Showing 15001 words to 18000 words out of 237912 words

Chapter 6 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt

27 Nov 2024

23399

cikinne ai sai kuyi mata lahani ita da shi k.......”
“K Halima bamu son tsarin banza da wohi. Kinason hiɗin ita Yaya Ladi ƙarya tayi kenan da tace akwai cikin? Bayan duk wanda ya kalla wannan sheɗaniyar yarinyar zai tabbatar da alamomin mai ciki tattare da ita...”
“Ba haka nake nihi ba yaya Asabe. Tayaya zan ƙaryata Yaya Ladi ni kuwa. Ni dai ina nuna maku muhimmancin bin komai a sannune. Yanzu wannan ruɗama yarinyar tunani da bugun nata da akeyine zaisa ta hiɗi gaskiya? A ganina idan anbi komai a sannu sai a kamo gaskiyar al'amarin da mahwarinsa basai anbi hanyar ilatata ba a dawo kuma ana dana sani”.
Inna zata sake magana Yaya Gajeje ta katseta. “Maganar Gwaggo Halima gaskiyane. Ya kamata mubi komai a sannu kawu. Dan kowa yasan halin Zinni bazata aikata wannan al'amari da ganganba inma har ya tabbata hakane. Ba muba ko jama'ar gari idan zasu hiɗi gaskiya sunsan Zinni yarinyace mai nutsuwa da haƙuri. Wlhy inaji a raina inhar da gaske ciki ne a jikin Zinni sai dai ɗayan biyu ne ya hwaru. Kodai wani la'ananne ne yay mata wayo ya ɓata mata rayuwa. Ko kuma acan inda ta baro wani yay mata hin ƙarhi ya aikata mata wannan zaluncin. Ku tunafa yarinyarnan nemarta akai aka rasa rana tsaka. sai kuma gata ta dawo babu zato. Abin mamaki kuma tamkar an rihe mana bakuna har yanzu bamu sake bi takanta muji yaya akai tabar garinga ba ta kuma dawo? Miya hwaru da ita data tahi? Ina taje? Waye silar hitar tata? Duk bamu binciketa b..........”
“Gajeje!!!”
Inna ta faɗa da wata irin mahaukaciyar tsawa tana nunata. Ta cigaba da faɗin, “Na rantse da ALLAH idan baki hita batun wannan ƴar iskar yarinyar ba daga yau sai na tsine maki a gidan nan ke da Sa'a. Har uban waye zai hiddata a gida da gari banda abokan iskancinta wanda ga sakamakon abibda takeyi ɗin nan ya bayyana kowa ya gansa”.
Dubanta Gajeje tayi zatai magana. Sai kuma mita tuna oho tai shiru kawai tai ƙasa da kanta tana sharce hawayen dake sakko mata.


Har dare gidan ya gagara komawa dai-dai. Zinneerah kam tana can ƙuryar ɗakinsu ta ɓuya tana cigaba da kukanta. amma duk da haka bata kasa jiyo yanda ake aibantata a tsakar gidanba ita da mahaifiyarta a bakunan wasu a cikin dangin Inna. Yayinda ƴammata masu zaman ƙunshin Karima suka fara raira mata waƙa cikin habaici da izgili kamar yanda Karima ta sakasu.
Babu wanda ya hanasu, dan Yaya Gajeje tabar gidan tun ɗazun. Baba kuwa yana zaune daga can bayan runbunsu shiba mai rai ba shiba gunki ba. Sam zuciyarsa da ƙwaƙwalwarsa basa aiki irin na mutane.
Duk da ƙarancin shekarunta yinin yau ya sake tabbatar mata da rayuwa ta sake kaita wani ajin jarabawar da yafi zaman gidansu ƙunci da tashin hankali. Ita dai ko Al-qur'ani aka bata zata iya rantsewa da shi akan bata taɓa aikata iskanci ba, amma sai gashi yau an wayi gari ita ake kira da suna mai ciki, cikinma cikin shege. Ta sake fashewa da kuka mai cin rai.


★★★


Zamu iya cewa a wannan dare barci ɓarawo ne kawai ya saci Zinneerah kasancewarsa gwanin iya sata. Amma badan taji sha'awar yinsaba ko buƙata.
A kiran sallar farko ta tashi, taji daɗin jin gidan shiru alamar kowa bai tashiba. Ta lallaɓa ta fito zuwa bayi. Bayan ta kammala lalurarta tai alwala ta sake shigewa ɗakinsu. Daga haka bata sake fitowa ba har sai da rana ta haska. Zuwa lokacin gidan ya cika da hayaniyar baƙi da yaransu. Kamar jiya dai kowa da zancen cikin nata ya tashi a baki, hakan yasa ta sake maƙurewa a ɗaki taƙi fitowa.
Tana zaune kanta cikin gwiwarta taji muryar Gwaggo Laritu ƙanwar su baba na kiran sunanta. Kanta ta ɗago muryarta data sha kuka a dusashe tana amsawa. Fuskar Gwaggo Laritu a haɗe tace, “Taso ki hito”.
Sosai gabanta ya faɗi, sai dai babu damar musu dole ta miƙe tana rangajin yunwa da damuwa. Kamar jira ake ta fito tsakar gidan yay tsit idanu caahh a kanta. Tai ƙasa da kai zuciyarta na tsitstsinkewa dan tashin hankali...
“Munahika, ƴar iskar yarinya. Ƙyahwa ta duƙar da kai kamar balamar tunkiya tunda kin kwaso mamu abin kunya”.
Inna ta faɗa tana jan tsaki. Ita dai Zinneerah kanta a duƙe bata yarda ta kalli kowaba. Ta kuma kasa ɗaga ƙafarta dan batasan ina zata dosaba.
Sa'a ce ta taso daga inda take zaune tazo ta kama hannunta, itama muryar tata a dasashe alamar tasha kuka tace, “Muje Zinni, su baba na jiranki a zaure”.
Da ƙyar ta iya ɗaga ƙafafunta tabi Sa'a har zauren. Baba na zaune shi da su Kawu Haruna. Ƙasa ta zube cikin rawar murya tana gaishesu. Babu wanda ya karɓa mata, sai Gwaggo Laritu ce tace, “Ya kamata mutahi kar rana tai tsaka tunda ta hito”.
Nanma babu wanda ya iya cewa komai, sai miƙewa da su kawun sukai amma banda Baba da kansa ke ƙasa. tunda Zinneerah ta fito ko motsi baimayiba. Koda sukai masa sallama zasu tafinma bai motsa ba. Bai kuma ce uffanba har suka tasa Zinneerah gaba suka fice.
Mashina biyu dake jiransu suka taras a ƙofar gida. Kawu Sabi'u da Kawu Haruna suka hau ɗaya. Ita kuma da Gwaggo Laritu suka hau ɗaya batare da tasan ina suka nufa ba.
Ƙasa zinneerah tai da kanta har suka baro cikin garin Danya. Wanda tasan tunda kasancewar safiyane kowa yaga tahowar tasu, waɗandama basu ganiba zasu samu labari ga waɗanda suka gani ɗin.

Har cikin Kusada masu mashinan nan suka kaisu babban asibitin Kusada. Kasancewar ɗan mashin ɗin daya goyo su Kawu babban ɗan Kawu Sabi'u ne shine yay musu shige da ficin komai har suka sami ganin likita kusan sha ɗaya na rana. Duk da a matuƙar tsorace Zinneerah take bataƙi amsa tambayar da duk likitan yay mata ba. Bayan ya gama mata tambayoyin yasa aka kira masa wata matashiyar budurwa. Zinneerah ya nuna mata yana faɗin, “Maryam kuje da ita tai hitsari akaima Bashir”.
Budurwa daya kira da Maryam ta amsa da to a girmame tana duban Zinneerah. Tashi Zinneerah tayi ta bita zuciyarta na ƙara shiga damuwa da firgici. Bayan ta kaita wani banɗaki tayi fitsari a wata roba suka fito. Zinneerah wajensu Gwaggo Laritu ta dawo. ita kuma Maryam ta tafi cika umarnin likita.
Sunyi zaman kusan mintuna arba'in Maryam tazo ta wucesu zuwa ofishin likita. Dansu tuni sun dawo waje sunba sauran marasa lafiyar damar shiga suma.. Kusan mintuna goma Maryam tazo tai kiransu.
Kamar ɗazu daga ita sai Gwaggo Laritu suka shiga. bayan sun zauna likita ya dubesu da murmushi yana faɗin, “Masha ALLAH mamana ga sakamakon gwajin hitsarin da mukai mata ya hito. Duk da dama dai kafinma hakan na fahimci ciwon na ƙanwata abin so ne. Amma duk da haka dai nafi yarda da'a gwada ɗin......”
Cikin ƙosawa Gwaggo Laritu tace, “To madallah, mike damunta?”.
Sake faɗaɗa murmushi likita yay yana duban Zinneerah da kanta ke a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta. “A'a Inna ba wani abu baneba face ƙaruwa muka samu. Tanada ciki na kusan watanni huɗu. Kuma Alhmdllh yana cikin ƙoshin lafiya kamar yanda itama alamomi suka nuna tana cikin ƙoshin lafiya, sai dai kuma ya kamata a ringa kula da abincin da zataci saboda shima yaron cikin nata ya samu nagartaccen raino.......”
Sam Gwaggo Laritu da Zinneerah ba fahimtar bayanin likitan sukeba tunda ya ambaci ciki. Dan Zinneerah ma wani irin hajijiya take gani. Tun ofishin na juya mata har ta koma ganin duhu a cikin idanunta. Sai kawai ganinta sukai a ƙasa daga ita har kujerar robar da take zaune a kai.
“Ya subahana”. Doctor ya faɗa yana zabura saboda faɗuwar Zinneerah. Hakan kuma yay dai-dai da dawowar Gwaggo Laritu datai suman wucin gadi itama hayyacinta. Yayinda su Kawu Rabilu suka shigo da gudu saboda jin sallalamin da likita da budurwar nan Maryam keyi akan Zinneerah da alamomi suka tabbatar da suma tayi............✍




“Hummmm!!!! Turƙashi, masu karatu wannanfa shi ake kira da ANA DARA GA DARE YAYI. shin yaya akai hakane? Yaya kuma za'ai? Mi kuma zai faru?. Gadai likita ya tabbatar da ciki a jikin Zinneerah baiwar ALLAH. yayinda Zinneerah ta tabbatar mana kuma bata taɓa iskanci da kowa ba. Shin tayaya aka samu ciki idan babu mahaɗi? Shin wanene uban wannan cikin? Ta yaya aka samar dashi? Da sanin Zinneerah ko fyaɗe ne? Mi Inna ta sani akan barin Zinneerah gida? Anya kuwa babu lauje cikin naɗi masu karatu? Ina mahaifiyar Zinneerah? Yaya Baba zai kasance da tabbatuwar wannan cikin dake jikin ƴarsa dake a matsanancin rayuwa a gidansa? Yaya jama'ar garin Danya zasu cigaba da ɗaukar Zinneerah yanzu? Yaya rayuwar Zinneerah zata cigaba da kasancewa a gidansu da garinsu?.


Wannan amsoshin duk suna ƙumshe a cikin littafin MAKAUNIYAR ƘADDARA da zai zo muku akan naira 300 kacal insha ALLAH. Dan girman ALLAH ina roƙonki ƴar uwata. Kibi ta hanyar data dace domin mallakar naki cikin kwanciyar hankali. Idan kin zama mai shigewa gaba wajen girmama sana'armu kema sai ALLAH ya ɗaga darajar taki komai kanƙantarta. Idan kin zama jagora ko mai burin ruguzamu UBANGIJI ya fimu sanin ke wacece.. Fatanmu kowa ALLAH yay riƙo da hannunsa akan neman halak ɗinsa. Dan ALLAH kuzo ku saya kafin ku karanta. Dan ALLAH idan kin saya karki zama ɗaya daga cikin masu fitar mana dan kawai ganin mun koma baya ko kuntata mana. Ku tuna da tarin alkairinmu na baya gareku, koda bazaku rama manaba karku cutar damu dan girman ALLAH mun roƙeku dan shine kaɗai zamu iya haɗaku da shi🤓🙏🏻.


ALLAH kai mana jagora. Yanda zamu fara lafiya ALLAH ya bamu ikon gamawa lafiya. Masoyanmu da basu gajiyawa wajen sayen hajarmu da mun fitar muna sake godiya a gareku, ALLAH yabar zuminci. Masoyanmu da basu taɓa sayaba kuma ku garzayo dan bana Zafafa shiri sukai na musamman domin farin cikinku. Masu jira a fiddo ku karanta kuma dan ALLAH kuzo ku biya ku mallaki naku a wannan karon kuma sai ALLAH ya kawo muku Customers akan naku kasuwancin. Mun gode. Mun gode irin trillions ɗin nan😘😍😘😍🤗😊😉.


*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_TYPING📲_*




*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*




*Page 6*


_________________________


Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗


Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali
Ina masu pimples
Tabo(spot)
Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance
Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba


Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki


Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu


Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself
100%tested nd trusted


Soap price:3k
Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free


Maiso kindly message 08062991549
Call 08064532391


Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏


Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝


Mg's skincare


Mg's bakery
You can still order ur birthday cake, cupcake,slice cake,meat pie,shawarma,samosa nd spring rolls for ur event @mg's bakery
Kindly call or chat
07046881166
07067210195
08062991549


Masu bukatar abayas,takalma da jakunkuna,ashobe,laces d atamfofi, materials nd the rest
07046881166
👏🤝






Page 6


.........Tun bayan wucewar su Zinneerah kusada Inna ta kasa zaune ta kasa tsaye. Ba komai ke mata kai kawo a rai ba sai maganar Gajeje da take cewa babu wanda ya binciki Zinneerah yaji ina taje. Idan har bata ɗauki matakiba to lallai abinda bata buƙatar ya fito da ga bakin Zinni shine zai fito, dan suna dawowa gida kowa zaiso jin ina taje ɗin? Yaya akai kuma ta dawo?.
Tsulum ta miƙe da ga zaman da tayi a bakin gado, ta rarumo yamutsatstsen gyalenta daketa tsamin dauɗa. Tana ƙoƙarin warwaresa ta yafa Magajiya ta shigo ɗakin...
“A'a, Asabe ina zuwa kuma?”.
Ɗan duru-duru tayi na alamun rashin gaskiya. Sai kuma tai saurin faɗin, “Uhm Magajiya zanje nan ƙauyen kwangi ne na amso kuɓewar dana bada a daka saboda miya. Na sha'ahwa gaba ɗaya sai yanzu na tuna. Gashi Atine tace tuwo aka ɗora yanzu da za'aci da rana. Kinga kuma dole ne miyar ɗaurin aure ma na gobe a haɗa da miyar yauƙi dan taushe ɗin nan ba isa zataiba”.
Kai Magajiya ta ɗan kaɗa mata, sai kuma tace, “Amma nikau da dai kin aiki ko Tinene ko Sa'a mana. Ke da mutane keta shigowa kuma ace kinje wani waje ai babu daɗi. Sannan waɗanan masu tahiya asibitin ya kamata ki jira kiga dawowarsu ko”.
Nannauyan numfashi Inna ta sauke tana ƙyaɓe fuska. Tace, “Kinga Magajiya hita batun waccan watsatstsiyar yarinyar. Dan babu mai ɓata mani taro aradu. Maganar amso kuɓewa kuwa gara naje da kaina. Dan daga Tinene har Sa'a mashiririta ne da kike ganinsu”.
Magajiya tace, “To ni haɗani da Tinenen muje. Ai in dani dai batacewa bata zuwa ko?”.
Sosai wani irin tuƙuƙin baƙin ciki ya turniƙe zuciyar Inna. Ji take kamar ta kaima Magajiya duka. Da ƙyar ta shanye abinda ya tokare maƙoshinta ta ƙaƙaro murmushi dan tasan nacin Magajiya batun yanzu ba. Tace, “To nahi yarda da wagga shawarar kau. Bara naga giccin Tinenen saina hiɗi maki ku tahi”.
Da to Magajiya ta amsa, tare da ɗaukar buhun da garin masara ke ciki wanda dama shita shigo ɗauka ta fita. Da wata muguwar harara Inna ta raka bayanta tana jan tsaki. Ta sauke gyalen nata tana ƙudundunesa ta cusa cikin lalitar bujenta na ciki. Ganin ya kwanta babu mai ganewa ta fito a ranta tana ayyana. (Ai idan kinsan wata bakisan wataba magajiya).
Shigewa tai cikin masu hidimar aikin abinci ta cigaba da harkokinta. Sai da taga kowa hankalinsa baya kanta tai wuff zuwa bayinsu tabi ta cikin dannin geza da akai musu sakamakon zubewar katangar bayin lokacin damuna daya wuce. Har yanzu kuma ALLAH baiba baba damar gyarawa ba.
Saurin zaro gyalenta tai ta warware ta aza bisa kai. Cike da sauri da sassarfa ta dinga ratsawa ta cikin gonaki dan kar wani ya ganta........


★★★★



A asbiti kam bayan tabbatar da Zinneerah ba suma tayi ba ruɗanin maganar likitace kawai ta haifar mata da hajijiya sai suka saka mata ƙarin ruwa. Hankalin su Gwaggo Laritu bai kwanta ba sai da likita yay musu bayani.
“Ku kwantar da hankalinku tana cikin ƙoshin lafiya. Kuma Alhmdllhi bama suma tayiba. Yanayin da take cikine ya kawo hakan, da alama kuma ko karin kumallo bataibama kuka fito”.
A kusan tare suka sauke ajiyar zuciya. Rabilu yaron Kawu Haruna daya kawosu yay saurin faɗin, “Likita to ko za'a samo mata wani abune taci?”.
“Eh za'a iya. Amma a yanzu dai mun saka mata ƙarin ruwa ta samu barci. a cikinsa kuma akwai abinda zai taimaka mata akan yunwar, da alama dai kai ne mai-gidan nata ko?”.
Murmushi kawai Rabilu yayi batare da ya amsawa likitan maganarsa ba. Sai dai Cikin ƙarfin hali duk sukai masa godiya. Amma a ƙasan ransu su kaɗai sukasan irin tashin hankalin da suke ciki game da wannan ciki na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login