Showing 105001 words to 108000 words out of 237912 words
Chapter 36 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt
da kallon fuskar tasa kawai tsoro take bata ma. Zatai magana ya katseta dan yasanta da shegen naci da mita akan abu, “Ki kwaso duk kayanki na ɗakincan tunda ba amfani kike da shi ba su zauna. Jamal ya zauna wajen Khalipha”.
A zabure ta miƙe tsaye tana dubansa hawaye na rige-rigen sakko mata. “Haba Yah Abdul-Mutallab, ɗakin nawa zan basu?”.
“Zama ɗakin kikeyi ne?”.
“To amma dan ALLAH kodai bana zama a ciki ai dai sunansa ɗakina. Suje ɗakin Granny su zauna mana”.
Wani banzan kallo ya mata idanunsa na sake canja kala. “Wlhy Farah idan kikace zaki bani ciwon kai akan zuwan yarannan tabbas zan baki ciwon zuciya ni kuma. Garama tun muna mu biyu kije ki kwaso abinda yake naki a can ki basu ɗakin, idan kuma kinƙi zakisha mamakina dan ina nan Abdul-Mutallab ɗin ɗin da kika sani”. Yana gama faɗa ya fice abinsa.
Khalipha kawai ya samu a falon, Granny taja su Zinneerah zuwa ɗakinta. Jamal kuma Khalipha ya kaisa nasa ɗakin. Duk ƙoƙarin ɓoye fushinsa da yake sai da Khalipha ya gane. Har cikin ransa baiji daɗiba. Shiyyasa yaso Yayan nasu ya haƙura da batun zuwan yaran tunda ba dole bane. Dan yasan Farah ba zataso suzo ɗinba. Tunda shima a yaya yake zaune gidan ma. Ita kanta Granny ɗan hali Farah ke nuna mata duk da tsufanta.....
“Ina suke?”.
Ya katse Khalipha muryarsa cike da ɗaci. Cike da son kauda masa damuwarsa Khalipha ya miƙe yana dariya. “Ai Yayanmu kasan waɗanan yaran ƴan gatan Granny ne. Ta jasu ɗaki wai suyi wanka da barci. Shima Jamal yana wajena”.
Goshinsa yaɗan murza da furzar da huci yana lumshe ido. Batare da ya samu yanda yake so na daidaiton muryar tasaba ya nufi ɗakin yana cewa, “Taya zasu zauna a wannan ɗakin harsu huɗu zasu takura mata ai”.
Bin bayansa Khalipha yay yana magana cike da lallashi. “Yayanmu daka barsu isarsu zaiyi ALLAH, kaga munma huta da mitar Granny akan kaɗaici ko”.
“Bazai yuwuba Khalipha ɗakin Farah zasu koma”.
Dama abinda Khalipha kema gudun kenan. Ya ƙara buɗe baki zaiyi magana a dai-dai isowarsu ƙofar ɗakin AK ya ɗaga masa hannu alamar ya isa. Kai Khalipha ya dafe dan harga ALLAH baya buƙatar wata fitina akan zuwan yaran nan tsakanin yayan nasu da matarsa. Idan ta gaskiya za'abi sune da laifi, gashi kuma dama ba'a sanar mata ba tun farko. To amma yasan halin Yayan nasu tunda yace haka za'ayi dole a yarda ayi hakan”.
Daga can Granny tace, “Khalipha shigo mana”. Dan batai zaton AK ɗin baneba. Batare daya nuna shi ɗin baneba kuma ya murɗa ƙofar ya shiga da sallama ciki-ciki. Akan Zinneerah data fara wanka harta kwanta ya fara sauke idanunsa. Ya janye yana maidawa ga Granny dake gyarama Meenal kwalar riga. Bahijja kuma na toilet tana wanka.
“A'a wai dama baka komaba?”.
Hajiya iya ta faɗa idanunta akan AK. Kansa kawai ya kaɗa mata yana kaiwa zaune. “Yanzu zan koma Granny, akan waɗannan dama na shigo, su koma can ɗakin ba'anan zasu zauna ba”.
Shiru tai tana kallonsa cike da nazari, sai kuma ta saki murmushi tana girgiza kanta. “Moddibo bazai yuwuba. Ka barsu anan muyi zamanmu zai ishemu”.
A karon farko ya kalleta shima. Ta kaɗa masa kanta da iya gaskiyarta tace, “Idan akai hakan ba'a ƙyautaba Moddibo. Inda itace taso su zauna mata a ɗaki dan kanta hakan ba damuwa bane. Amma ko nice miji yayma ƙarfa-ƙarfa akan danginsa su zauna min ɗaki zanga kamar an ƙasƙantar da nine. Ka barsu kawai suyi zamansu nan zai ishemu duka zaman kwana nawane ma”.
Bai iya yace mata komaiba, sai idanunsa dake ƙara canja launi ɓacin ransa na bayyana a fili, miƙewa yay a hankali batare da ya sake kallon kowansuba yace, “Saina dawo”. Daga haka ya fice yabar ɗakin..
Da ga hajiya iya har Khalipha da su Meenal da kallo suka bisa suma damuwa fal ransu. Suna son Yayansu dan shima yana son su. Ko rashin sakewarsa a garesu kowa yasan wannan halinsane da kuma yanayin rayuwar daya tashi a hannun Mahaifiyarsa. Amma sunsan badan ƙuntatawa a garesu yake musu hakaba.
Afusace Meenal tace, “Wlhy na tsani matarnan, danma taga ta samu Yayanmu mai haƙuri dajin maganar iyayensa shiyyasa takema mutane wani iskancin”.
“Barta hankali zamu koyama shegiya ai a wannan karon, tunda ta yarda mukazo gidan nan wlhy tayi gamo da gamonta kuwa”. Cewar Bahijja itama muryarta har zuga take.
Rai ɓace Hajiya iya ta kallesu tana musu daƙƙuwa. “Duk kunci iyayenku, ina ruwanku a cikin wannan zancen? Kunsan ALLAH duk wanda ya aikata wani abu a gidannan saina ɓata masa rai kuma ya koma gida. Ina kuma sake gargaɗinku shiga abinda ba'a sakakuba. Wannan ma ai rainine. Koyaya take ai matar Yayankuce taci albarkacinsa a wajenku marasa kunya”.
Duk ƙasa sukai da kawunansu alamar nadama. Dan dama sunsan wannan ba tarbiyyarsu bace. Hasalima Hajiya iya bata yarda da irin wannan maganar a gabansu, yau ma dai akasi aka samu. Haƙuri suka bata. Shima Khalipha ya ƙara musu faɗa sannan yace suzo suci abinci shima zai wuce school ne.
Duk wannan abin da sukeyi Zinneerah najinsu sarai, amma tai shiru kamar barci takeyi. da Khalipha ma yace a tadata taje cin abincin Hajiya iya hanawa tai. Catai su barta idan ta tashi sai taci nata tunda ta riga tayi barci.
A ɓangaren AK kuwa koda ya fito daga ɗakin hajiya iya ɗakinsa ya sake komawa. Zaune ya tarar da Farah da waya a hannu kamar ba ita ta gama kukaba yanzun. Ko'a jikinsa dan ya shirya mata tsaf, ya kuma san Mammah bazatazo gidanba dan yunda Hajiya Iya ta dawo daga asibiti taƙi zuwa, dama kuma ko asibitin bataje ta dubataba. Yanzu hakama tana China batare da sanin Farah ɗin ba, dan shekaran jiya ta wuce da daddare.
“Ki tashi ki tattara komanki dake a ɗakin nan ki maidashi ɗakinki. Karna dawo na taddaki anan ko wani abu naki”. Daga haka ya juya ya fice abinsa bai jira cewartaba.
Fuskarta bayyane da tsantsar mamakinsa ta bisa da kallo. Yana fita ta miƙe a fusace dayin wurgi da wayar hannunta. ‘Ni zaka wulaƙanta akan waɗanan banzayen ƴan uwan naka Abdul-Mutallab? Saboda nace bazasu zaunamin ɗakiba kaima zakace na bar maka ɗakinka bayan kasan nafi son zama a cikinsa. Na rantse da ALLAH sai yaran nan da tsohuwarnan sunbar gidannan zan baka mamaki kai dasu. Bazan sake zubar da hawayena akansu a banzaba mu zuba mu gani’.
Yanda take surutai ita kaɗai a kuma matuƙar fusace sai ta baka dariya. Ta koma tamkar wata zararriya. Sanin halinsa yasa bata ƙetare maganarsaba ta shiga tattare duk wani abu nata tana saka mai aikinta tana kaiwa ɗakinta. Sai dai kuma alwashin ƙuntata su Hajiya iya a gidan tacisa yafi sau shurin masaƙi.
Bayan ta gama tattare komai nata tsaf ta saka mai aikin nata sake gyara masa sannan ta jawo masa ɗakin ta rufo harda saka key.
Su dai duk wannan abu dake faruwa su Hajiya iya basu saniba suna ɗaki abinsu tana hira da jikokinta. Abincin ma anan sukaci kusa da ita har Jamal da yana gama kimtsawa ya tafi can. Shiko Khalipha ya wuce school kamar yanda ya faɗa.
________________★
*_DANYA_*
Su inna sun kai Karima asibitin kusada. Likitocin nata faɗa ganin yanda jikinta ko ina sayin duka ga tsohon ciki da a yau ma yaketa nuna alamun zai fito duniya. Dan tunkan su wuce ashe naƙuda take shiyyasa jikin nata ya nema rikicewa.
Ɗakin haihuwa suka kaita dan shine yafi cancanta da ita a wannan halin. Daga haka suka shiga bata taimakon gaggawa. Suka bar su Inna a waje da zaman jigum-jigum. Tun suna zuba idanun jiran kukan jariri da wuri har al'amarin ya fara fin ƙarfinsu. Dan ihun Karima kawai suke jiyowa babu na jariri. A haka suka cinye wannan yinin suka shiga marece. mahaifiyar Babawo sai kiransa take a waya yaƙi ɗauka. dan tunda ta sanar masa abinda ke faruwa kafin su baro Danya bai sake yarda ya ɗaga mata wayaba. Dole sai ƙaninsa keta kaiwa da kawo akan komai har ALLAH ya sauki Karima wajen ƙarfe goma na dare.
Tsabar wahalar data sha daga ita har jaririyar sun fita hayyacinsu ko kukan kirki batayiba. Koda aka buƙaci kayan haihuwa babu abinda sukazo dashi asibitin. Aiko Nurse ta balbalesu da masifa dan haushi. Inna ta miƙe itama a fusace tana danƙarama Nurse zagi abu ya nema zame musu faɗa sai da aka lallashi Nurse ɗin da ƙyar. Dan sun fahimci Inna ma ba kanwar lasa baceba.
Wannan abin daya faru yasa gari na wayewa aka basu sallama suka dawo gida duk da Karima na buƙatar zama ƙarƙashin kulawar likita. To amma jarabar Inna bazaisa su iya cigaba da kulawa da Karima ɗin cikin kwanciyar hankaliba dan haka suka sallamesu..........✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 31*
_________________________
_*LAVENDER RESTAURANT..*_
_(Palace of mouthwatering food/delicacies)_
_IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_
_*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE.._*
_*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.._*
_*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283 akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021 to 3/10/2021 Nigeria @ 61_*
_*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU._*
_*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN. _*
_*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇🏾RIGIJI GABJI_*
_*Nigeria @ 61 _*
_*COOKING COMPETITION!!!_*
_*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine da wasu prize suma saura kuwa zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar_*
_*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA_*
____________________
*Page 31*
..............Farah na kammala bin dokar AK na komawa ɗakinta shiri tai ta fita zuwa gidan Mammah, a garin suke amma ba'a street ɗaya suke ba. Su Hajiya iya basusan bata a gidanba sunata hidimarsu. Sai dai su duba lokacin salla su tashi suyi su koma tebirin hira. Sai da Khalipha ya dawo shima ya zauna suka ɗora cike da farin ciki.
Sunata zuba idon ganin dawowar AK gidan amma shiru, dan har lokacin dawowarsa aiki ya wuce babu shi. itama kuma Farah ɗin dawowar Khalipha gidan ya fahimtar dasu ta fita. Dan mai aikinta ta gama duk wani aikinta na wannan ranar ta tafi itama. Sai ya kasance sai su kaɗai ne a gidan kawai. Gajiya ta saka su Zinneerah kwantawa da wuri suka bar Yah Khalipha da Hajiya iya zaman jiran shigowarsa amma shiru.
Hankalin Khalipha ne ya fara tashi, duk da yasan bawai wani abune ya samu yayan nasu ba, bazai wuce dai ɓacin rai ya hanashi shigowa gidan ba. Miƙewa yay ya fita domin zuwa can ma'aikatar tasu ya dubashi ko yanacan idan bai tafi gidan Mammah ba, tunda yaga gimbiyar gidan da alama itama tana can. Zuwanta canɗin kuma bawai zai haifar da ɗa mai ido ba ga Yayansu, dan sai ta masa haɗin da sai Mammah ta ɓata masa rai musamman daya kasance itama akan abinda bata farin ciki da shine tunda itama Farah ɗin ai karatunta take bi. Tun farko an nuna mata su ɗin basu da muhimmanci da mutunci shiyyasa take kallonsu a hakan
Kusan a lokaci guda AK da Khalipha suka ɗora hannyensu akan handles ɗin ƙofar, shi da nufi fita, shi kuma da nufi shingowa. Sai dai AK dake ƙoƙarin shigowar ya samu nasarar turo ƙofar. Baya Khalipha yaja yana sauke ajiyar zuciya. Hakan yasa Yayan nasu binsa da kallon mamaki.
“Lafiya kuwa? Ina zakaje?”. Yay maganar yana kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa da duban Khalipha ɗin.
Cikin damuwar ganin yanayinsa Khalipha yace, “Yayanmu dama kai zanbi hankalin Granny duk ya tashi da rashin dawowarka akan lokaci.
Duk da damuwar dake tattare da fuskarsa da zuciyarsa sai ya saki guntun murmushi kawai yana miƙama Khalipha ɗin kayan hannunsa. Shi kuma ya hau zame coat ɗin saman sult ɗinya yay hanging ɗinta. Takalman ma ya zame ya ajiyesu a ma'ajiyarsu ya saka Slippers ɗin shiga cikin gidan. Batare da yanzuma yay maganaba ya nunama Khalipha hanya alamar suje.
Tunda suka shigo falon idon Hajiya iya na a kansa. Shima inda take ya nufa kai tsaye, batare da yayi maganaba ya zauna kusa da ita yana sauke numfashin gajiya da lumshe idanunsa. Hannunsa hajiya iya ta kamo cikin nata tausayinsa da ƙaunarsa na ratsata. Batare da ta damu da sanin matsalarsaba ta fara magana cikin lallashi.
“Bansan yaushe ka fara zama mai rauni hakaba Moddibo? Dan nidai moddibo dana sani ada mai yawan haƙurine da juriya da kawaici akan al'amuran rayuwa. Sannan ba komai yakema zafi ba sai yayi nazari akansa”.
Lumsassun idanunsa dake cike da gajiya dason yin barci ya buɗe yana ɗagowa zaune sosai, ɗayan hannunsa ya ɗora kan nata yana dubanta cike da sonta da ƙaunarta. cikin muryarnan tasa mai tarin kamala da rashin sakewa yace, “Har yanzu Moddibonki na a yanda kika sanshi Granny. Abinda kike tunanin ba shine damuwarsa ba”.
“Miye damuwarka idan ba matsalar matarkaba to Moddibo?”.
“Haba Granny, ni yanzu har akwai wata matsala ta Farah da zata sakani a matsala? Wlhy sam ba itace tushen damuwataba. Ɗazunma ta taka sahun ɓarawone kawai shiyyasa kika ganni kamar a cikin zafi. Wani ɗan matsalane akan business insha ALLAH kuma komai zai dai-daita ki tayani addu'a”.
Sosai Hajiya iya ta gamsu da maganarsa. Dan tasan shi mutumn kai tsaye da bai iya ɓoye-ɓoye ba ko ƙarya akan abinda ba haka yakeba. Tunda yace ba Farah bace matsalar da gaske ba itaɗin baceba. Ajiyar zuciya ta sauke tana sake kammo hannun nasa cikin nata. Da kulawa tace, “Muna muku addu'a a koda yaushe Moddibo, kuma zamu ƙara insha ALLAH. Duk wanda ya manta da ALLAH shike ambato yaya zaiyi”.
Murmushi yayi dake bayyanar da gajiyarsa mai sanyi, ya jinjinama Hajiya iya kai yana duban Khalipha dake murmushi shima, “Hakane Granny, shiyyasa a koda yaushe nakeson kasancewa a tare dake. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsahon rai mai amfani”.
“Amin ya rabbi”. Ta faɗa tana murmushin itama da shafa kwantaccen sajensa.
Mikewa yay yana faɗin, “A gajiye nake Granny, bara naɗanje na kwanta ina baƙin naki ne?”.
Khalipha ne ya bashi amsa da cewar, “Tab Yayanmu ai duk sunyi barci. dan Beauty ma da tafi kowa ragantaka tariga kowa kwanciya”.
Kallon Khalipha yay gira a ɗage kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa. Gaba yay a binsa murya a cinkushe yace, “Sai da safenku nidai nayi ciki”.
Da ALLAH ya