Showing 18001 words to 21000 words out of 37846 words

Chapter 7 - Yar gwagwarmaya complete Book by Yar Autar Arkilla.txt

25 Oct 2025

376

tashi amma ganin Faisal a gurin yasa ta daure ta hadiye abun. Hakan kuwa bai hanawa gumi ci gaba da tsatstsafo mata ba. Ta mike ta nufi dakinta.


Da shigarta dakin ta fara binciken wayar tashi tun daga bangaren test message har zuwa email. Amma bata samu komai mai kama da wannan ba. Hawaye kuwa sai zariya suke a fuskarta jiki na bari. Kar dai zargin yarinyar nan ya tabbata. Kar ace da gaske mijinta safarar mata yake. To in ba haka ba wace yarinya ce ya karbi kudinta da har ake cewa in babu ita ya dawo da kudin?. Bata da amsar tambayoyinta, amma dukkanin alamu sun nuna mijinta na safarar mata ne. "Innalillahi wa inna ilaihi raji-un". Kalmomin da bakinta ke ta nanatawa kenan, a kokarinta na ganin ta samun nutsuwar zuciya. Ta kasa zama ta kasa kwanciya bata toilet bata dakin nata cikinta sai juyi yake. Tana cikin haka Alhajin ya shigo ransa a matukar bace, saboda sakonni biyu na tashin hankali da ya samu. Na farko hoton gawar dansa da ya gani Fadwa ta yada, dan shi a tunaninsa babu rai a jikinsa. Ga kuma labarin kiran da kotu take masa ya wanke kansa a ranar litinin, da ya riske shi. Hajiya Laurat ta yi iya kokarinta wajen ganin ta boye tashin hankalinta. Ta masa sannu da zuwa bai amsa ba. Tace cikin sanyin jiki "an yi ta kiranka a waya baka nan, musamman wani Mr. Suwat da ya maka kira sun fi ashirin. Shi kam saboda yawan kira ma sai da nasa aka daga aka ce masa baka nan". Da sauri ya kalleta "wa ya daga wayar?". Tace "Faisal ne. Yace mutumin yace in babu kayan ka mayar masa da kudinsa man". Wani gwauron numfashi ya sauke cike da godiyar Allah a ransa. Sannan yace a diririce "su turawan nan sam basu da hakuri, da zarar abu ya hada ku sai su yi ta matsa maka". Yana kokarin fita ta jefa masa tambaya "kasuwanci ka fara Alhaji?". Tambayar ta zo masa a ban-barakwai ya kalleta da mamaki "au da baki san ina kasuwanci ba?". tace "wallahi ban sani ba, Allah ya sanya alkhairi" yace "amin" yana danna kiran wayar tare da ficewa.


Dakinsa ya nufa kai tsaye. Da sauri ta mike ta bi bayansa da sanda. Saboda zuciyarta ta kasa hakuri lallai tana son sanin gaskiyar mijinta.


Ya murda kofar ya shiga yana magana kasa-kasa a wayar. Dai-dai kofar dakin ta tsaya. Dukda bata jin me yake cewa sosai amma ta tabbatar da Suwat din ne yake magana, dan taji yana bashi hakuri. Ko matsowa ya yi oho, ta dai ji muryarsa ta fito sosai yana cewa "kai matsalarka kenan wlh. Na gaya maka yarinyar nan an sace ta tare damatan nan da aka sace min. Amma ka nace sai ita. Ka bari in kawo maka wata ka gwada ta, na tabbata zata fi maka waccan ma. Domin wannan mai zafi ce bata dade da farawa ba". Bata ji me aka ce masa a cikin wayar ba, ta dai ji yace "to ko kai fa, gobe zan turo maka ita ka tare ta airport. Saboda ni banida lokaci yanzu, ina cikin wata damuwar". Duk a cikin harshen turanci yake maganar.


Jin kafufuwanta na rawa yasa ta yi gaggawar barin wajen tun basu kasa daukarta ba. Da taimakon Allah ta isa dakinta saboda duhu-duhu da idonta ke gani. Addu'a kam duk wadda ta zo bakinta yi take. Wannan wace irin masifa ce? Ashe dama haka Alhaji yake? Ashe yarinyar nan mai gwa-gwarmaya a kan gaskiyarta take? Innalillahi wa inna ilaihi raji-un. Sai ta fashe da kuka. Nan da nan zazzafan zazzabi ya rufe ta, jikinta sai kyarma yake yana ciccira.


*Maitama*
Bayan dogon lokacin da matashin likitan ya shafe a kansa. Baffa ya dawo hayyacinsa, har ma ya shiga baccin dole.


Da dare misalin karfe takwas ta shirya zama da matan nan da suka sato, wadan-da tun da suka zo gidan basu taba ganinta ba. Suna zaune cirko-cirko aka budo kofar aka shigo. Gaba daya suka dago tare dan jin wani lafiyayyen kamshi da ya cika dakin, sabanin kullum idan mai shigowar ya zo. Ganin mace ya basu mamaki matuka. Hakan yasa suka kara maida hankali gareta. Kujerar robar da ta shigo da ita ta ajiye ta zauna tana fuskantar su.


"Sannunku 'yan uwa, kuyi hakuri fa, na tara ku nan amma ban samu muka hadu ba. Na san ba wadda ta san ni a cikinku. Sai dai na san zaku san sunana. Fadwa nake 'yar gwa-gwarmaya. Na kawo ku nan ne domin ganar da ku asalin batan da kuke kai. Ku mata ne, amma har yau baku san daraja da martabar da 'ya mace take da ita ba. Mafi yawan mata sun kare kansu da mutuncinsu. Amma saboda ire-irenku matan titi, ana yi musu kallon wulakanci. Irinku mata masu zaman kansu ku kuke karya darajar 'ya mace a idon duniya. Shin ku bakwa kishin jinsinku ne?". Ta takaita tana kallon fuskokinsu da suka yi la'asar. Ganin ba wadda ta yi magana yasa ta ci gaba.


Nan da kuke gani na, na tsinci kaina a kuncin rayuwar da ya nunka wanda ko-waccenku ta taba shiga. Na rasa mutuncina, alfaharina. A lokacin da yake daf da amfana ta. Ni marainiya ce, wadda ta taso da burin yin karatu mai zurfi don inganta rayuwarta. Hakan yasa na tilastawa kaina karatu, ba dare ba rana. Kwazona yasa makaranta da iyayen rikona suke alfahari da ni. Ni kuwa ina yin wannan fafutukar ne dan samawa kaina kima a idon duniya, na taso da burin gwadawa 'yan uwana marayu cewa babu maraya sai rago. Amma kafin cimma wannan burin Uban-gidanku ya ruguza rayuwata. Ya yiwa burukana kisan gilla. Kutsen da ya yi a cikin rayuwata da nufin taimako shi ya maida ni yadda kuka ganin nan. Shugaba Habib ba karamin makiyi bane ga mata. Ku sani gatan da yake yi muku ba so bane, ba kuma taimako bane, kasuwancinsa kawai yake ingantawa da ku. Yayin da ku kuma a kullum kuke dada nisanta kanku daga rahmar Allah. Kuke fama da bakar addu'ar matan kirki bisa bata musu suna da kuke. A kan karamin laifin da bai kai komai ba ku baro gidajen iyayenku. Ku bar duka danginku dan kuna jin da akwai abin kudi a jikinku. Kun manta wannan abin na dan lokaci ne? Kun manta kuruciya ke karuwanci?". Ta koma sararawa tana kallonsu.

Ba wadda ta yi magana jikinsu kuma ya yi sanyi sosai. Ta jijjiga kai tace "ni mai son ku ce, mai matukakar kaunar ku. A rayuwar da ta rage min bani da burin da ya wuce inga na samawa mata 'yanci. Burina a wayi gari babu karuwa a kasar hausa. Ya zamana duka matan duniya sun san matsayi da darajarsu. Ko-wane namiji ya wahala ya biya sadakinki kafin ya mallake ki. Wannan shi ne cikar kimar mace. Ba wai ta zama bola abin zuba sharar ko-wane fasiki ba Yanzu ku kalli nan". Ta danna musu play ga TV dake dakin wanda ta riga ta gama saita komai. Hoton video ya bayyana yadda aka keta haddin Anisa 'yar Shugaba. Duka sun gane ta, suka shiga kallon-kallo. Fadwa ta kashe TV ta koma fuskantarsu.


"Da gan-gan nasa aka yi mata haka. Domin shi ma ya ji yadda iyaye suke ji, a lokacin da yake dora musu 'yaya a kan turbar karuwanci. Saboda wannan da kuka gani kwanakinsa uku a asibiti bai san kansa ba. Kun san saboda meye? Saboda ita tashi ce, ya san darajarta, yana son mutuncinta. Ku kuma ya dauke ku dabbobi wadanda basu da iyayen da zasu cutu kan rayuwar da suke. Da yawa a cikinku nan bakin cikinku zai kashe iyayenku..." Tun bata karasa ba wata a cikinsu ta fashe da kuka.


Sannan ta taso daga inda take zaune ta nufo inda Fadwa take.















*Nasmat* ✍
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)

πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€




πŸ‘¨πŸ»β€πŸ’»πŸ‘©πŸ»β€πŸ’»
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
​​WΙ› Ι‘Κ€Ι› Ι¦Ι›Κ€Ι› tΡ³ Ι›Ι—ucΙ‘tΙ›, MΡ³tiΡ΅Ι‘tΙ› Ι‘Ι³Ι— Ι›Ι³tΙ›Κ€tΙ‘iΙ³ Ρ³uΚ€ ʀɛɑɗɛʀร​.
_____________________________________

Β©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________





*Godiya mai tarin albarka gareki MAMAN ISLAM na gode da yabo, da tarin adduo'inki gare ni. Fatana shi ne Allah ya bar zumunci da kaunar juna* ```Ki sani ina sane dake a cikin jerin masoyana, ana matukar tare``` 🀝







```Page 17```







Da zuwa ta zube a gabanta, tare da kama kafafuwanta ta soma magana cikin kukan... "Hakika Anti ke mace ce da kika san darajar mata. Da ace duka mata zamu yi koyi dake, da duniya ta tsarkaka, da masifun da muke ciki sun takaita, da bala'in da ake saukar mana ya ragu. Domin a yau a halin da muke ciki babu abinda aka mayarwa hankali kamar zinace-zinace. Wallahi Anti safarar nan ta mata da ake kar ki so ki ga yadda ake yi da su. Da yawa daga cikin mu ma ba ta inda Allah ya halatta ake amfani da mu ba. Kazantar ta girmama, babban tashin hankalin ma shi ne, ki ji, ko ki ga masu daukar nauyin matan suna tura su yin karuwancin. Da yawa a cikinsu manyan mutane ne, masu kima da daraja a idon al'uma. Wadanda ko sunansu aka kira a cikin masu laifin ba zaki yarda ba. A yau su ne suke bautar da 'yayan talakawa masu karamin karfi. Wadanda 'yayansu ke barin gidajensu a sanadin yin cikin shege, ko auren da basa so (auren dole). Da kuma masu samun wani sabanin daban tsakaninsu da iyaye. Wanda wannan kuskuren namu ne mu da iyayenmu. Wasu iyayen su suke korarsu suce sai sun bar gidan, wasu kuwa ba ma da sanin iyayenba suke lallabawa su baro gidajen saboda gudun auren wanda ba shi suke so ba.

Anti da haka rayuwar 'yaya mata take fara lalacewa, a farkon fitowarmu wahala muke sha sosai, domin ko abinda zamu ci wahala yake mana. A haka ne muke samun masu neman mu fasikanci, tun muna jin tsoron yi har mu fara. Sannu a hankli mu samu muhalli, kudi da ababen more rayuwa. A cikin haka ne muke haduwa da irin su shugaba. Wadanda ke kwadaita mana duniya da kyale-kyalinta. Sai muga ai da wanda muke a nan da wanda zamu yi a can duk karuwanci sunansa. Wannan ne yasa bama shayi ko shakkar amsa kiransu. Ya zamana har ma dadi muke ji idan aka zabe mu, domin kudaden da muke samu a can sai mu shekara a nan bamu same su ba.


Wannan ne yake sawa muke biyewa masu yin safara, da saninmu muke bada kanmu gare su. Amma a yau Allah ya kawo mana ke, babu shakka ke *fitilar 'yan-cin mata* ce. Kin haska ni, na kuma ga tarin kazanta da koma bayan da nake ciki. Anti Fadwa na bada kaina gareki, daga yau an daina amfani da ni wajen yada zina a doron kasa. Na yi niyyar tubarwa mai duka. Tare da neman gafararsa bisa laifukana na baya". Ta karashe maganar tana tsananta kukanta, tare da kankame kafafuwan Fadwa da take rungume da su. Kafin Fadwa ta ce wani abu, ta kusa da ita ta fara magana... "Babu shaka a maganar Zainab, iyayenmu ma suna da rawar da zasu taka, domin rage yaduwar karuwanci a kasarmu. Wannan rawar ko ita ce: su guji korar 'yayansu mata daga gidajensu don kaddara ta afka musu, ko don sun ki bin zabinsu ga aure. Idan aka samu haka hakika za'a rage masifu. Sannan kuma mu mata mu kiyaye, kurciya ta daina fizgarmu muna yin abinda muke so. Wlh mata muna cikin hatsari. Nima daga yau na tuba, ina bayanki. Ki ci gaba da haska muna hanya, yake wannan *fitilar*".


Ta miko hannayenta ga Fadwa. Fadwa ta amsa ta rike ta gam. Haka dai da guda-guda suka yi ta bada kansu gareta. Duka su goma sha bakwai din-nan babu wadda ta juya bawa. Allah ya yi musu rabo sun yarda har cikin ransu cewa karuwanci koma baya ne, kuma masifa ne ga rayukan mutane, har wadanda basu ji ba, basu gani ba. Domin ita masifa idan zata sauka ba kan iya masu laifin take tsayawa ba. (Shiyasa a kullum idan kaga laifi ba a so ka kauda kai dan kai baka aikatawa, an fi so ka tsaya ka yi iya kokarinka wajen ganin ka dakatar da shi. To ko da abin yafi karfinka ka riga ka samu ladar. To balle kuma ka yi nasarar dakushe shi. Allah yasa mu dace amin.)


Farin ciki mara misaltuwa ya kama Fadwa, har ta rasa bakin magana, sai wasu siraran hawaye dake bin kuncinta. Ta kalle su, kallo na jin dadi tace "alhamdulillahi dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, madaukaki. A yau ina cikin farin cikin mara misali, dalilin wannan goyon bayan naku. Domin da gudumawarku ne zamu samu dukkanin hujjojin da mahukunta suke bukata domin gurfanar da Shugaba a gaban kuliya. Ta ware hannayenta aiko duk suka yanyame ta, ko-wannensu na cike da farin ciki.


A wurin ta ware guda takwas daga cikinsu, wadanda tauraruwarsu ke haskawa, kuma su ne Shugaba yafi ji da su a kasuwar tashi ta sake su. Saboda ta san muddin ta sake su duka zai gano shirinta a kansa. Bayan ta gama shirya musu yadda zasu dauko mata sirrukansa irin na harkarsu, ta bawa ko-wacce daga cikinsu kayan aiki, sannan ta dora su a hanya.



*3:56pm*
Wayar Shugaba Habib ta fara ruri. Kishingide kawai yake yana saka da warwara. Tunanin 'yarsa Anisa da halin da take ciki ya addabe shi. Sai juyi yake yana neman abin yi. Hakan yasa bai yi wani jinkiri wurin daga wayar ba. Lambar Umaima ya gani. Daya daga cikin matan nan da Fadwa ta sace masa. Da sauri ya daga wayar yana kiran sunanta. Ta amsa da kyar ta fara magana cikin yanayin galabaita. "Shugaba ka taimake mu, gamu nan mun gudo daga hannun azzalumar nan, amma bamu san inda muke ba. Muna cikin wani hali dan Allah a kawo mana dauki".













*Nasmat* ✍
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)

πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€




πŸ‘¨πŸ»β€πŸ’»πŸ‘©πŸ»β€πŸ’»
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
​​WΙ› Ι‘Κ€Ι› Ι¦Ι›Κ€Ι› tΡ³ Ι›Ι—ucΙ‘tΙ›, MΡ³tiΡ΅Ι‘tΙ› Ι‘Ι³Ι— Ι›Ι³tΙ›Κ€tΙ‘iΙ³ Ρ³uΚ€ ʀɛɑɗɛʀร​.
_____________________________________

Β©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________



_Alhamdulillah ala kulli halin_

*Assalamu alaikum masoyana, masoya wannan labarin na 'YAR GWA-GWARMAYA. Babu shakka na san kun nuna so da kauna kuma kun jira. Ku sani ba dan ciwo ba da babu abinda zai tsayar da ni. Da wannan shafin nake muku albishir cewa na dawo bakin fama. Da iznin Allah zaku ci gaba da samun labarin kullum, kamar yadda aka saba. Na riga na gamsu cewa abinda kuke nuna min shi ne asalin abinda ake kira kauna. Ku sani, ku kara sani, nima nan ina kaunar ku duka. Allah ya bar zumunci ya yi karko amin.*

_Nasmat ta gode!_







```Page 18```







Shiru ya yi, yana nazarin maganarta, kafin daga bisani tunani ya zo masa da mafita. "Umaima." Ya kira sunanta a dan gajarce. "Kin sani sarai cewa ba zan iya zuwa ko turo wani daga bangarena ya taimake ku ba saboda gudun zargi. Amma ki jira yanzu zan turo muku lambar jami'an tsaro, ku neme su, su zasu zo duk inda kuke su dauko ku a saukake". Yana gama maganar ya kashe wayar, sannan ya tura mata test mai dauke da number Asp Sauwam.

Ba bata lokaci ta kira lambar. Shima dai a galabaice ta yi mishi bayanin halin da suke ciki. Nan da nan kuwa ya tashi ma'aikatansu ya tura su inda ya gano a can suke ta hanyar yin (tracking) din number da ta kira shi da ita.

Shugaba ya kasa zaune ya kasa tsaye. Sai kai komo yake yana jiran jin yadda zata kaya. A haka dansa Faisal ya same shi. "Kai lafiya ka fado min daki ba ko sallama?". Ya tambaya yana kallon yanayinsa. Shi kuwa cikin rudu da tashin hankalin da yake ciki yace "Dady ka taimake mu. Momy ce ba lafiya, gata can kamar zata mutu". Ya waro ido da alamar al'ajabi. Bai koma cewa komai ba ya nufi dakinta da sauri-sauri, gudu-gudu. Faisal din ya rufa masa baya yana sharar kwalla.

Halin da ya same ta ciki ya yi matukar razana shi, bata iya magana, ga wani jijjiga da jikinta ke yi. Sam bata san waye a kanta ba. A take ya ajiye mamakinsa gefe Faisal ya taimaka masa suka kinkime ta zuwa mota. Driver ya ja su suka nufi asibiti.


*Police station*
Linda da Zainab, da sauran 'yan matan nan ne durkushe a gaban Dpo bayan da jami'an 'yan sandan suka ceto su a cikin wani babban jeji. Bayan ya gama rubutu a file din dake gabansa ya dago ya kalle su. "Wacce ta yi garkuwa da ku tace ku ajiyar shugaba Habib ne, shin ya wannan zargin yake?". Wata mai suna Aysha ta amsa "karya take yallabai, mu bamu da wata alaka da shi". Ya jijjiga kai. "To yanzu ina ragowarku suke, a wane hali kuka baro su?". "Suna can hannunta yallabai, kuma a gaskiya suna cikin wahala. Mu kanmu yin Allah ne kawai ya tsiratar da mu".

"Shikenan duka zaku koma muhalkanku, hukuma kuma zata ci gaba da bincike domin gano inda ragowar suke. Zaku iya tafiya." Suka yi masa godiya suka fita.


Hankalin Shugaba ya rabu kashi-kashi. Ga matarsa kwance a asibiti bata san inda kanta yake ba, ga zuciyarsa ta kasa hakura da tunanin halin da 'yarsa Anisa da Baffa suke ciki. Ga kiraye-kirayen turawa a bangare daya, wadan-da dayawa a cikinsu ya karbi kudadensu ne kan cewa zai turo musu yara. Duk ya furgice ya yi wani zuru-zuru da shi.


A lokacin ya sami sakon Umaima cewa sun koma gida su takwas da suka gudo, ragowarsu kuwa suna hannun 'yar gwa-gwarmaya. Yana goge sakon likitan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login