duk da tana jiyo motsinsu da hirarsu a falo taƙi fita.
★
A ɓangaren su Hajiya iya kuwa babu wanda ya damu da rashin sake ganin Farah a gidan. Hirarsu suka sha yau ma, salla kawai ke tashinsu har Khalipha ya dawo musu da abinci shima ya zauna aka ɗaura hirar da shi. Babu jimawa shima AK ya dawo gidan. Koda ya shiga yayo wanka shima dawowa yay cikinsu ya zauna ransa fes da farin cikin ganinsu cike da gidansa, abinda yayta fata da mafarkin gani a shekarun baya amma hakan bata kasanceba sai yanzun, duk da ba saka baki yake a hirarba sai ya gadama zaka fahimci yana tare da jin daɗin zaman. Hasalima aikinsa yaketa famanyi a lap-top kamar baya a wajen. Dan shima rashin ganin gilmawar Farah a gidan yasashi tunanin ko bata nan.
Sai kusan gab da magriba sai gata ta fito da alamun barci ta tashi. Sosai yake binta da kallon mamaki. Itako tayi kicin-kicin da fuska cike da takaicinsa. Kenan har takai ya dawo gidan bazai nemetaba saboda yana tare da ƴan uwansa. Batare da tayi magana ko kula gaisuwar dasu Meenal ke mataba ta juya ta koma ɗakinta hawayen takaici na zubo mata. Da kallo duk suka bita harta shige.
Fuskarsa na nuna alamun ɓacin rai yace, “Dama tana gidan?”.
Babu wanda ya iya bashi amsa a cikin su Jamal. Sai Hajiya iya ce tace, “Nima duk zatona ta fice ai, dan tunda kuka bar gidannan wani cikinmu baiji ko motsinta ba. Lafiya kuwa take Moddibo? Ya kanata kaje kaji”.
Maida kansa yayi ga aikinsa yana gyaɗama Hajiya Iya kai kawai, dan shi bazaiso ɗan sauran mutuncinta ya ƙarasa zubewa a idonsu ba. cikin son danne takaicinsa dason rufa asirinta, Ya miƙe yana faɗin, “Inaga to jikin natane babu daɗi. Granny wannan babyn naku na bama matata wahala ya kamata ku tsawatar masa”.
“Kai kai Moddibo kana nufin ciki ne da ita?”. Hajiya iya ta faɗa cike da zumuɗi saboda jin firucinsa.
Ƙayataccen murmushi ya saki yana kallonta. Hakan da yayi ya saka su Bahijja miƙewa suka hau murna da rawa. Yanda sukai ɗin sai ya sakashi jin ƙarin daɗi a cikin rai, a bazata suka haɗa ido da Zinneerah da take murmushi har haƙoranta na bayyana, ita dai tana daga zaune bata tashiba. Saurin maida nata idanun tai ƙasa tsigar jikinta na tashi, dan yanda yay murmushin ba ƙaramin sake fiddo kamanninsa da Little yayiba. A hankali shima ya janye nasa da raɓasu ya wuce zuwa ɗakin Farah ya barsu hajiya iya na jero godiya ga ALLAH da kirarin farin ciki Khalipha da Zinneerah na amsa mata da amin. Dan su Bahijja shirmen da suke na murna yasa bajin mi hajiya iya take faɗa sukeba.
Sai da suka bari yaja wasu ƴan mintuna da shiga sannan suka miƙe suma domin zuwa dubata. Sallama suka farayi ya amsa musu da cewar su shigo sannan suka shiga. kusan Zinneerah ce ƙarshen shigowa.
Farah na kwance a gadon. shi kuma yana zaune kusa da ita gab hannunta cikin nasa. Dan tunda ya shigo zuciyarta ta bata shawaran cewar tai amfani da wannan damar kawai tace bata da lafiya. Hakanne kawai mafitarta gudun samun matsala. Sai kuma akai sa'a shima ya shiga tambayarta mike damunta? Shine ta sanar masa da zazzaɓi ta yini da ciwon kai. amma tasha maganin da Doctor ya bata.
Kukan da tasha yasa idanunta kumbura dama gata fara. Ta ɗagosu da ƙyar tana ɗan dubansu da amsa sannu da addu'ar da suke mata. Koda idanunta suka sauka akan Zinneerah dake can ƙarshe bayan Khalipha sai da taji wani tuƙuƙin baƙin ciki. Ta janye idanunta dake sake cikowa da ƙwallar jin kishin kasancewar yarinyar a garesu, tanajin tsoron ganin wata mace da aure zai iya shiga tsakaninta da mijinta ta raɓesu, shiyyasa zaman Zinneerah a gidan yafi na kowa damunta a yanzu........
“Da alama ma dai yinin yau bakici komaiba?. ko kina da buƙatar wani abune a nema miki ƴar albarka?”. Maganar hajiya iya dake shafa mata kanta ta dawo da ita hankalinta. Kafin tace wani abu AK dake jin daɗin kulawar da Hajiya iyan ke nunawa akan matar tasa yace, “Nima abinda nake mata magana kenan kafin ku shigo, ya kamata ko tea tasha”.