Showing 21001 words to 24000 words out of 37846 words
Chapter 8 - Yar gwagwarmaya complete Book by Yar Autar Arkilla.txt
dake kula da ita ya fito ya kira nurse suka koma ciki da sauri. Faisal kam banda kuka ba abinda yake. Jimawa kadan likitan ya fito yana sanar musu ta sami bacci. Ya kuma bukaci ganin Alhajin a ofishinsa. Bayan sun je ne yake sanar masa damuwa ce silar ciwon matarsa. Hakan bai bashi mamaki ko yasa yayi wani tunani ba saboda sanin halin damuwar da dukkaninsu suke ciki na batan 'ya yansu. Addu'ar samun sauki suka yi mata shi da likitan, sannan ya yi masa sallama ya fita.
Daga asibitin ya wuce gida ya yi wanka ya canza kaya, sannan ya dan sami nutsuwa ya kira wayar gidan da 'yan matanshi suke dan raba musu aiki.
Amina ce ta daga wayar, wayar da take kan recording. Ta gaishe shi cikin girmamawa ya amsa. Kana yace "ki gayawa Aysha ta shirya yau da yamma zata tafi Mexico, Umaima kuma da sassafe zata wuce Rasha. Zainab ta tafi Dubai, ke kuma Canada. Sauran su jira zuwan kasuwa. Zan turo wa ko-waccen ku lambar wanda zata hadu da shi. Ku kasance cikin shiri bamu da lokaci sai kirana suke". Ta amsa da "to". Suka ajiye wayoyin. Ta isar da sakonsa ga duk wadanda ya abmbata. Nan da nan suka hau shiri cike da murnar samun dama.
Dukkaninsu sun sani wannan shi ne aikin karuwancinsu na karshe dan tsaida shaidu da manyan hujjoji kamar yadda suka tsara da Auntynsu Fadwa.
To fa π€
*Nasmat* β
ππππππππππ
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
ππππππππππ
π¨π»βπ»π©π»βπ»
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
ββWΙ ΙΚΙ Ι¦ΙΚΙ tΡ³ ΙΙucΙtΙ, MΡ³tiΡ΅ΙtΙ ΙΙ³Ι ΙΙ³tΙΚtΙiΙ³ Ρ³uΚ ΚΙΙΙΙΚΰΈ£β.
_____________________________________
Β©
'Yar mutan
Arkillaβ
____________
```Page 19```
*Barka dai masoya makaranta wannan labarin. Ina yi wa kowa da kowa barka da wannan lokaci. Har yau dai hakuri nake bawa masoya kan tsaiko da ake ta samu ga wannan labarin. Wanda dukansu suna samuwa ne bisa manyan dalilai. Na farko na hadu da matsalar rashin lfy, bayan dawowana kuma sai matsalar waya. Wadannan abubuwan su ne suka yi mini katanga da ku da wannan labarin. Gabadayanku ina sonku kamar yadda kuke so na. Babu shakka masoya abin alfari ne ga ko-wane tauraro. Ina alfari da ku duka. Nasmat ta dawo, labarinku ma ya dawo ku mu je zuwa. π*
Washe gari dukkaninsu suna kasashen da aka bukaci su je. Aysha ce ta fara kammalawa a kwana dayan. Bayan ta gama maida rigarta ta kalli tsumakakken baturen da ya gama amfani da ita yake saka kaya tace cikin turancinta da bai gama kama bakinta ba "wai tafiya zaka yi, kudin aikina fa?". Busashshen baturen ya kalleta da mamaki yace cikin ingantaccen turanci "wannan wace irin magana kike kamar wata bakuwa? Kudinki kam tun kafin ki zo suka sauka a asusun mai gidanki Alaji Abib". Yadda suke kiransa kenan. Aysha ta wayance da cewa "Oh! Yi hakuri, na manta ne saboda uzuri na bukatar kudin da nake ciki". Baturen mai suna Michale ya daga kafada irin ko a jikinsa din nan ya fice yana mata sallama. Ta sauke numfashi tana mai kashe camera da ta kunna tana daukar maganganun da suke. Ta mike cike da murna tana hada kayanta dan komawa gida Najeriya.
*Ranar assabar a maitama*
Bayan ta gama motsa jiki ta fito da nufi komawa dakinta, sai ta tsinci kanta da son ganinshi da halin da yake ciki. Duk da Ab'ha ya sanar mata cewa guy din ya warke sumul. Kawai ta ji ne tana son ganinsa ne. A hankali ta nufi kofar dakin da yake cikin takunta na cikakkiyar mace mai ji da kanta. Ta mirda kofar bayan ta murza key, ta tura ta shiga. Baffa da idonsa suke kan kofar tun da ya ji ana taba key ya zubawa mai shigowar ido. Shi a zatonsa Ab'ha ne domin rabonsa da ganin Fadwa tun ranar da wannan tsautsayin ya gifta ta masa dukan kawo wuka. Amma Ab'ha kam kullum suna tare, shi yake kula da abincinsa. Sun saba da shi sosai fiye da kima.
Ita da shi duka ba wanda ya yi magana, sai dai dukkaninsu sun zurfafa ga kallon junansu cikin wani irin yanayi. Ita ce ta fara yin jarumtar kauda kanta ga barin kallonsa tana mai jin haushin zuciyarta kan yadda take yabawa da kebance kyan zubi da halittar Baffa a kan duk wani da namiji da ta taba gani a rayuwarta. Bata san shi ba sai a kan wannan abin na ubansa, amma zuciyarta tana nuna shi daban ne da ko-wane namiji. Take haushin kanta ya fara kamata, sai ta ga kamar yana ganin halin da take ciki. Da sauri ta juya da nufin barin dakin ba tare da tace komai ba. Har ta kama handle na kofa zata murda ta ji sautin muryarsa cikin sanyi da tausasawa yana cewa "dakata mana Fadwa, ba dan ni da nasabata ba ki tsaya ki saurare ni domin Allah". Cak! Ta ja ta tsaya, tare da dakatar da bude kofar da ta yi niyya. Babu wani kwakkwaran dalili kawai sai ta ji jikinta ya yi sanyi. Ko dan yanayin yadda ya fitar da maganar ne?.. Ci gaba da maganar da ya yi ne ya katse mata tunani. "Ki yi hakuri Fadwa. Hakika na sani idan kika kalle mu ta fuskar nasaba da tushe sam ba mu can-canci ki yi mana afwa ko rangwame ba. Amma ina so ki kawar da duk wadannan. Ki kallemu a matsayin al'uma, 'yaya marayu wadanda basu da uba a duniyar nan. Fadwa ki dubi Allah da darajar Annabinsa ki dawo mana da Anisa. Da can a baya ina miki kallon azzaluma mara imani wadda ake biya kudi tana cutar da mahaifina. Amma a yanzu da Allah yasa aka yi walkiya ta haska idona na ga komai Fadwa. Abokin aikinki ya gaya min komai ya kuma nuna min tsayayyin hujjojin da suka saka na yarda da ku, na ji bayanai dabam-daban a bakin 'yan matan nan da suke nan. Fadwa na gano mahaifina da halayyarsa su suka saka kike yin duk wani abu da kike. Har ga Allah ban ga laifinki ba, mutumin da aka zalumta kamar ke babu abinda ba zai iya yi ba. A yanzu na san waye mahaifina, na san cikakkiyar gurbatacciyar sana'arsa. Na tsane shi, na tsani halayyarsa. Bana fata ko burin a koma kiransa ubana, bana son ko-wace alaka ta koma hadani da shi na tsane shi." Ya matse idonsa da karfi wasu zafafan hawaye suka silalo zuciyarsa cike da nadama da dana sanin zamowa daya daga cikin 'yayan Alhaji Habib.
"Ban san ya kike ji ba a matsayin ki na wadda aka batawa rayuwa, aka raba ta da mutuncinta ta karfi. Amma na san yadda ni nake ji a matsayina nan yaya, kuma dan uwa ga wadda irin hakan ya faru da ita. Uwa ce kawai ban san yadda ita kuma zata ji ba." Ya koma matse idonsa domin rage musu nauyin hawayen dake ta turereniya da juna a cikin su.
"Fadwa ki dubi Allah ki dubi halinda mu da Momynmu muke ciki ki dawo mana da Anisa. Wallahi na rantse miki a yanzu bana ganin laifinki. Mahaifina shi ne ya assasa komai kuma shi ne mai laifin. Na roke ki da Allah ki dawo da wannan 'yar ga mahaifiyarta." Ya karashe maganar cikin rishin kuka. Take ta ji wani iri ba dadi. Bata juyo ba, kuma bata ce komai ba. Ta bude komai da sauri ta fita. Baffa kuwa kansa ya daga sama ya ci gaba da kuka cikin kuna da zafin zuciya. Kukan da yake jin yinsa zai iya rage masa wannan zafi da nauyin da yake ji bisa kirjinsa.
Da zuwa ta fada kan faffadan gafonta, mai laushi da kyan shimfida. Ta lumshe manyan idanuwanta tana tariyo abinda ya faru, sam bata yi tsammanin yaron nan zai fahimta kuma ya sauko cikin sanyi haka ba. Mamakinta shi ne yaushe ma Ab'ha ya iya wannan jawabin da kokari na ganar da da laifin ubansa? Tunawa da maganganunsa yasa wasu siraran hawaye zariya kan kyakkawar fuskarta. Sosai kalamansa suka fama mata raunin zuciyarta, wanda ya fara bushewa. Tunawa ta yi da Ummynta uwar riko ba ma wadda ta yi dawainiyar kawota duniya ba. Ta amsa sunan uwa domin har ta koma ga Allah da tabo na ciwon abinda aka yiwa 'yarta duk da cewa ta dawo gabanta.
Sai tausayin mahaifiyar su Baffa ya kamata, hakika zata fi Ummy bakin ciki, domin kuwa ita Ummy bata ma gani da idonta ba. Ita kuwa ta gani, yadda aka keta haddin 'yarta gudan jininta sannan kuma aka badda ta ta inda basu san inda take a duniya ba. Kunkanta ya kara tsananta, tasayinsu yasa ta ga bata kyauta ba. Ta san duka abinda take tana yi ne domin ramuwa ga Shugaba, amma wannan hukuncin ya yi tsauri ga ahli. Domin kuwa shi uba ne kawai, ba zai taba jin kwatankwacin yadda uwa zata ji ba.
*Nasmat* β
ππππππππππ
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
ππππππππππ
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*β
_*WΙ ΙΚΙ Ι¦ΙΚΙ tΡ³ ΙΙucΙtΙ, MΡ³tiΡ΅ΙtΙ ΙΙ³Ι ΙΙ³tΙΚtΙiΙ³ Ρ³uΚ ΚΙΙΙΙΚΰΈ£*_
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?
Β©
'Yar mutan
Arkillaβ
____________
```Page 20```
Ranar kam kwanan bakin ciki da tausayin mahaifiyarsu Baffa ta yi. A ranta tana ganin rashin kyautarwarta, domin a ganinta hukunci na mai laifi ne. Su kuma basu san komai ba. Washe gari tun da asuba ta bar gidan bayan ta yiwa Ab'ha sallama da kara jaddada masa ya kula da gida. Shi kansa bai san inda ta nufa ba. Sai dai bayan fitarta ta kira waya ta umarce shi da ya kwance Baffa ya bude shi, shima ya sake cikin gidan kamar ragowar 'yan matan nan. Duk da ya ji mamakinta na yin hakan amma abun ba karamin dadi ya yi masa ba, domin kuwa yana jin dadin zama da Baffan. Guy din yana da saukin kai da saurin fahimta.
*Washe gari da dare*
Suna cikin yin kalacin dare suka ji an budo kofa an shigo. Fadwa ce ta shigo cikin wata shiga ta atamfa England dinkin zamani, na riga da sket. Kanta yane da wani karamin gyale sky blue kalar kayan jikinta. Hannunta rike da na Anisa wadda ta sha jinin jikinta tana jiran ganin inda aka kawo ta da kuma abinda zai koma biyowa baya. Ab'ha da Baffa suna kan danning suna cin abinci. Yayin da su kuma 'yan matan suke baje a kan Capet din falon suna gabatar da nasu kalacin. Ganin Fadwa da wadda ke tare da ita yasa ko-wannensu dakatawa da abinda yake yi suka zuba musu ido cike da mamaki da al'ajabin wannan ba zata.
Anisa kuwa ganin babu idon sani a gurin ya saka idonta suka fara cikowa da kwalla. Daya bayan daya take kallonsu, ai kuwa karaf idonta suka suka kan dan'uwanta gudan jininta Baffa. Wani uban tsalle ta daka ta kwace hannunta daga cikin na Fadwa ta nufe shi da gudu tana mai kiran sunansa da karfi. "Yaya Baffa!". Ta rungume shi tare da sakin wani irin kuka mai taba zuciya da sanya ta nutsuwa. Baffa da ya gama sandarewa idonsa kyar a kan Fadwa, ya kasa dauke su a kanta ya kuma rasa kalmar da zai furta mata a matsayin godiya ko nuna farin ciki bisa wannan gagarumin taimakon da ta yi masa.
Hannayensa ya daga dakyar ya rufe Anisa dake kankame da kirjinsa, ya damke ta tsam, yana ji kamar mafarki yake yau ga kanwarsa a gabansa. "Anisa..." Ya kira sunan cikin wata raunanniyar murya da ta fito can karkashin makogwaronsa, yana shafa kanta. Kukanta ya tsananta ta kankame shi tana son magana bakinta na rawa, a hakan ta daure ta fara maganar. "Yaya nan kuma ina ne? Me kake yi a nan? Yaya dan Allah ka dauke ni mu je gida, wannan da kake gani azzaluma ce yaya itace ta..." Hannun da ya dora a kan lebenta shi ya dakatar da kalaman dake fita bakinta. Ta dago kai ta kalle shi, sai ta ga yana girgiza mata kai idonsa cike da kwalla.
Yasa hannu ya janye ta daga gabansa ya fara takawa daga inda yake zuwa inda Fadwa take tsaye tana kallonsu. Har a zuwa lokacin babu wata kalma da ya ji ta zo masa wadda ta can-canta ya yi amfani da ita wajen godewa Fadwa. Sai da ya zo daf da ita sannan ya tsaya ya zamana ko-wannensu na iya jin numfashin dan'uwansa. Rashin sanin abin yi yasa ya sauke girmansa da ji da kansa ya tankwashe kafarsa ya gurfana a gaban Fadwa cikin matukar girmamawa da darajawa ya kama kafufuwanta yana son furta mata kalmar godiya amma ya gagara. Wani irin shokin ta ji ya shige ta tun daga kan yatsun kafar tata har cikin gashin kanta. Da sauri ta ja da baya tana mai girgiza masa kai alamar ya bari. Bata yi magana ba ta raba shi ta wuce da sauri ta shige dakinta kana ta rufo kofar.
Anisa kuwa tsaye kawai ta yi tana kallon ikon Allah. 'Yan matan nan sun zagaye ta suna mata barka da dawowa gida amma ko jin su bata yi. Idonta na kan yayanta da abinda ta ga yana kokarin yi ga wadda ta ruguza mata rayuwa. Kuka ta fashe da shi ta karasa gareshi "yaya kanka daya kuwa? Ka kuwa san wace ce wannan? Fadwa ce fa, wannan 'yar gwa-gwarmayar da ta d'ai-d'aita rayuwata ta maida ni karuwa, kuma abin ki fasik..." Baffa ne ya yi saurin toshe bakinta yana girgiza kai. Ransa a matukar bace ya fara magana bayan ya kama hannayenta.
"Aa kanwata, karki ga laifin fadwa bisa abinda ta aikata gareki. Domin kuwa babban mai laifin shi ne Dadynmu. Dady da kike gani shi ne cikakken azzalumi, wanda ya kai makura ga lalatawa da tarwatsa rayuwar 'yayan mutane..." Ya kwashe komai da ya ji game da mahaifinsu da abinda ya yiwa Fadwa ya gaya mata, ya kuma nuna mata hujjojin da shima aka nuna masa, ga uwa uba shaidar kan-kat! Wato wadannan 'yan matan da suke masa kasuwancin karuwanci.
Kuka sosai Anisa ta yi, wanda har yasa ta tsani ci gaba rayuwa a matsayin 'yar Alhaji Habib Shugaba. Tsananin son 'yan uwanta da Momynta ne kadai yasa take son ta rayu. Ba dan tana da su ba da yau ta zama daya daga cikin jerin wadanda bakin ciki yasa suka kashe kawunansu. Ta yi kuka, ta yi gumji, har ta dawo babu murya kuma babu hawayen.
*Asibiti*
Karfe bakwai da rabi na daren, yana zaune a kan kujerar robar dake fuskantar gadon majinyatan. Hannunsa rike da hannunta wanda aka saka mata roba ta karin ruwan jiki. Faisal kenan kanin Baffa kuma yayan Anisa d'a ga Hajiya Laurat matar Alhaji Habib Shugaba. Idonsa a kan uwar tashi dake kwance tamkar babu rai a jikinta. Banda kuka ba abinda yake yi. Addu'a kam bai sai adadin wadanda ya yi ba. Zaune kawai yake amma shi kansa hoto ne kawai ruhinsa ya balle izuwa duniyar tunanin wannan iftila'in da ya afka musu. Ga Momy kwance a asibiti, Baffa ya bata, ita Anisa ba a ma san inda take ba. Wannan wace irin masifa ce. Kofar dakin aka budo aka shigo, ya dago kansa dakyar ya zubawa mai shigowar ido. Mai gadin gidansu ne Izike. Har zai dauke idon nasa ya yi gaggawar komawa da su ga kofar, saboda ganin wadanda ke biye a bayan Izike. "Anisa! Yaya Baffa!!". Ya ambaci sunayen cikin tsananin mamaki da tan-tamar sune ko dai idonsa ne suka fara yi masa gizo?
Anisa ce ta tabbatar masa da su din ne. Ta hanyar rugawa da gudu ta kankame shi tana kiran sunansa "yaya Faisal". Firgigit Hajiya Laurat ta farka daga nannauyan baccin da take bayan ta dawo daga suma. Kamar a mafarki ta ji ana kiran sunayen 'yayan nata. Ai kuwa tana yin arba da su ta shiga kiciniyar cire robar dake hannunta ta mike zaune.
Gaba daya suka yi kanta suna kokarin kwantar da ita. Ta ja Anisa zuwa jikinta ta rungume ta. Wani kuka mai karfi ya kwace mata a dalilin tunawa da yadda ta ga ana wulakanta 'yar tata a fai-fan video ana keta haddinta. Ta rumtse ido da karfi tana kaico da alawadan kasancewarta matar shi.
Bata san lokacin da bakinta ya furta kalmomin ba. "Allah ya isa tsakanina da kai Alhaji, har abada ba zan yafe maka ba. Ka cuce ni ka cuci zuri'armu".
*Nasmat* β
ππππππππππ
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
ππππππππππ
π¨π»βπ»π©π»βπ»
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
ββWΙ ΙΚΙ Ι¦ΙΚΙ tΡ³ ΙΙucΙtΙ, MΡ³tiΡ΅ΙtΙ ΙΙ³Ι ΙΙ³tΙΚtΙiΙ³ Ρ³uΚ ΚΙΙΙΙΚΰΈ£β.
_____________________________________
Β©
'Yar mutan
Arkillaβ
____________
```Page 21```
Gaba daya yaran suka zuba mata ido cike da mamakin jin abinda take fada musamman Faisal da bai san komai game da mahaifin nashi ba. Su kuwa Baffa da Anisa mamaki suke ta yaya Momy ta san laifin na mahaifinsu ne? Waye ya sanar da ita?... Suna cikin wannan tunanin suka jiyo Faisal yana jerewo Momyn tambayoyi cikin wata rikitacciyar murya mai dauke da dimuwa. "Wane Alhajin kike nufi Momy? Ba dai Dady ba ko? Me Dady ya yi miki wanda har kike cewa ba zaki yafe mishi ba Momy? Shin wace cuta kike ganin ya yi mana a matsayinmu na zuri'rku?
Momy kam sai