Showing 147001 words to 150000 words out of 237912 words
Chapter 50 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt
ƙanƙame little tayi a jikinta da sauri mamakin abinda Yayansu yayi na neman kasheta da ranta. Ta bisa da kallo harya shige ɗakin hajiya iya ko waiwayosu baiyiba. “Aunty!!” little ya faɗa da ƙarfi cikin kunnenta yana bubbuga mata kafaɗa. Babu shiri ta juyo garesa tana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Sai kuma ta saki murmushi da lakace hancin little ɗin tana faɗin, “Haba bawan ALLAH kashemin dodon kune zakayi ne? Waya kawoka nan?”.
Bata da mai bata amsa. Danshi little ma dariyarsa ya saki maiban sha'awa saboda lakace masa hanci da tayi, ya kwanta a kafaɗarta yana zagayo hannunsa ɗaya a wuyanta zuwa ɗayar kafaɗarta. Hannunta ta ɗora akan gadon bayansa tana shafawa a hankali da murmushi, murya ƙasa-ƙasa tace, “I miss you my heart, ALLAH ya albarkaci rayuwarka, ya baka kariya a kowanne sakan na agogo”.
A ɗakin hajiya iya kuwa koda AK ya shiga tararwa yay su Baffah na magana. Baffah na zayyanema Hajiya iyan yanda sukai da Mammah. Gaishesu yayi, duk suka amsa masa da kulawa. ya yunƙura da nufin fitowa ya basu waje Hajiya iya ta dakatar dashi ranta a ɓace dajin abinda Mammah tazo tayi.
Komawa yayi ya zauna kansa a ƙasa dan yaƙi yarda ya kalli kowansu, bayason suga damuwar dake kwance a cikin idanunsa.
Cikin kaushin murya Hajiya iya tace, “Ina maka murna da samun yarinyar ƙwarai kamar Zinneerah moddibo, itama kuma ina tayata murna da samunka matsayin miji. duk da har yanzu zuciyata ta gaza hasaso ko tunanin ta yanda kuka samar da Abdul-Mutallab. Amma a dalilin wani bayani da Khalipha yaymin yasani shiga wasuwasi, zuciyata kuma ta ƙara shiga ruɗani da bayanin mahaifinka akan abinda ya faru randa aka sanar maka yaron jininka ne. Sai dai hakan dakai ba shike nuna zan yarda dakai ɗari bisa ɗari ba Moddibo har saina san gaskiyar al'amarin nan. Amma zan cigaba da roƙon ALLAH ya bayyanamin gaskiyar kafin nabar duniya. Ada nayi tunanin barin tarewar Zinneerah harta kammala karatunta na sakandire. Yanzu kuma na canja shawara saboda dalilai masu yawa. Ciki kuwa harda gadaran da mahaifiyarka keson nuna mana akanka da ƴar uwarka, tunda dai ita na fahimci batasan kawaiciba. Kaje daga yau ka fara gyaran gidanka, ka kuma shirya haɗama Inno lefe dan nan da kwanaki goma zata tare”.
Ba AK kawai ba hatta Baffah da Mommy sai da suka ɗago suka kalli Hajiya iya. Cinkin ɗan rawar baki Baffah yace, “Amma Inna karatunta fa?”.
“Tayi a gidansa”.
Ta bama Baffah amsa kai tsaye babu alamar wasa ko sassauci a saman fuskarta. Ɗan ajiyar zuciya Baffah ya sauke duk da shima bawai yana nufin wani dogon zango Zinneerah zata kaiba. Dama dai tunaninsa bai wuce ta gama zana jarabawarta ta ssce da zasu fara kwanan nanba. Amma kuma tunda hajiya iya ta yanke hukunci shi hakan ya masa kodan ya sake tabbatarma Hindatu shine boss.
Mommy ce tai ɗan murmushi tana kallon hajiya iyan, cikin kwantar da murya tace, “Innarmu baƙya ganin anyi gaggawa. Mu bashi damar shiryawa a tsanake sai a haɗa danasu Ni'ima tunda wata biyu ne kawai ya rage”.
“Na riga na gama yanke hukunci Bilkisu, ba kuma zan canjaba saboda shine dai-dai. Anjima kaɗan za'a kaini gidan Hauwa'u itama”.
Dole Baffah da Mommy suka amsa da to, AK kuwa uffan baice mataba. Dan shi yanzuma hankalinsa ba'a kansu yakeba. Tunanin wace magana? Khalipha ya sanarma Hajiya iyan yakeyi.
Ganin yanda yayi ɗinne yasa hajiya iya kallonsa a ƙufule. “Saboda an manna maka abinda ka ɓata yasa kaimin shiru Abdul-Mutallab?”.
Yanda ta faɗi real name nashi ya tabbatar masa da har zuciyarta ne. Dan haka ya ɗago ya kalleta, wani ɗan murmushi ya sakar mata yana miƙewa, “Indai nine kamar ki ɓata ranki, duk yanda kikeso haka za'ayi”.
Daga haka ya nufi ƙofar fita abinsa.
Su duka da kallo suka bisa. Hajiya iya dake masa kallon harara tace, “Munafuki kama fito ka faɗa kowa ya sani”.
Babu shiri dariya ta suɓucema Baffah da Mommy, dan yanda Granny tai maganar dolene ta baka dariya. Itako tai kicin-kicin da fuska kamar ba ita ta faɗa ba.
Koda AK ya fita baiko kalli kowa a falonba ya fice, garden ya nufa kai tsaye, yana shiga ya ciro wayarsa a aljihu ya dannama Khalipha kira. Cikin sa'a kuwa ta shiga. Ring ɗaya ana biyu Khalipha ya ɗaga dan yaga sanda Yayan nasu ya fita daga falon kamar a fusace.
“Ka sameni a garden”. Ya faɗa kawai yana yankewa.
Miƙewa Khalipha yayi da sauri ya fice shima sauran yaran na binsa da kallo. Tun kafin ya ƙaraso cikin garden ɗin ya hango AK daketa safa da narwa hannayensa duka biyu goye a bayansa. Sai da ya iso daf da shi sannan yay sallama. Juyowa AK yayi ya zuba masa birkitattun idanunsa da suka gama tsorata Khaliphan a take. Duk yanda yaso daurewa sai ya kasa dole ya risinar da kansa ƙasa. Cikin harɗewar harshe yace, “Yayanmu gani”.
“Na ganka ai”.
AK ya faɗa yana nufar kujera ya zauna. Fahimtar da Khalipha yayi yau a yaya yake ba besty ba sai ya nufesa shima ya zauna kusa da shi cikin rauni.
“Yayanmu wani abu ya faru ne?”.
“Zai dai faru Khalipha”.
Ƙara daurewa Khalipha yayi, dan shi duk tunaninsa ko Yayansu bayason auren Zinneerah ne, duk da yanajin zafin rasata bazai so Yayansu rabuwa da itaba dan sun dace. Duk da kuma yanada mata ya fisu buƙatar Zinneerah a yanzu.
Cikin nuna damuwarsa a bayyane yace, “Yayanmu dan ALLAH miya faru? Wlhy tsoratani kake sakeyi”.
Kamar AK bazai tankaba sai kuma ya gyara zamansa yana duban Khalipha ɗin da ƙyau. Zazzafar iska ya furzar idanunsa na sake rinewa. Kai tsaye yace, “Wace magana kukai da Granny?”.
“Granny kuma? Ni?”.
Khalipha ya faɗa cikin jinjinawa da son tunanowa.
Shiru AK yayi baice komaiba. Hakan ya bama Khalipha damar shiga kundin tunani na tsahon mintuna huɗu. Sai kuma ya duba AK yana ɗan jinjina kansa. “A sanina dai gaskiya babu wata magana da nayi da ita. In badai akan maganar IV......”.
Sai kuma ya kasa ƙarasawa.
Da idanu AK yay masa alamar cigaba. Dole Khalipha ya ɗan haɗiye yawu yana maida kansa kasa. Maganar da suka tattauna da Hajiya iya akan hanyoyin iya samuwar ciki ya sanar masa. Har yakai aya AK baice komaiba, dan tun a fara bayanin ya raba hankalinsa biyu, ɗaya ga Khalipha ɗaya ga nazari da fashin baƙin dukkan kalma ɗaya dake fita a zancen Khalipha ɗin.
“Amma kai miyasa kayi wannan hasashen?”. AK yay tambayar yana duban Khalipha cikin ido.
“Ba hasashe nayiba Yayanmu, kawai dai yanda ita Granny tai maganar hanyoyin iya samuwar cikine sai ta dalili ɗaya yasa nai mata fashin baƙi akai cewar yanzu akwai wasu hanyoyi da suka ɓullo a likitance. Ni wlhy bamma ɗauka zata riƙi maganar serious ba sam”.
Karan farko AK ya saki wani lallausan murmushi da ɗaura hannunsa akan kafaɗar Khalipha ya dan bubbuga tare da miƙewa. Daga haka baice komaiba ya nufi barin garden ɗin yabar Khalipha binsa da kallo.
Sai da ya ɓacema ganinsa sannan ya sauke numfashi shima da ɗaura hannunsa akan kumatu yayi tagumi. A fili ya furta, ‘Anya kuwa nima ban cancanci yin nazari akan wannan batunba. Gashi dai na faɗama Granny ne kawai bada wani daliliba. Amma yanda Yayanmu yay serious a maganar da yanda ya dage akan shi bai aikata komai akan samuwar Abdul-Mutallab ba kamar akwai ruɗani’.
‘Tabbas akwai ruɗani’. Khalipha ya sake faɗa yana miƙewa zaram tamkar wanda aka tsikara. Domin shikam dai akwai abinda dama ya tsaya masa a rai game da cikin da akace aunty Farah na dashi ranar, shi likitane, likitan ma dayake karatu akan matsalolin mata. Amma sam baiga wani alamomin mai ciki tattare da Aunty Farah ɗinba. Anya kuwa Yayanmu da Aunty Farah babu wani abu da suke ayanzu yake ƙoƙarin bayyana kansa da kansa?...........✍
_Sannu-sannu bata hana zuwa, sai dai a daɗe ba'ajeba. Naga wasu sun ƙagara susan yanda aka samu little da zuwan Zinneerah aikatau, karku damu zaku sani, dan kowane al'amari da muhallinsa yake tafiya, idan kuma gaggawa ta shigo sai ya koma ba'akan tsarin dazai birgeba, wata ranama labarin zamu gama baki ɗaya insha ALLAH. Kudaiyi tattalin man kanku karya tsiyaye, al'amarin mai saukine😂. Ina gaisuwa irin trillions ɗin nan.☺️🤝🏻._
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_______________________
*Page 46*
.........Koda akazo yin breakfast yau gaba ɗaya gidan aka haɗu harsu Momie domin nuna murnar dawowar Hajiya iya. Aiko taji matuƙar jin daɗi dan bakinta yaƙi rufuwa. Little na jikinta tana bashi da kanta. Ita Zinneerah ma har mamakin yanda ya saki jiki da kowa takeyi, gashi yanzu ta fahimci dai yana neman zama ɗan gidan. Har ranta tanajin daɗin yanda kowa bai taɓa gano alaƙarta da little ɗinba. Amma idan ta tuna randa zasu iya sanin abin na damunta da sakata a fargaba.
Tunda ta zauna bata yarda ta kalli inda AK yake ba, dan ta samu ta ɗan maƙale ne jikin aunty Safiyya ba sosai ake iya ganinta kamar kowa ba. Garama Huzaifa da yazo zai zauna sai da ya tsokaneta. Murmushi kawai tayi dan ita kam ba iya irin wannan wasan tayiba saboda miskilancin ta. Shima dai ya fahimci miskilarce, hakan ya sashi faɗin, “Like Husband like wife”.
Murmushi su Baffah duk sukayi, yaran kuwa kowa yay ƙasa da kai yana gumtse dariya. Ita dai Zinneerah ba sanin inda ya dosa tai ba. AK kuwa yi yayi kamarma baiji mi Huzaifa ya faɗaba, ya maida hankali gacin abincinsa kawai dan hajiya iya ta riga tai musu sabon idan suka zauna gaban abinci shi kaɗai suke bama dukan nutsuwarsu har sai sun kammala.
Shine farkon tashi, kamar an tsikari little shima ya miƙe daga jikin hajiya iya yana faɗin, “Abbana zanje”.
Yanda yay zaram ɗin ya miƙe da maganar tasa data fita raɗam ya saka kowa yin dariya, banda Zinneerah da aranta take raya (kajimin yaro da shegen ɗafa, wai Abbana).
AK kam dawowa yay da baya yasa hannu ya ɗaukesa yana murmushi, ba komai kesa little na ƙara manne masaba sai yawon da yake fita da shi, shiko yaro dama akwai son yawo shiyyasa duk inda sukaga maza koda basu da wayo suke maƙale musu. Balle little dake da wayo masha ALLAH.
“Sweetheart kaima fa ka iya yawo na lura”. AK ya faɗa lokacin da suke nufar ɗakinsa shi da little.
Mommy dake binsu da kallo ita da Baffah tace, “Ƙuruciyar little tamkar Adnan, har wayon tsiyar ya kwaso bai rageba. Wani irin bugawa ƙirjin Zinneerah yayi a take, har takai ta ɗago ta kalli Mommy batare data saniba. Haɗa ido sukai da Hajiya iya dake kallonta cike da nazari ita, tai saurin maida kanta ƙasa. Harga ALLAH maganar ta daketa shiyyasa duk abincinma ya fita mata a rai.
Ganin yanda taketa faman juya cokali a cikin abincin Hajiya iya tace, “Inno kin ƙoshi ko?”. Da sauri tako ɗaga kanta jin ta samu mafita, kafinma Hajiya iya ta sake cewa wani abu ta miƙe da sauri. Sauran da duk basu san mike faruwaba basu fahimci komaiba. Da wannan damar Zinneerah ta samu ta silale daga wajen ta koma ɗaki.
Tayi zurfi a tunani sosai Hajiya iya ta shigo, harta zauna Zinneerah batasan da zuwantaba, sai da ta gama mata kallon nazari tsaf sannan ta taɓata. Nufashi Zinneerah ta kawo a zabure, sai dai ganin hajiya iya ya sakata sauke ajiyar zuciya da ɗan ƙaƙaro murmushi.
“Granny ashe kin shigo? Bara na ɗauka miki maganinki kisha”. Tai maganar tana ƙoƙarin tashi. Kamo hannunta Granny tayi ta maida ta ta zaunar. Hakan yasa Zinneerah ɗan kallonta. Amma ganin itama kallonta Granny keyi saita maida kanta ƙasa dan kallon ya banbanta da wanda ta sani. “Kamannin Abdul-Mutallab da Moddibo na ruɗaki ko? Muma haka suke ruɗamu a koda yaushe. Sai dai nasan jinine kawai yasa Hauwa'u haifo mai kama da Moddibo”.
Ɗan murmushin yaƙe kawai Zinneerah tayi kanta a ƙasa har yanzu, Hajiya iya taci gaba da magana batare da ta damu da yanayin Zinneerah ɗin ba. “Ki shirya zuwa anjima da yamma hajiya Zulai zatazo ku wuce katsina akwai wani aike da zaku kaimin amma ke da ita kawai zakuje”.
Saurin ɗagowa Zinneerah tai ta kalli Hajiya iyan a karo na farko, dan itafa tama kanta alƙawarin bazata ƙara taka ƙafarta katsina ba saboda tsoron karsu Hajiya su ganta. Duk da a yanzu tafi ƙarfin a ƙara kaita inda aka kaitan, kuma tasan ba gidan yankan kai baneba kamar yanda ƙuruciya ta sata kiran wajen a baya.
Cike da basarwa Hajiya iya tai ɗan dariya, “Oh wai kokin taɓa zuwa Katsina ne Inno?”.
Murya a raunane Zinneerah tace, “Sau ɗaya Granny”.
“Kai, duk da kasancewarki bakatsina? A to karma ki faɗa gaban su Jamal sumiki dariyar Danya kawai kika sani”.
Ƴar dariya tayi saboda yanda hajiya iya tai maganar cike da raha. Batare da tunanin komaiba tace, “Granny ai shima aiki Inna tasa wata mata taje dani nayi bama yawo naje ba”.
“Aiki kuma? Kina nufin aikatau fa kenan?”.
A take damuwa ta bayyana akan fuskar Zinneerah, ƙwalla suka ciko mata idanu, murya a raunane tace, “Eh aikatau Granny, ni bansan miyasa Inna bata sonaba. Dagafa wata ƙawarta tazo ta bata labarin kuɗin da ake samu shikenan tasa na bita ko baba bai saniba. Amma tsabar sharri dana dawo sai tace wai yawon banza naje, wlhy kuma ba yawo najeba”.
“Toke miyasa baki faɗama Babanki gaskiyar abinda ya faruba?”.
“Haka kawai naji inajin tsoro Granny, koma nayi niyyar faɗa masa saina kasa dan Baba tsoron Inna yakeji saboda masifarta wlhy, bama shi kaɗaiba ƴan garinmu da yawa tsoronta sukeji dan jarababbiyace sosai”.
“Kai wannan mata ALLAH ya wadaran halinta, ina daɗi ace miji na tsoronka. To amma ke miya faru har tasa aka tafi dake aikatau babu wanda ya sani, harma ta samu damar miki sharri kinje yawo?”.
Hannu Zinneerah tasa ta share hawayenta daketa sakkowa saboda tuna a yanda tabar Danya wancan lokacin, babu wani tunanin wayon manya Hajiya iya ke mata ta fara zayyana mata yanda abin ya kasance.
“Hajja lanti ƙawar inna ce sosai, dan nidai tare na sansu tunda na fara wayo, dan Hajja Lanti dillaliyace a garinmu, tana kuma saida abubuwa iri-iri. Daga baya kuma ta koma ɗaukar yara tana kaiwa aikatau a birni. Hajja lanti ba sona takeba itama, shiyyasa bana murna da zuwanta gidanmu, dan duk randa tazo da wahala kaga harta tafi Inna bata dakeniba saboda tsaban iya haɗa gulmanta. A wata ranar asabar na dawo daga tallan gyaɗa da riɗi a gajiye na iskesu zaune a tsakar gidanmu suna magana da ban san kota micece ba. Ni dai na gaidasu na bama Inna kuɗin tallar na shige ɗaki dan tace karna sake zama a tsakar gida idan tayi baƙi. Ban jima da shiga ba ta ƙwalamin kira. Koda na fito sai da suka gama min kallo na wani lokaci ne naji hajja Lantin na cewa “Ai wannan ma itace dai-dai a yanzu. Dan za'a jima ana samu tattare da ita”. Bansan ina zancen nasu ya dosaba. Ni dai Inna tacemin naje na canja kaya nawuce can bakin ɗorawar kan hanya na jira Hajja Lanti zamuje anguwa. Ban musa mataba naje na canja kayana na fito, saita sake korani da cewar naje na saka kayan sallata. Zuwa nai na sake canjo kayan na fito, a gabansu na tafi inda tace naje na jira hajja Lanti ɗin. Na jima a bakin ɗorawa zaune sannan hajja lanti tazo ita da wasu yara da ban sansu ba. Batare da itama tamin bayaniba ta bani hijjabi da nikab wai na saka. Nidai ban musa mataba na saka. bayan na sakane ta kira masu mashin su uku suka daukemu