Showing 162001 words to 165000 words out of 237912 words

Chapter 55 - MAKAUNIYAR KADDARA!! BY BILYN ABDULL CE.txt

27 Nov 2024

23385

zamansu nan su biyu hartaji gaskiyar zance akan little. Dan ba ƙaramin yaƙi zatai da zuciyartaba wajen bin shawarar Mahma akan ta kwantar da hankalinta wajen AK.
Shiko AK duk da abinda tai masa naƙin bin umarninsa datai ta koma haka ya danne yay mata tarba data bata mamaki. Daga ƙarshema suka shiga duniyar soyayya. Biye masa tayi da ƙoƙarin danne damuwarta, amma duk da haka sai da ta tambayesa ina ya samu gida?.
Murmushi kawai yay mata da kissing goshinta, a AK ɗinsa data sani mai tattalinta da bata kulawa ya amsa mata da cewar, “Gidanki ne da baƙyason zuwa, ina fata dai komai ya miki?”.
Fuska taɗan ɓata tana gyara kwanciya a jikinsa, “My hero ko yamin miye amfaninsa tunda ba zama cikinsa zanyiba, dama ka sayar kayi wani hidimar da kuɗinka danni nanda sati gudama zan koma london”.
Wani shegen murmushi ya sakar mata da kashe mata ido ɗaya, yace, “Yayi Mrs Shira, nifa shiyyasa kike matuƙar birgeni”.
Yanda yay mata ɗin ya sakata nishaɗi ta ƙara ƙanƙamesa tana dariya. Da ga haka suka sake komawa duniyar masoya ƙasan ran kowa da abinda ya damesa, sai dai sunata ƙoƙarin ɓoyema junansu bisa mabanbanta dalilai.


Washe gari tunda safe AK yabar gidan bayan Khalipha da kansa yazo ya kawo musu breakfast, lokacin ma Farah nashan barcin gajiyar murzar juna da sukai jiya, shima sai note ya bar mata suka fice tare da Khalipha.


*_DANYA_*


A Danya shagalin biki ake na gaske, dan dangin mmn sadiq har safiyar yau zuwa sukeyi, hakama abokan arziƙinta na nan danya sunta zuwa mata baici duk da zuwa yanzu ta wuce da saninsu. Kusan goma na safe sai ga dj da kayan kiɗa dasu Haneef, dama sun haɗa ɗan meeting nasu zasuzo Danya su cashe tunda Yayansu ya hanasu a kano, su dukansu suka taho har Adilah da ƴaƴan Uncle Ahmad da zuwa yau dai sun zama ƴan gari kodan halin su Haneef na barkwanci.
Sosai isowarsu da dj ya karama bikin armashi, dan a take suka warware sauti biki ya ɗau harama ƴan danya suka ƙara shaidawa. Dan su Meenal da ƴan ɗan musa filin rawa suka shi su Moos'ab suka dinga zazzaga musu liƙi. Yaran gari dana dj na daka wawa. Al'amarin kamar wasa saiga biki yayi armashi, dan ita Zinneerah harma ta faraji a ranta ko Moos'ab ɗin aka aura matane.
Tayi ƙyau cikin less lemon green da ratsin orange, Meenal ta tsara mata kwalliya ta fito ɗas a amaryarta abin shawa da birgewa. Gyaran da tasha yana nuna kansa a fartarta da ƙamshinta da duk inda ta zauna sai ya cika waje. Ga lalle tasha a daren jiya da yay matuƙar mata ƙyau. Badan tasoba Jamal ya jata har tsakkiyar fili inda su Saifudden suka rufeta da liƙin ƴan ɗari bibbiyu sabbi ƙal. Ai sai bama tasan lokacin data fashe da kuka ba bisa dalilai masu yawa. Hakan da sukai yasa yaya gajeje ma zuwa ta farama Zinneerah liƙin ƴan hamsin-hamsin tana hawayen daɗi, sai ga Sa'a da chewing gum da sweet itama data siya ta fara zazzagesu akan Zinneerah. Aifa sai guri yaɗau ihu da sowa dan sun burge. Gwaggo maryama ma shigowa tai tayi nata liƙin, suma sai ga ƴan ɗan musa suna nuna tasu bajintar kowa dai-dai karfinsa. Wanima naira 100 zaizo ya liƙa mata ya fita.
Wannan al'amari ya ƙuntata zuciyar Inna matuƙa, har takai ta yanke jiki ta faɗi sai da akai kama-kama wajen kaita ɗakinta. Sai Karima da Atine da Tinene da nunkufurci kecin ransu suka zauna da ita a ɗaki suna zage-zage wai da biyu su maman sadiq sukazo suka kafa bikin ai dama a danya. Duk da wasu a ƴan uwan mmn sadiq ɗin sunji sai basu kulasuba. Dan tunkan su taho an roƙesu kosunzo dan ALLAH karsu shiga sabgar Inna Asabe komi zatayi, dan su dai farin cikine ya kaisu suje ayi a tashi lafiya a miƙa amarya ɗakinta. Da wannan yasa suka sharesu.
Su Yaya Gajeje kuwa basusan mike faruwaba suna can anashan dj dasu a waje hankali kwance.


Shagali kam dai an shasa sai dai ace Alhamdulillahi, Zinneerah tayi kukan daɗi, tayi na damuwa, tayi na godiya ga ALLAH, ansha hotuna kuma da mai hoto dasu Mas'ood sukazo dashi, zuwa ƙarfe huɗu kuma sai ga motsocin ɗaukar amarya sunzo.
Kasancewar Zinneerah tasha faɗa wajen iyaye da kakanni tun a daren jiya sai yazam yau sallama kawai aka kaita taima su baba da danginsa. har ɗakin Inna da sai yanzu kowa yasan da faɗuwarta, amma kasancewar ta farfaɗo hakan bai hana su Yaya Gajeje shirin raka ƙanwarsu ɗakintaba. Hardasu Karima mai jego kuwa dan sunce sai sunje sunga uwar da ake nusu fariyya da ita sukam.
Inna bata hanasuba, dan itama daga ƙarshe catai zataje duk da halin da take a ciki na alamar ciwo. Dan ko gani batayi daƙyau saboda jininta da ya hau sama ƙololuwa dan damuwa da ruɗanin tashin hankalin da take a ciki. Baba zai hanata Gwaggo Laritu tace ya barta. Ai gara taje ta gano komai da idanunta zaifi. Amma yace sam bazatajeba sai daga baya saje da amaryarsa idan ALLAH ya sauketa lafiya. Tamaji da kanta. Badan tasoba dole ta haƙura dan da gaske tana a cikin wani hali dannewa kawai takesonyi dan zuwa taga ƙwaƙwaf. Amma tunawa ga ƴaƴanta nan yasa ta haƙura ta shige ɗaki tana kukan da bataso kowa ya gani.


Tunda aka saka Zinneerah ta shirya bayan an ɗanƙara mata nasiha take rusar kuka da shiga tashin hankalin tunanin wanene mijin nata. Dan yanda Moos'ab ya nuna mata baiyi kama da miji a garetaba. Sai dai idan suna ɓoyewane har sai taje can ta gani. Kasancewar an turo motoci babu laifi kowa sai da ya samu wajen zama duk da wasu a matse suka tafi, ga kuma motocin ƴan ɗan musa suma sun sake taimakawa. dan a danya har ƴan gayyar soɗi dason ɗakko rahoto sai da sukabi.
Motar da baba ya kama amarya Zinneerah kuwa ya saka da hannunsa sabuwace dal a ledarta Baffah ya bada a ɗakkota ciki, ita da Gwaggo Laritu da wata Gwaggo Aisha ƴar ɗan musa suka shiga tana tsakkiya, Adilah na gaba kusa da Huzaifa da zai ja motar. Wasu a cikin baƙin ɗan musa zasu wucene gidan mmn sadiq sai zuwa gobe suje suga ɗakin amarya kafin su koma gida. Dan haka motocin ɗaukar amarya sun riga su mmn sadiq tafiya dan su sai da sukai zaman yin sallama da mutane da godiya ga baba sannan suka taho gab da magriba.


Zuwa lokacin motocin ɗaukar amarya tuni sun isa cikin kano har Shira's house, inda Zinneerah keta kwasar kuka har suka iso gidan. Gidan da take zaune a cikinsa matsayin ƴa gata ta dawo a matsayin amarya.
Hajiya iya da kanta ta fito ta tarbi Innon ta bakinta kamar zai yage dan fara'a. Zinneerah ta faɗa jikinta tana sakin wani sabon kukan. Itama rungumeta tayi cike da farin ciki.
Ƴan kawo amaryama sun sami tarba ta mutunci da girmamawa. Inda aka saukesu a sashen Mommy dan sassan gidan duk cike suke da baƙi, hatta sashen Uncle Ahmad da matarsa keta baƙin rai sai da hajiya iya ta tura baƙi idanma mutuwa zatai ta mutu matsalartace cewar hajiya iya.
Zinneerah kuwa direct sashen hajiya iya aka nufa da ita. Baƙi kuwa aka sake karramasu da lafiyayyen abinci mai rai da lafiya. Aikam su kam warshan, dan babu wanda yayma kansa mugunta ci sukai sukai nak banda Tinene da ta faraci tahau amai.
Wannan abu ya bama kowa mamaki har aka shiga kallan kallo, amma gudun tada zaune tsaye Gwaggo Laritu da ke kallon tinene gabanta na faɗuwa ta janyeta gefe tana sanarmusu shawarace taima Tinene mugun kamu. Shiru dai kowa yayi badan baida abin faɗaba. Musamman ma su yaya Gajeje da tsoronsu ya fito ƙarara a fuskokinsu suna bin Tinenen da kallo.
Bikin mata ya cigaba da gudana a cikin gidan, dan sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu za'ai walima and liyafar cin abinci, su AK kuma bayan isha'i zasuyi fatin da su Huzaifa suka shirya wanda sai a yammacin yau yasan dashi. Faɗa yaytayi su Dr Mahmud na lallaɓashi, sai da yaji iyakar su mazane kawai ya sami nutsuwa ya sassauta masifar yana maida numfashi.
Dole badan yasoba yay shirin cikin ɗanyar shadda bayan sallar isha suka tafi hall ɗin da fatin zai gudana. bayan yama Farah dabara irin na maza akan zaije bikin wani abokinsa ne. Sanin baya zuwa irin waɗan nan abubuwan da ita saboda kishi yasa batako damuba...............✍






*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍




*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*

*_TYPING📲_*




*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 50*
_________________________


_*MS TREATS*_


_(PALACE OF PERFUMERY & TRADITIONAL VARIETIES)_


_COME & EXPERIENCE EXCEPTIONAL SCENTS’ AND DELICACIES, YES WE ALSO CARTER TO SMALL & LARGE EVENTS._


_Turaren wuta irinsu_


_Smal halut_
_Sandal coconut _
_Janal banal _
_Arabian oud sandal bakhuor _
_Special kajiji _
_Sandal flake_
_Vip hawi _
_Sudanes sandal rose _
_Humra _
_White humra_
_Black humra _
_kulaccam _
_Dilka soap_
_Whitening soap _


_SPICES_


_Curry powder _
_Corriander powder _
_Tumeric powder _
_Mix spices _
_Ginger powder _
_Black pepper _
_White pepper _


_SNACKS_
_
_Samosa_
_Spring rolls _
_Meatpie _
_Cupcake _
_Birthday cake _
_Doughnut _


_Contact 07061106161 or 08099990056_
_address: bayan northwest university layin gidan ruwan dish_
_KANO, NIGERIA_


_________________________


*Page 50*


..........Soaai AK yayi mamaki matuƙa da ganin abokansa waɗandama shi kobi takansu bayayi yanzun, hakama abokan harkar business ɗinsa dake anan Nigeria. Dole dai ya ware ya shanye mamakinsa ya shiga basu hannu suna gaisawa da tayashi murna, tare da masa ƙorafin ba'a gayyacesu ɗaurin aureba sa fatin da babu amarya babu ƴammatan amarya balle Uwargida. Murmushi kawai yakeyi bai iya cewa komai dan baida abin faɗar.
Daga haka komai ya kasance a nutse cike kuma da birgewa. Dan abune na masu aji sam babu wata hayaniya. Anci ansha an sake taya ango da amarya murna da musu fatan alkairi, zuwa goma taro ya tashi lafiya kowa yana sam barka. Baƙi suka koma masaukinsu masu gidaje anan kano suka kama gabansu.
Sosai AK yaji daɗin fatin nasu kuwa. Dan koba komai ya haɗu da tsoffin abokansa da uzurorin rayuwa ya sashi mantawa dasu. Koda ya ɗan leƙa gidan nasu bayan sun tashi kasa zama yayi saboda hayaniyar ƴan biki, wai a hakanma wasu sunyi barci saboda gajiya, dole yayma su Baffah da Uncle Ahmad da suke nane da juna sallama ya gudo gida.
Lokacin daya shigo gidan Farah tayi barci, dan haka shima kayan jikinsa kawai ya zare yay wanka da neman makwanci saƙe-saƙe fal ransa. Musamman fargabar zuwan su Mammah gobe idan ALLAH ya kaimu da Mahma ta sanar masa. Sam bayason Mammah tazo ta tada hankalinta a cikin wannan taron mutanen ƴan biki, shiyyasa tun ɗazun abin ke damunsa da ƙyar yaketa faman tausar kansa.
Yau sukai niyyar tahowa Mahma ta sake lallaɓasu akan su zauna zaman shirya abubuwa yanda zasu iya tunkarar Baffah. Dan sunyi aniyar tahowa su shiga garin danya da akace musu amarya take kafin su wuce kano. Hakan yasa Mahma kautar da hankalinsu har amarya ta isa ɗakinta lafiya sannan. Tasan dai idanma sunzo a gobe insha ALLAH aikin gama ya gama kuma.


_______________________★


Washe gari aka tashi da shirin gagarumar walima wadda daga ita kuma sai miƙa amarya Zinneerah ɗakin mijinta. Zinneerah data kwana a ɗakin AK ita da Adilah kuwa da zazzaɓi ta tashi, amma tanata daurewa dan har wasu ƴan sauran gyara da suka rage hajiya Falmata tai mata a daren. Tsabar gyaran data sha maranta har wani ciwo yakeyi mata. Haka dai ta cigaba da daurewa har hajiya Iya ta shigo ɗakin domin dubata. Dan Adilah dake fashin salla ma ko tashi a barci batayiba.
Sun gaisa da hajiya iya take tattaɓata ganin duk tayi wani iri, “Kai Inno ai zazzaɓi ne a jikin nan naki, haka kika kwana da shi ma ko?”.
Cikin ƴar shagwaɓar da suka sabama hajiya iyan ita dasu Jamal ta ɗaga mata kai idanunta na cika da ƙwalla. Sannu hajiya iya ta shiga jera mata, kafin ta taimaka mata shiga bayi dan ta samu tayi wanka. Koda tayo wankan ta samu ta shirya cikin atanfa sabuwa ƙal data amshi jikinta ɗas ta fito a amaryarta, Adilah kanta data farka sai yaba ƙyan datai takeyi, murmushi kawai Zinneerah keyi dan sosai take ganin girman Adilah ɗin kasancewarta ba ƙarama ba, sai dai kawai ALLAH ya bata ƙaramin jiki ga kuma yanayin inda ta tashi rayuwar turai, dan ita hausarma ba iyawa taiba tunda ba zuwa Nigeria ɗin Mammah take bari tayiba. Iya kacinta dasu magana da turanci, saiko AK dake iya jin yaren Mammah na larabci sukanyi, shiyyasa basa shiri da hajiya iya sosai saboda takaicin Adilah ɗin bata iya hausaba.
Tea hajiya iya ta kawo mata a sha da magani ta sake kwanciya kafin lokacin walimar.


★★★


A katsina kam ko breakfast ɗin arziƙi basuyi zaman yiba suka kamo hanyar kano, lokacin da suka iso gidan anata kwasar mutane zuwa ƙaton hall ɗin da za'a gudanar da walimar. Yanda anguwar ta rikice da kai kawon motoci masu kwasar mutane yasa dole su Mammah suka fakin tun a waje, Mahma ce kawai ke dauriyar gaisawa da mutane, amma Mammah da Aunty Zakiyya sunata shan ƙamshi.
Koda suka iso cikin gidan sun sami Baffah tare da baƙi, yana ko ganinsu yabar baƙin da uncle Ahmad ya nufosu fuskarsa ɗauke da murmushin daya sake fusata Mammah, aiko tayi kicin-kicin da rai tamkar zata fasa ihu. Sai dai batace komaiba bisa ga gargaɗin Mahma da sukasha.
Duk yanda Aunty Zakiyya taso nuna halin nata ga Baffah kasawa tai, dan wani irin kwarjini yay mata da cikar kamala. Dole tai ƙasa da kanta tana gaisheshi da girmamawa. Shima cike da fara'a ya amsa mata harda tsokanarta.
Yanda Mammah ta ɗauke kanta daga garesa haka shima yayi tamkar bai gantaba, cikin girmamawa yacema Mahma su shiga ciki. Murmushi tai masa, yay gaba suna binsa a baya har sashensa tacan baya da ƙofar falonsa ta ainahin bedroom ɗinsa take. Dan yasan acanne kawai babu wani hayaniyar mutane da hankalinsu zai kai kansu saboda wutar bala'i daya hanga a idanun Mammah.
Kafin su shige ya aika Jamal da sukaci karo ya sanarma hajiya iya zuwansu, daga nan ya wuce a haɗo abinci a kawo musu. Mammah zatai magana cikin masifa Mahma ta dakatar da ita da idanu, dole taja bakinta tai shiru tana haɗiyar zuciya.


Cikin ƙanƙanin lokaci hajiya iya ta ƙaraso tareda su Bahijja dake ɗauke da abinci, suna ajiyewa suka gaishesu suka fice. Mahma da aunty Zakiyya ne kawai suka gaida hajiya iya, Mammah kuwa sai da Mahma ta harareta sannan ta gaisheta da ƙyar. Hajiya iya bata damuba kam, dan ba yaune farauba.
Yanda hajiya iyan ta nuna rashin damuwarta ya ƙara zafar Mammah ta fara magana a ƙufule, “Kabeer miye wannan ke nufi?”. Tai maganar tana ajiye masa invitation card a tsakkiyar centre table. Uncle Ahmad daya shigo falon ne ya ɗauka ya duba ya maida ya ajiye. Kasancewar shima ɗan zafin kan ne a gadarance yace mata “katin gayyatar walimar liyafar cin abincin auren gudan jininmu mana”.
Kallonsa tai rai a ɓace tana juya idanu, “Kai kuma bansa da kaiba mijin tace, kaji da taka matsalar kafin ka tsoma baki a ta wasu”.
“Hakan na nuna miki cewar wadda ta maidani mijin tace ɗin tafiki komai, tunda ke kin kasa maida Yayana mijin tace ɗin saboda ƙarancin ƙyaƙyƙyawan nazari da kishin hauka dake damunki. In banda abinki Hindatu tayaya kike tunanin raba ƴaƴa da mahaifinsu ta ƙarfin tsiya? Ke waya rabaki da naki har suka bar duniya”.
“Wlhy Ahmad ka kiyayeni, kasan na fika zafin kai”.
“Anƙi kiyayar taki, kiyi duk abinda zakiyi”.
“Zako kaga mizanyi ɗin, dan wlhy wannan auren kun ɗaura banza saina rabashi, in banda son zuciya taya yaro yana zamansa lafiya da matarsa zaku ƙaƙaba masa auren yarinya baƙauya mara galihu.........”
A fusace hajiya iya ta katseta da faɗin, “A rashin galihun nata shi ɗan naki ya gani yakeso, tunda har ya iyama yarinya ciki a waje ta haihu ita ƴar son naki bata haifaba. Hindatu ki kiyayeni wlhy, ina ɗaga miki ƙafa saboda ɗanki, amma inaga wannan karon saina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login