Showing 198001 words to 201000 words out of 237912 words

Chapter 67 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt

27 Nov 2024

23390

shi. Ashe wannan damar Farah ta samu daga garesa take yanda ta gadama. A binda kuma ta fahinta da shi adalcine kawai da sanin darajar mace da son mutuntata ya sashi zama mai sauƙi ga iyalansa badan anfi karginsa bane ko bazai iya motsa ƙwanji ba. Jitai wani natsuwa da kaunarsa na sake saukar mata a rai da bargo, har tana jerama UBANGIJI kalaman godiya da samunsa matsayin abokin rayuwarta batare da yayi shawara da itaba ko dubi da cewar AK ɗin ya ɗarata a komai na darajojin duniya, a lahiran kuma tana fata da addu'ar su kasance a muhalli ɗaya a gurbin gidan aljanna insha ALLAHU rabbi..
Da wannan tunanin ta kammala shiryawa a gurgurguje duk tunaninta su Granny na'a gidan basu tafi ba.............✍






*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍










*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*


*_TYPING📲_*




*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 60*
________________________




*_KAƊAN YA RAGE SU ƘARE_*




*_MATA ƴan ƙwalisa kuna ina za'aci kasuwar sama babu ku?. Mg's skincare ɗin fa na gab da ƙarewar kaya kuna nan sake da baki baku mallaki naku ba_*




_Mg's SKINCARE nagartattun kayan ne dake gyara jiki da fata cikin sauƙi, sunada inganci da rahusa dai-dai da aljihunku._


*Da kin fito a ringa ga tauraruwar taurarin nan mai fatar da babu kamarta tamkar dinare abin haske da walwali.*


*_Sabulunsu kawai kika ɗana sai kinsan kin kai kuɗinki inda babu asara balle dana sani_*


_A yanzu haka muna jerin kayayyaki da suka rage kamar haka_👇🏻


Available


_Akwai: herbal whitening black soap 3k_
Akwai: beauty kit 11k shi set ne yakunshi Abu 6
Soap
Body cream
Face cream
Body nd face scrub
Cleanser
Glow oil


Location
kaduna buh mn tura Kaya ko Ina saidai inmutum ya amshi kayanshi zebada kudin delivery


WhatsApp 08062991549
Call 08064532391


Instagram:glow_with_mgs


Facebook:mg's skincare


*_Karku bari ayi babu ku guys, siyan nagari maida kuɗi gida._*


________________________




*Page 60*


...........Fitowa tai da sanɗa kanta a ƙasa saboda tunani da kunyar su Granny da take zaton har yanzu suna gidan. Yayinda AK dake zaune a falon shi kaɗai yana latsa waya mayataccen ƙamshin haɗin khumrah ɗinta ya samu nasarar kaiwa ga hancinsa. A hankali ya ɗago yana kallon sashen ƙofar bedroom ɗin nasa zuciyarsa na wani motsawa a cikin ƙirji.
A kan laɓɓansa ya ambaci kalmar “Mash ALLAH” yana wani lumshe idanunsa. Ganin tana nufar hanyar fita da sanɗar da takeyi ya ɗan murmusa, sai da ta ɗan gotashi yace, “Nan zaki zo ai”.
Ina ƙasa Zinneerah ta shige dan kunya, har mamakinsa take ganin shi ko'a jikinsa tamkar bai aikata wani aika-aika ba.
“Kona taso?”.
Taji ya sake ambata. Kafinma ya gama rufe baki ta nufosa dan shi ba abin wasanta bane, abinda ya shiga tsakaninsu kuma bai rage masa kimarsa da girmansa a idanuntaba sai ma ƙaruwa da yayi. Ta ɗanji sanyin ganin babu su Granny, dan haka taso kaiwa tsugunne gabansa.
Bai motsa daga kishin giɗar da yay a kujera yana mata kallon ƙasan ido ba, ya kamo hannunta ganin zata tsugunna. A saman cinyarsa yay mata masauki. Hakan ya sata saurin kallonsa. Da wannan damar yay amfani wajen riƙe idanunta cikin nasa. Duk yanda taso ta janye ta gagara. Sai neman kashe mata jiki yake da wani sakaltaccen kalo dake tada mata tsigar jiki. Babu shiri idanunta suka fara tara hawaye.
Karan farko tun shigowarta falon guntun murmushi ya bayyana a fuskarsa, ya lumshe ido ya buɗe a kanta yana kamo fuskarta cikin tafukan hannunsa. “Miyasa ke raguwane?.”
Cikin suɓutar baki tace, “Tsoro kallon yake bani”.
Harga ALLAH ta bashi dariya, duk yanda yaso danneta kar yayi kuma hakan bai yuwuba, sai gashi da sakin murmushin da har haƙwaransa na bayyana. Shagala tai da kallonsa dan tabbas murmushi na masa ƙyau musamman wanda ke bayyana haƙwaransa irin wannan. Nisan da tai a nazari yasa harya iso da fuskarsa gab da tata bama ta saniba. Sai jin saukar laɓɓansa kawai tayi akan nata. Duk yanda taso ta nuna zamewa hakan ya gagara. Dan wani irin sallo da tunda uwarta ta haifeta ba'a taɓa mata shiba yake sarrafa lips ɗinta.
Luf tayi tana amsar rikitaccen karatun na babban yaya data fara haddacewa daga safiyar jiya zuwa yau. Sai da ya tabbatar ya ida zubar da ɗan sauran ƙarfin data samu sannan ya barta yana rungumeta a jikinsa gaba ɗayanta. Yanda yaken sauke numfashinsa mai sanyi da nutsuwa a cikin kunnenta yasata sake lafe masa a jiki tana rumtse idanu. A ranata ko rayawa take, ‘Yayanmu zaka kasheni da wannan salon naka da yafi ƙarfin shekaruna’.
Sun kai kusan mintuna uku a haka kafin ya ɗagota yana kallon fuskarta, duk yanda yaso su haɗa ido yanzun kam taƙi yarda. Yatsunsa biyu ya sa ya ɗago haɓarta, bai damu daƙin yarda su haɗa ido da taiba.
Tana bashi dariya da ƙara birgesa da wannan sanyin nata, dan haka yay wani munafukin murmushi da kamata ya miƙar.
Dining suka nufa yana riƙe da hannunta, sai da ya zaunar da ita sannan shima ya zauna. Da kanta ta miƙe ta haɗa masa abincin yanata faman binta da fitinannen kallon nan nasa dake sakata dabircewa komin jarumtar da taso nunawa.
Shiko fahimtar da yay kallon nasa na mata tasiri tunma suna can gidan yake sakashi kasheta da su. Bata zuba nataba, bai kumayi maganaba, sai da ta gama ta koma ta zauna ta ɗan dubesa. Ganin shima dai kallon nata yake ya sata janye nata idanun gefe.
Komai baice mataba ya fara cin abincin, sai da yay nisa da ci sannan yay magana batare daya kalletaba. “Juyo nan”.
Juyowar tai tana fuskantarsa, sai kawai yay mata alamar ta buɗe bakinta. Ganin yanda fuskar tasa take ya sata buɗewar. Daga haka ya cigaba da ciyar da ita yana ci shima har suka cinye. Godiya yayma UBANGIJI yana miƙewa ya barta a wajen. Hakan ya sata miƙewa itama ta tattare kayan a basket ɗin da aka kawo, sam batajin daɗin jikinta, a yanzu haka tafi buƙatar ta samu waje ta kwanta. Sashen ta bari baki ɗaya zuwa nata, tana shiga ta sauke ajiyar zuciya da nufar kitchen.
Tana cikin wanke kwanikan ya shigo kitchen ɗin, waiwayowa tai ta dubesa. Ya canja kayansa zuwa shadda fara tas da tai masa tsananin ƙyau, ga mayataccen ƙamshinsa mai cika hancin mai shaƙa da bashi nutsuwa. Ya ɗan janye idanunsa daga kanta yana kallon agogon hannunsa. “Bara na gaishe da su Mammah kina buƙatar wani abu ne?”.
Duk da tayi mamakin jin zancen Mammah sai batace komaiba taɗan girgiza masa kanta.
Takowa yay gabanta yana ɗago fuskarta suka kalli juna. “Baza'amin addu'a ba?.” ya faɗa a wani irin sanyin murya.
Tana mamakin a yanda ya iya sarrafa yanayinsa a salo daban-daban, kuma duk cikin kame kansa babu wani rawan kai ko gaggawa tattare da shi. Idan badan ita da take ganin true color ɗinsa a tsakanin jiya zuwa yau ba babu wanda za'a faɗama haka yake ya yarda, dan ko'ita idan yay abu ya basar sai take ganin tamkar ba shine ya aikataba. Ya barta da kunya shiko ko'a jikinsa.......
“ALLAH ya tsare ya dawo da kai lafiya Yayanmu”.
Haɓarta ya saki da tura duka hannayensa a aljihunsa yana kallonta, “Har yanzu matsayin Yayan kawai gareni?”. Ya faɗa yana tsatstsare ta da idanunsa masu kaifi a gareta.
Ɗan ɗago idanu tai ta kallesa, ya wani juya mata nasa manyan idanun yana ƙara tsuke fuska.
“Yanzu ni waye a wajenki?”
Ya faɗa cikin muryarnan tasa ta rashin sakewa.
Mamaki tambayar tasa ta bata, da ɗan rawar murya da kunyarsa ta haifar mata tace, “Yayanmu!”.
“Daga nan fa?”.
Duk da ta fahimci abinda yake son jin sai ta noƙe dan itama ɗin dai gwanace a miskilancin.
“Zaki magantune”. Ya faɗa yana sake kallon agogonsa da juyawa zai fita. Jitai duk babu daɗi,
“Kayi haƙuri idan na ɓata maka rai Yayanmu”.
“Ba haka matata ke bani haƙuri ba, dan haka sai ki shirya ta yanda nafi buƙata kafin na dawo”. Ya faɗa yana ficewa batare da ya waiwayota ba.
Kallo ta bisa da shi zuciyarta na maimaito mata karatun hajiya Falmata daki-daki. Ganin tunanin bazai kaita ko inaba ta cigaba da aikinta cikin dauriya dan wani sabon zazzaɓi ke neman saukar mata, ga wajen itakam har yanzu zafi yake mata kaɗan-kaɗan. Duk da yanda take jin nata haka tai juriyar gyara gidan har sashensa, sauƙintama ba wani datti bane. Turaren wuta ta saka har General falo da ƴar barandar waje. Ta bi kuma da fresheners masu daɗi. Sosai nutsuwa ta ƙara saukar mata jin ko'ina ya ɗauka ƙamshi kamar yanda take buƙata. Daga haka ta taƙarƙara ta koma bedroom ta kwanta kozata samu barci ya ɗauketa kafin sallar la'asar.
Tana kwanciya ana fara knocking, dole ta miƙe kamar zatai kuka. Hijjab ta saka sannan ta fito ta buɗe. Ganin su maman halima yasa fara'arta bayyana tana jera musu sannu da zuwa. Suma cike da kulawa suke amsa mata suna shiga da kayayyakin da sukazo dashi. Akwatinanta ne na lefe da tarkacen ƴan kayayyaki. Sai kayan gara da suka bata mamaki.
Naziru daya kawosu ne yace ta buɗe ƙofar kitchen ta baya a saka tacan zaifi sauƙi. Dan yasan hanyar tunda da shi aka kawo furnitures ɗinta. Cike da girmamawa ta karɓa masa. Taje ta buɗe ƙofar shi da maigadi suka dinga jigilar shiga dasu su Sakina na tayasu da wanda zasu iya. Hardasu kayan cin-cin. Jitai ƙwalla ya cika mata ido najin daɗi da tausayin su baba. Iyaye dabanne, duk da sunsan babu abin AK ɗin ya rasa a rayuwarsa sunyi hoɓɓasa ɗin ganin sun cika mata darajarta akan abinda al'ada ta tanadar. Dan dai gara al'adace da ƙyautatawar iyaye ga miji bawai wajib bace kamar yanda samarin yanzu suke kallo, harma suke samun damar yarfa mace in ba'ai mataba saboda son zuciya.
Sai da aka gama shiga da komai sannan ta kawo musu ruwa da lemo sukai zaman gaisawa. Sakina sai kalle-kalle take da jinjina wannan gida a ranta, duk da da ita aka kawo amarya yau dai tafi kallon komai yanda ya kamata dan shiyyasama ta nace sai tazo. Aiko sai gashi ƙiri-ƙiri tana nuna hassadanta a fili dan sai wani yamutse-yamutsen fuska take ita da uwarta dake ji kamar ta fidda Zinneerah ɗin ta kawo sakina ciki.
Ita dai Zinneerah bama bi takansu taiba, dan akwai sauran ƴan ɗan musa da sukazo tare su uku sai maƙwaftansu mmn sadiq ɗin abokan arziƙinta suma su uku, sai ƴaƴan mmn halima da ita, da matar Naziru.
Kasancewar su mmn halima tsaffin mata ya sasu fahimtar yanayin Zinneerah ɗin, sai mamaki ya kama irinsu mmn sakina da matar Naziru da ita kanta mmn Haliman dan sudai sunsan Zinneerah ba wannan ne aurenta na farko ba, tunda gata harda little. To amma yanayin nata yayi kama da na wadda namiji ya fara taɓawa. Sauran kam dai har ransu gani suke Zinneerah ta kawo mutuncinta, musamman ma ƴan dan musa da babu wanda yasan ƙaddarar data afku ga Zinneerah ɗin har yanzu. Duk da kuwa Inna Asabe ta saki maganganu da sukaje danya sai duk suka kallesu matsayin hassada kawai da sharrin baƙin kishinta da bai ɓoyuwa harga ƴaƴa. Sai da suka shiga ko ina suna mai yabawa da jera addu'oin fatan alkairi.


★★★


Koda Mahma ta koma gida bata yarda ta nunama su Mammah komaiba, hasalima dama basusan inda tajeba. Da sukace zasuzo gidan AK ɗin kuma cikin dabara ta hanasu akan su bari sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu sai a maida Farah baki ɗaya dan ya kamata takoma ɗakin mijinta tunda ta samu sauƙi.
Da farko Zakiyya ta tubure akan Farah bazata komaba har sai AK ya saki Zinneerah, zuwa lokacin Farahn ta haihu. Kallonta kawai Mahma tai tana gitgiza kai da sake yarda da zancen AK. Kamar zatai magana akan cikin Farah ɗin sai tai musu shiru kawai. Dan ita Farah ɗince da kanta tace zata koma gidanta saboda tunowa da zafafan gargaɗin AK. Ba aunty Zakiyya da Mammah ba hatta Mahma sai da tai mamakin furicin na Farah, amma sai batace komaiba tai murmushi kawai.
Aunty Zakiyya kuwa wani shegen harara ta watsa mata da faɗin “Saiki koma ballagaza kawai mayyar miji”.
Kaucewa dukan nata tayi tana kumbura baki, dan ita dai wlhy shawarar Adilah da sukai waya jiya da daddare zatabi, gara ta koma koma mi za'ayi ayisa acan.


★★★


Hajiya iya kuwa data koma duk da tana fushi da Uncle Ahmad har yanzu taƙi saurarensa dan ta dage sai ya ƙara aure ya ajiye matar a Nigeria koda zata barsa ya koma. Kokuma ya bar iyalansa anan. Wannan shine zaɓin data bashi kawai ta tsuke bakinta.
Zaunar dasu tai shida Baffah da Mommy ta sanar musu komai daya faru. Baffah dai yasha mamaki wannan al'amari, Uncle Ahmad kuwa da dama gaba ɗaya hasashensa da nazarinsa ya tafi kacokan a wajen ne tunda Baffah ya bashi labarin abinda ya faru da tarihin Zinneerah sai baiji komai ba sai takaici da tausayin Zinneerah ɗin.
Cikin zafinsa yace, “Aiko indai ta tabbata sune suka aikata yanda sukai wasa da rayuwar yarinyarnan suma tasu saita shiga garari wlhy, dan bazamu barsuba sai inda ƙarfinmu ya ƙare. Gatan da suka kalleta da tashinsa a farko har suka aikata mata wannan ta'asar zasu tabbatar da tunaninau gurɓatacce ne kuwa”.
Ɗari bisa ɗari duk suka bashi goyon baya. Suna cikin tattauna yanda zasu ɓulloma al'amarin Khalipha ya shigo gidan, shine ya musu ƙarin bayani akan kamo hajiya lanti da sukai a yanzu haka kuma tana hannun hukuma, Alhmdllh kuma ta bada haɗin kai akan cewar zata sadasu da hajiyar data kaima su Zinneerah dan itama saboda ita taje katsina. Amma sai ta tarar tana saudia dan can ta koma da zama. dama can sana'arta kai yara saudia aikatau, duniyace tai mata gwatson ƙyanwa tunda aka cimimiyota ta dawo kuɗin komawa ya gagareta. To yanzu dai Alhmdllh akwai bikin yaronta da akai a wannan satin rana ɗayama da nasu Zinneerah, itama jira take a gama bikin dama ta sameta dan tazo Nigeria.
Sunji daɗin jin hakan, a take suka yanke zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu itama a damƙota kawai kafin ta sake tafiya, suma kuma su Mammah karsu bar ƙasar.
A wannan tattaunawar AK da yazo gidan gaishesu ya samesu. Zama yay suka ɗan ƙara tattauna zancen sannan ya shiga ya gaida matan gidan. Daga haka ya ɗauka little daya maƙale masa suka wuce gida dan sai da ya fara zuwa ya gaishe dasu Mammah. Acan ɗinma bai nuna musu komaiba, dan koda Farah tace zata koma gida gobe a taƙaice yace mata, “Ƙofa abuɗe take” daga haka yaja bakinsa ya tsuke. Bai kuma bi takantaba harya baro gidan. Aunty Zakiyya kam bata tanka masaba shima bai tanka mataba dan idan taurin kai ne gidan ta taras.


______________________


*_DANYA_*


Ƴan biki sun dawo gida lafiya, yayinda kowa ya fara ƙoƙarin fesar da maganar daya gumtso akan auren na Zinneerah da daular duniyar da ALLAH ya kaita ciki. Ga miji ɗan gaske acewarsu (🤣ba bily ba😂). Wasuma da biyu suke ƙara kambama zancen dan baƙanta ran Inna data haukace musu da bala'in su fice mata a gida.
Ko'a jikinsu, dan da suka fitanma gaba suka ƙara wajen isar da labarai kala-kala harda waɗanda ba'ayiba ma. Gasu Yaya Gajeje kuwa ga labarin a ransu ga tsoron tunkarar Inna da batun abinda suke hasashe tattare da Tinene, dan tunda suka shigo gidan ɗaki ta shige ta ƙudundune a zani tana rawar sanyi.
Da ƙyar Yaya Gajeje taja ƙafafunta ta nufi gidan saboda yara data bari, gashi yamma nayi tunda tana ƙauyen gaba dasune duk da babu nisa.
Duk da takaici da zafin da inna keji a ranta da labarin ɗaukakar da Zinneerah ta samu hakan bai hanata zaman jin labari a bakinsu Atine dakeyi suna gatsine-gatsine ba kishi fal ransu.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login