Showing 108001 words to 111000 words out of 237912 words

Chapter 37 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt

27 Nov 2024

23416

tashemu lafiya suka amsa Hajiya iya na nufar ɗaki, shima Khalipha sai ya miƙe ya nufi nasa ɗakin bayan ya kashe komai na falon.




*WASHE GARI*


Hajiya iya ce ta tashi su Bahijja da ƙyar domin yin sallar asuba. Dan har yanzu akwai tarin gajiya tattare dasu. Suna idar da sallar ma tsaresu tai sukai zaman yin azkar. Kowa yana tura baki gaba yayi sannan suka koma suka sake kwanciya. Bata hanasuba dan tasan akwai su dason barci dama.
Barcinsu suka sake kwasa sosai, dan basu farkaba sai kusan tara shima hajiya iya ce ta tadasu. Bayan duk sunyi wankan haɗuwa sukai suka gyara ɗakin sannan suka fito falo inda hajiya iya take. Fitowarsu dai-dai da shigowar mai aikin Farah. Cikin girmamawa ta gaida Hajiya Iya. suma su Zinneerah ta dubesu tana musu sannu da zuwa dan jiya tsoron uwar ɗakinta ya hanata musu.



★★


A ɓangaren Farah kuwa. Koda ta fita gidan a jiya kai tsaye gidan Mammah ta tafi, sai dai tayi rashin sa'ar iske Mammah ta wuce ƙasar China jiya akan harkokin business ɗinta. Hakan baisa ta damuba ta shige tsohon ɗakinsu da Adilah tai kwanciyarta. Dan ita tana ƙasar U.S yin wani course na shekara ɗaya da rabi.
Mama Zaliha da suke kira da Mahma ce kaɗai a gidan, itama Yayace gasu Mammah anan gidan take zaune tun bayan rasuwar mijinta acan Morocco. Takaicin halin Farah yasa taƙi tambayarta miya kawota gidan har sai safiyar yau. Bayan ta idar da sallar asuba ta sami Farah a ɗakin nasu itama ta idar da sallan tana karatun Al-Qur'ani. Zama tai a bakin gado tana kallon ɗiyar ƙanwar tasu da gata ya maidata kamar wata shashasha. Tabbas ta yarda da maganar hausawa da sukance gata mugun ciwo. Dan kuwa shine yayma Farah katutu har bata banbance fari da baƙi a cikin al'amuranta.
Sai da Farah takai aya sannan ta rufe Al-Qur'anin tana duban Mahma. Cike da girmamawa da shagwaɓanta ta gaidata kamar yanda ta saba. Mahma dake dubanta da kulawa itama tace, “Miya faru kikazo nan kika kwana auta?”.
Baki Farah ta tura gaba idanunta na cika da ƙwalla. Kanta tsaye cike da gadaranta tace, “Mahma na baro masa gidanne su zauna shi da dangin nasa”.
“Kimin magana a warware zanfi fahimta fiye da bani ita a dunƙule. Ko kina nufin har yanzu matsalar zuwan Kakar tasane bai kareba kuma?”.
“Ni bashi bane Mahma, ai nace dai na haƙura wannan, amma yanzu dan tsabar wulaƙanci shine ya ƙara kwaso min ƙannensa da wata yarinya da bansanma miye alaƙarsuba aka kawo batare da ya sanar min zuwansuba”.
“Humm” Mahma ta faɗa tana murmushi da girgiza kanta. Sai da ta gama yima Farah kallon nazari na kusan sakkani arba'in kafin ta gyara zamanta da ƙyau. “Farah anya kuwa kinsan mikikeyi? Gaki dai mace mai tarin ilimin addini dana boko, wayayya wadda ALLAH yayma baiwa kala-kala da ni'imomi, sai dai kuma shashasha ce. Wai sai yaushe zaki daina biyema Hindatu da Zakiyya ne? Farah kinsan ko muhimmancin nuna darajar dangin miji da mutuntasu ga miji kuwa? Kodan kina ganin kullum Hindatu na aibanta dangin Abdul-Mutallab shiyyasa kike ganinsu kamar marasa daraja a idanunki? Bara na faɗa miki gaskiya idan zaki ɗauka. Hindatu mahaifiyarsa ce, zai iya jurewa ya shanye yakumayi haƙuri akan duk wani tarkace da zata jingina danginsa da shi koda yanajin zafin hakan. Keko matarsace duk da kina ganinku jini ɗaya da kuma fawar da kike samu ga mahaifiyarsa zai iya ajiyeku akansu wlhy. Shin bazaki godema ALLAH da ni'inar da yay miki na samun miji irin Abdul-Mutallab mai kawaici da haƙuri ba. Dan wlhy na tabbatar badan soyayyar da yake miki ko tirsasawar hindatu a garesaba yake ƙyaleki. Haƙurinsa da sanin ya kamatansane kawai ke rinjayarsa wajen baki uziri kafin ki kaisa bangon da bazai iya jurewaba. Idan kuma kikai wasa zakiyi nadama a lokacin da guri ya ƙure miki ki kuma rasa samu damar gyara komai. Saboda zuwan wannan yaran kawai ya isa nuna miki gudin halinki yasa ya guji ya faɗa miki ki sanarma mahaifiyarsa ta hanashi, kinga kuwa sai ki dawo hankalinki da irin masu halinki dan mata da yawa sunada wannan bazan halin shiyyasa da yawa duk son da mazansu ke musu sai kiga yana raguwa harsu fara tunanin ƙaro musu abokiyar zama koda kuwa babu haka a tsarinsu. Ni nasan babu wani ilimin zama da miji da baki dashi Farah. Dan kuwa idan da dama ma sai dai ki koyar da wasu. Amma tun zuwan ƙaninsa gidanku kin watsar da komai na ingatacciyar rayuwar aurenku. Kin maida hankalinki wajen kawo ƙararsa kullum da kushe danginsa da nuna ƙyamatar su kusancesa. Anya baƙya tunanin cewa akwai matsala? Baƙya tunanin hankalinsa zai iya fara karkata bisaga ƙudirin dangin nasa nason ƙara aurensa. Yanzufa cikine dake, amma ki duba ko'a jikinsa. Yanda ya nuna murnarsa da farin cikinsa akan wancan cikin da kika samu ya zube bai nunaba akan wannan. Banama tunanin ya sanar da kowa a cikin dangin nasa, tunda dama wancan karon hanashi faɗa musu kukayi wai sai dai suji kin haihu. Sai gashi baki haihunba kuma sabida ALLAH ya rubuta cikin ba zaunanne baneba. Wlhy ki dawo hayyacinki, ki dawo da ingattacciyar rayuwar aurenki kamar farko domin cigaba da damƙe zuciyar mijinki. Duk wannan gantali da shirmen naki babu inda zai kaiki sai komawa baya a garesa. Dan kullum sabbin halayyarki dusashe taurarenki yakeyi a wajensa. Ki dinga daurewa wajen danne wannan zafin kishin naki da kika gada kodan tsare martabarki. Wlhy duk yanda kuke zaton kunada kishi na damaku na shanye. Amma tunda nai haƙurin zama da kishiyoyi har biyu a lokacin rayuwar aurena ya kamata kuma ku saduda. Dan rayuwarma nawa takene baki ɗaya. Daga randa UBANGIJI ya bukaci ganinka dole ka amsa kiransa koka shirya kobaka shiryaba. Duk wata dukiyarka da suna da ilimi da mulki da nasaba da koma miye da kake takama dasu bazasu amfanar dakai da komaiba sai ƙyawawan halayenka da ibadarka. Dan haka sai kisan inda ke miki ƙaiƙayi kibar wannan shirman da kika ɗakko mara hanyar ɓillewa ki koma Farah ɗinki dana sani ada mai hankali da sanin yakamata akan rayuwar aurenta. Ki kuma tashi ki shirya ki koma gidan mijinki tunkan ya fahimci kinbar gidan. Ki kuma kama kanki akan zaman dangin nasa. Ki kiyayi yawan kawo kararsa dan kina zubar masa da kimarsa a idanunmu alhalinsa dan kece sheɗaniyar. Dan wlhy idan Hindatu ta dawo naji kin kira wayarta akan wata matsalar danginsa da kaina zan saka Abdul-Mutallab ya ƙara aure......”
Da sauri Farah ta ɗago ta duba Mahma idanunta na kawo hawaye. Mahma tace, “Kalleni da ƙyau da gaske nakeyi, dan ko ita Hindatun sai dai tazama ƴar kallo bareke da kike matsayin ƴa. Idan zakije ki kama kanki kije ki kamasa kafin na saitaki a layin daya dace da ke tunda ke shashash ce. shin gata haukane ma kenan?”.
Cikin kuka Farah tace, “To amma Mahma shima idan yazo kimasa faɗa ya daina min ihu banaso. Sannan ya daina nunamin kamar danginsa sun fini a wajensa tunda nima dai ƴar uwarsace kuma jininsa mafi kusanci”.
“Naji zan masa. Amma sai naga gyara daga gareki sannan.”
“Insha ALLAH zan gyara, kuma zanyi duk yanda kikace”. A karan farko Mahma tai murmushi da kamo hanunta jikinta. Tace, “Yauwa kokefa ƴar albarka. Amma duk kin wani susuata kanki tamkar wata shashasha wadda batasan ciwon kantaba da mutuncinta. Karki sake kiyi saken da Abdul-Mutallab zai kufcemiki dan zaki dawwama a dana sani har ƙarshen rayuwarki kuwa”.
Kanta ta jinjinama Mahma cike dajin daɗin nasiharta tana kwantar da kanta a bisa cinyarta. Sake kwantar da murya Mahma tayi ta lallasheta sosai da ƙara mata shawarwari sannan ta sakata tai wanka ta shirya, ko breakfast batai zamanyiba ta kamo hanyar dawowa gida zuciyarta fal tsare-tsaren dawowa da martabar aurenta daga yau kamar yanda take ada kafin zuwan Khalipha daya susutata saboda rashin son ganin dangin AK raɓe dashi bisa huɗubar Mammah............✍






*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*




*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 32*
___________________




_*LAVENDER RESTAURANT..*_
_(Palace of mouthwatering food/delicacies)_


_IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_


_*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE.._*


_*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.._*


_*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283 akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021 to 3/10/2021 Nigeria @ 61_*


_*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU._*


_*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN. _*


_*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇🏾RIGIJI GABJI_*


_*Nigeria @ 61 _*
_*COOKING COMPETITION!!!_*

_*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine da wasu prize suma saura kuwa zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar_*


_*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA_*


____________________






*Page 32*


............Shigowarta gidan yayi dai-dai da dawowar Khalipha daga yo musu takeaway daya fitayi. Kamar koda yaushe shine ya gaisheta sabida halinta nason nuna isa. Koda ta shigo gidan ta kalli ko'ina sai taga yamata yanda takeson tsaftarsa duk da an cika matashi, dan Farah mace ce mai tsafta, sannan duk wani abu da mace keyi dan ganin ta faranta ran miji Farah ta iyashi. Matsalarta kawai zafin kishi da hawa kan karatun su Mammah naƙin danginsa, dan tunda Khalipha yazo gidan ta dainama Adnan mafi yawan abubuwan da take masa na kulawa, ita burinta kawai Khalipha yabar mata gida. Shiko ya fita taurin kai yay kunnen uwar shegu da ita.
Samun komai yanda takeso yasata batayi ƙorafi ba ta shigo cikin kame kai da tsare gida ta gaida hajiya iya. Yanda take cika da batsewa yasa suma su Jamal gaisheta suna ƙoƙarin kama kansu.
Ko kaɗan hajiya iya bata nuna mata komaiba ta karɓa mata gaisuwarta hardasu tsokana. Batare data kula tsokanar da Hajiya iyan kemataba ta nufi ɗakin AK tana harar Zinneerah da ƙudirta abubuwa masu yawa akanta. Dan har cikin ranta tanajin kishin zamanta a gidan fiye dasu Bahijja. Bakomai yasata jin sassauci akan su Bahijjan ba sai sanin uba ɗaya suke da AK babu wani maganar aure a tsakaninsu. Sai dai kishin cika mata gida da sukayi. Zinneerah kuwa tasan babu uwar da suka haɗa na shaƙiƙanci shiyyasa takejin zafinta. Itafa sabida shegen kishinta ko ƙawayenta bata yarda su raɓeta balle suzo mata gida. Tafi ganewa ayi catin ko waya yafi sauƙi ƴar nesa-nesa. Suma fahintarta yasasu janye jikinsu gareta suka bita yanda takeso duk da wasunsu ma sunyi aure. Tsaron nata kuma baisa wasu a cikinsu gagarar bibiyar mijin nataba acan waje batare da sanintaba. Danma shi AK ɗin na ƙoƙarin taka musu burki dan ba ɗaukar wargi ko shirme yake ba shima ɗin aƙidarsa tayi yawa.


Tsaye ta samesa gaban Mirror yana fesa turare. Ta bishi da kallo cike da so da ƙauna da kishinsa mai yawan gaske, wanda ita kanta batasan adadinsaba. Sosai yayi ƙyau cikin pitch suit ɗin nasa da suka dace da kalar fatarsa mai sheƙi da ɗaukar idon mai kallo. Ga abu mafi soyuwa a gareta tare dashi shine kwantaccen sajensa da sumar kansa dake dai-dai misali dan ba tarata yayba da yawan tsiya. Tana nan dai-dai misali.
Duk da yaji shigowar tata bai fasa abinda yakeyiba. Sai da ya ajiye gwangwanin turaren ya gyara zaman tie ɗinsa sosai da ƙara kwantar da sajensa sannan ya juyo gareta yana zuba mata manyan idanunsa masu cikar gashi da haske. Gasu da kwarjini masha ALLAH tamkar ba namiji ba. Haddace kowanne kalar kallonsa da ma'anarsa ya sakata risinar da kanta ƙasa. Kafinma yay magana tace, “I'm very sorry, bada niyyar kwana najeba zazzaɓine ya rufeni acan ka tambayi Mahma ma”.
Janye idanun nasa yayi kawai yana girgiza kansa. Ya ɗauka agogonsa ya hau ɗaurawa batare da yace mata komaiba. A hankali ta tako garesa tana kama hanun da ɗage wanda yake ƙoƙarin ɗaura agogon dashi. Sakar mata yayi babu musu ta ƙarasa saka masa. ta sake ɗaukar wasu kalolin gwangwanayen turaren ta fesa masa tana ɗan murmushi, kafin kuma ta rungumesa cike da so da ƙaunarsa.
Ajiyar zuciya suka sauke a kusan tare. Ya lumshe idanunsa da zagayeta da hannayensa shima yana lumshe idanunsa. Dan da gaske shima yayi kewar tata. Tunda suka dawo daga 9ja taƙi kwantar da hankalinta waje guda ta nutsu kullum da shirmen da take tashi musu dashi a gidan. danma wani abun tana shakkarsa shiyyasa take tsoron aikatawa. Fatan da addu'arsa shidai dama a kullum ALLAH ya gyarata ta koma Farah ɗinta daya sani ta baya mai tattalinsa da son farin cikinsa akoda yaushe.
Ɗagota yayi yana mai tsare ƙyaƙyƙyawar fuskarta da kallo mai cike da ma'anoni masu yawa. “K baki gajiya dakai ƙarar mutane kullum wajen iyayenki?”.
Cikin marairaice murya da shagwaɓa duk da ranta fal yake da tsantsar takaicin zaman su Hajiya iya gidan ta sake narke masa. “Ai dai nace kayi haƙuri, kuma kaima kasan a yanayin da nake shiyyasa nake shiga saurin fushi”.
Kansa kawai yaɗan rausayar yana sauke idanunsa akan cikinta. Sai kuma ya ɗaura hannunsa saman cikin tare da ranƙwafawa ya sumbacesa sannan ya ɗago. “Dolene inzo naima babyn nan gargaɗi ya bar rikitamin ke kina bani ciwon kai”.
Karan farko tai ƴar dariya da sake rungumesa tana maijin tsananin daɗi. Dan tunda ta samu cikin nan bai taɓa nuna kulawarsa kamar ta yau ba. Kodan ta kasa kwantar masa da hankaline oho, dan wancan cikin daya zube lokacin da aka sanar masa da samuwarsa tamkar zaiyi hauka dan daɗi, yabi ya rinƙa tattalinsa da nuna zaƙuwar ganin ya fito duniya. Daya zube ɗin kuwa hardasu ƙwalla yayi, yabi ya shiga damuwa sosai, sai zuwan Khalipha gidan ne ya sakashi komawa normal life ɗinsa. yayinda ita kuma suka fara samun matsala daga nan.
Shima ƙaramar dariyar yayi yana ɗagota. “Uhm kinga barni naje mu gaisa dasu Granny inada meeting 11am”.
Duk da zuciyarta ta sosu da zancensa sai ta daure ta kanne, koba komai anci mata lokaci ai tunda gashi lokacinta sai ta raba dasu. Da basa gidan kuwa itace zata kasance da shi har lokacin fitar tasa ta cika. A tare suka fito dan tayi alƙawarin sai dai suci lokacin nasu tare itama dan bazata barmusu ba.


A dining suka iske su Hajiya iyan zasuyi zaman karyawa da abincin da Khalipha yaje ya sayo. Mai aikin Farah kuma ta shirya musu shi a dining tamkar a gidan aka girka shi. Khalipha na daga tsaye bayan Granny suna magana dan shi fita zaiyi. Juyowa yay saboda jin ƙamshin turaren yayan nasu da takun sa da baya ɓoyuwa ga duk wanda ya sanshi. “Barka da asuba Yayanmu”. Ya faɗa dai-dai suna ƙarasowa wajen.
Hannunsa AK ya kamo cikin nasa yana faɗin, “Halan yanzu ka tashi kake kiran asuba likita?”.
Fuskar Khalipha da murmushi yace, “Ai ni harma fita nayi naga gari Yayanmu, kai nedai nake tunanin yanzun ka tashi shiyyasa na faɗa”.
Kafin AK ɗin yace wani abu Granny dake kallonsu cike dajin daɗi da sha'awar yanda shaƙuwarsu take wanzuwa cikin ƙanƙanin lokaci tace, “Ni nama zata yau bazai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login