Showing 9001 words to 12000 words out of 37846 words

Chapter 4 - Yar gwagwarmaya complete Book by Yar Autar Arkilla.txt

25 Oct 2025

369

wadan-nan da suke hannunmu dan gano meke tsakaninsu da ita."


Ya dasa aya, yana jiran abinda Shugaban zai fada. Shugaba daya zama kamar mutum-mutumi ya fara tsuma. Cikin rawar murya ya fara magana. "Haba dai Sauwam ta yaya wadan-nan 'yan ta'addan zasu amfane mu cikin wannan case? Gwara ma ka sake su su tafi, Fadwa nake son jin ka kama, ba wasu tsageru ba. Batawa kanka lokaci ne kawai zaka yi. Ka sani sarai mugu baya tona aibun mugu. Ba mamaki ma wasu kudin ne suka hada su. Ka yi watsi da wannan kawai ku nemo Fadwa ita ce abar farauta."


Ya takaita yana sauke numfashi kamar wanda ya yi gudun mitoci. Mamakinsa ya kama Asp. Kasancewarsa kwararren ma'aikacin tsaro da bincike, ya tsinci alamomi na tsoro da rashin gaskiya a cikin kalaman Shugaba.


Bai koma cewa komai ba ya katse wayar. Shugaba ya sauke numfashi yana godewa Allah. Dan shi a zatonsa har an gudanar da binciken ne, sun bayyana sunansa a matsayin wanda ya tura su yin kisa.


Ab'ha ya kalli Fadwa dake kallon hotunan manya da kana-nan karuwan da Shugaba yake aiki da su yanzu. A cikin karamin falon hidanta da ya zame musu gurin zama. Yace Fadwa ni kuwa da zaki karbi shawarata da na baki ita. Na tabbata kuma muddin muka yi amfani da wannan shawarar ba karamin girgiza wan-can tsohon zamu yi ba". Ta sauke numfashi zuciyarta na mata tafasa, kamar ko wane lokaci idan tana kallon hotunan. Tana ganin yadda ya kara jefa rayukan 'yayan jama'a cikin bala'i. Ta sauke manyan idanuwanta a kansa tare da cewa "ina jinka".


Ya dan shafi gefen kansa. Yana al'ajabin yadda Fadwa ta zama marar fara'a kuma mara son yawan magana. Yace "abinda ya kamata mu yi yanzu shi ne, mu fara sato 'yan matan nan da yake amfani da su wajen bunkasa kasuwancinsa a nan. Mu tanadi waje na musamman inda zamu tara su. Na san wannan ba karamin tashin hankali zai haifar masa ba. Tsakaninmu da 'yan matan kuwa ba cuta ba cutarwa a hankali muna nuna musu illar abinda suke yi, ga rayuwarsu da ta iyayensu har Allah yasa su dawo hanya.


Kin ga babu mamaki hakan ya zamo mana wata sauka-kakkiyar hanya ta tona asirinsa." Ya kare maganar idonsa a kanta. Fadwa ta yi shiru tana nazari, a ranta cewa take babu shakka duk kaifin basira da tunanin mace, ba zata taba zama dai-dai da namiji ba. Wannan ita ce hanya mafi sauki da zasu bi su girgiza Shugaba kuma su tashi hankalinsa. Duk da cewa bata da burin da ya wuce jefa shi a tashin hankalin amma sam bata taba kawo wannan ba.


Ab'ha kuwa har ya fara cire rai da zata yi magana. Domin ya fara sabawa da wasu halayenta. Sai kawai ya ga ta saki wani lallausa kuma kakkyawan murmushi, wanda tun da suka hadu bai taba ganin irinsa a fuskarta ba. Ta kama hannunsa ta rike gam a cikin nata. Cike da farin ciki tace "har yanzu basirarka tana nan Abba. Hakika wannan ita ce shawara mafi dadi da muhimmanci da na taba ji tun bayan da na fara gwa-gwarmaya. Na gode Ab'ha. Babu shakka tarayyarmu zata zamo makamin tarwatsa zalumcin Shugaba."


Ab'ha ya ji dadi sosai. Yadda ta karbi shawarar tashi, har ma ta nuna jin dadinta a fili. "Babu filin godiya tsakaninmu Fadwa, kin manta duk tafiyar daya ce?".


Ta yi dariya. Abu mafi tsada a rayuwar Fadwa. Tace "haka ne, sai mu fara shiri. Domin na dade da sanin gidajen da yake tara su".


Ta dauko hotunan nan da list na sunayensu suka fara dubawa. Yana budawa tana gaya masa guraren da suke zaune.


*01:30am*
Karfe daya da rabi na daren ranar. Kamar yadda suka shirya suka fito cikin shirinsu. Ita din tana sanye da bakaken kaya na roba, riga da wando. Sun bi jikinta sun shafe, kai kace a nan aka kirkire su. Sai bakar hular sanyi da ta saka bayan ta tufke gashin kanta waje daya. Takalmin kafarta ma bakake ne irin masu shegen tsinin nan. Sai glass da ta rufe idonta da shi wanda shima dai bakin ne. Wannan ita ce shigar Fadwa a duk lokacin da aiki irin wannan na fitar dare ya same ta.


Ab'ha yana cikin kayan sanyi up and down. White in colour. Ya rufe kansa da hular sanyi ita ma fara. Sai takalminsa cover farare. Bai saka wani glass a fuskarsa ba. Haka suka jero cikin takun nuna isa da izza har suka isa gaban wata mota kirar boss dake ajiye a garejin dake ciki matsakaicin gidan suka tsaya. Ba wanda ya yi magana a cikinsu. Suka kalli juna na 'yan dakiku kafin daga bisani suka yi shaking hand, sannan ko wanne ya zaga ya zauna a mazaunin gidan gaba. Ab'ha ne mai tukin ya tada motar a hankali ya silalata suka fice...












*Nasmat* ✍
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)

πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€




πŸ‘¨πŸ»β€πŸ’»πŸ‘©πŸ»β€πŸ’»
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
​​WΙ› Ι‘Κ€Ι› Ι¦Ι›Κ€Ι› tΡ³ Ι›Ι—ucΙ‘tΙ›, MΡ³tiΡ΅Ι‘tΙ› Ι‘Ι³Ι— Ι›Ι³tΙ›Κ€tΙ‘iΙ³ Ρ³uΚ€ ʀɛɑɗɛʀร​.
_____________________________________

Β©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________








*Keep following...*







```page 9```








Bangaren Shugaba kuwa hankalinsa ne ya yi masifar tashi a lokacin da Chaka yake gaya masa police sun kashe masa yara biyu, sun kuma kama wasu biyun. Domin in da akwai abinda yafi tsoro a duniya bai fi tonuwar asirinsa ba.


Zaune yake shi kadai a tafke-ken falonsa yana zare ido. Ya rasa yadda zai yi. Ga wani wahalallen gumi dake tsatstsafo masa a duk kofofin gashin dake jikinsa. A haka ya fara jin karar wayarsa alamar kiransa ake. Saboda halin da yake ciki sam bai yi tunanin duba lamba ko sunan mai kiransa ba. Ya daga wayar da guntuwar sallama. Karar tashin dariyar da ya ji ne ya saka shi saurin cire wayar daga kunnensa, ya duba number. (Unknown) ya gani. wannan ya tabbatar masa da mai kiran "Fadwa ce". Ya fada a cikin zuciyarsa. Dan kuwa ya sani ita kadai ce mai kiransa da boyayyiyar number. Kamar zai katse kiran, sai kuma ya kasa. Yana so ya ji me zata ce masa.


Ya mayar da wayar a kunnensa ba tare da yace komai ba. Fadwa kam dariyarta ta yi mai isarta sannan ta takaita ta fara magana. "Alh. Habib Shugaba. Gaskiya kana da matukar wayau. Sosai nake yabawa zummarka ta son ganin ka kawar da duk wanda ya fara gano gaskiyarka. To ba ma wannan ba. Na kira ka ne dan tayaka murna na ji an kama karnukan farautarka biyu, bayan da aka aika biyu barzahu. Ba shakka 'yan sandanmu na aiki tukuru wajen ganin sun kawar da ta'addanci a kasarnan. Sosai na jin-jinawa aikinsu. Sai kuma ka bani tausayi..." Mai makon ta karasa maganar sai ta koma kecewa da wata dariyar. Nan ma sai da ta yi mai isarta, sannan ta ci gaba da magana. "Ka san inda kake bani tausayi? Duk da cewa ka sani amma bari in kara tuna maka." Ta yi shiru kamar ba zata yi magana ba. Sai can tace "gaskiya ka bata wayonka wajen barin karnukan nan su san cewa kai suke yi wa aiki. ka san fa tsagerun yanzu sam basu da juriya. Ya kake tunani idan suka ji horo suka bayyanaka a matsayin uban-gidansu? Kai inaaa gaskiya abin ba zai maka kyau ba. Fatan alkhairi Shugaba..". Sai ta karashe cikin dariyar nan tata. Sannan ta katse wayar.


Shugaba da ya gama tafiya duniyar mutuwar sassan jiki ya tattara dan ragowar kuzarin da ya rage masa ya motsa hannunsa dakyar ya sauke wayar daga kunnensa. Ya zuba mata ido, kamar mai neman mafita a jikinta. Ya tabbata abinda yarinyar nan ta fada duka zai iya kasancewa.


Nan ma ya koma shiga wani sabon rudu, hankalinsa ya kara tashi. Ya mike daga zaune ya fara zarya a falon, yana kai da komo kamar wanda aka saka matarsa labor. Ya rasa inda zai fara. Tun da yake harkokinsa bai taba haduwa da matsala kamar Fadwa ba. Gashi babu hali ya kira jami'an tsaro game da wadanda aka kaman.


Yana cikin wannan halin ne wayarsa ta koma daukar ruri. Ya dagota yana kallon sunan mai kiran. A take 'yan hanjin cikinsa suka kada. Gumin da yake yi ya ninku. Ya tattara yawun bakinsa dakyar ya yi musu wata hadiya, ji kake "mukut". Tamkar wanda aka shaki wuyansa kafin ya hadiyi yawun. Ya shafi fuskarsa da tafin hannunsa sannan ya koma bude ido ya kalli sunan mai kiran dan tabbatarwa. Shakka babu Asp Sauwam ne mai kiran. Hannunsa ya shiga kyarma ya kasa daga wayar har ta yanke. Ba jimawa kiran ya sake shigowa, bai san ya aka yi ya dauki kiran ba. Sai kawai ya ji muryar Asp yana kiran sunansa ba ko sallama. "Shugaba kana ji na kuwa?". Da ace da wani a dakin to babu abinda zai hana shi jin kukan 'yan cikin Shugaba...






*Ku yi hakuri da wannan, na san ya yi kadan. Ina cikin uzuri ne shi yasa.*





Insha Allah gobe zan ci gaba. Kuma in muku da yawa 😜










*Nasmat* ✍
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)

πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€




πŸ‘¨πŸ»β€πŸ’»πŸ‘©πŸ»β€πŸ’»
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
​​WΙ› Ι‘Κ€Ι› Ι¦Ι›Κ€Ι› tΡ³ Ι›Ι—ucΙ‘tΙ›, MΡ³tiΡ΅Ι‘tΙ› Ι‘Ι³Ι— Ι›Ι³tΙ›Κ€tΙ‘iΙ³ Ρ³uΚ€ ʀɛɑɗɛʀร​.
_____________________________________

Β©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________











*Domin ki kawa ta gari ASIYA ISAH (MAMAN NANA FIDDAUSI) Ubangiji ya raya mana baby rayuwa mai albarka. Sannan ya kara dankon so da kauna da Oga.*





```page 11```






Sannu a hankali yake tukin kamar wanda baya son tafiya. Duk da akwai tsaro sosai a lunguna da sakon garin hakan, hakan bai kawo musu cikas a tafiyar tasu ba. Har Allah yasa suka isa GRA. layi na uku, gida mai lamba ashirin da biyu. Dai-dai nan suka tsayar da motar suka fito. Gabansu gadi duka nufi gate din gidan kamar masu gida.


Da sauri ta jiyo ta kifta masa ido, alamar ya koma mota. Bai tsaya komai ba ya juya zuwa mazauninsa. Da zuwa ta kwan-kwasa gate din gidan bayan ta cire hular kanta ta baje gashin a gadon bayanta da gefe-gefen fuskarta. Ta gyara tsayuwa. Shiru ba amsa, sai da ta koma kwan-kwasawa a karo na biyu sannan tsumakakken buzun ya taso yana tambayar "wane ne a cikin daren nan?". Karamar kofar ya bude yana haska ta da fitila. Cikin gurbatacciyar hausarsa yake tambayarta "waye ne kai?". Ta sakar masa murmushi "sannu Audu. Ni ce Bintu kawar Shakira. Wani fati na zo dare ya yi min kusan nan, shi ne nace bari kawai in zo in kwana a nan."


Ya kara gyara tsayuwa yana nazarinta. Da ganin yanayin shigarta dai ya san duk sune da masu gidan. Sai dai yanayin tsaro sam ba a bashi damar barin wani ko wata ya shigo gidan bayan mazaunanshi ba. Yace "aa kayi hankuri, wallahi bai bari wani siga". Ta bata fuska "haba Abdu kar ka min haka mana, yanzu in ka hana ni ina zan je in kwana kenan?". Duk ya tabbatar ta san su tunda har sunansa take fadi. Amma fir ya hana ta shiga, saboda tsoro da gudun ya rasa aikinsa kamar yadda aka gindaya masa sharadin.

"Kai hankuri yarinya. Wallahi ba laifinmu, laifin masu gida ne". Ya ja baya yana shirin rufo kofar. Ganin zai bata musu aiki, Fadwa ta yi wuf ta shako wuyansa. Kafin ya yi wani yunkurin tuni ta rufe bakinsa da naushi, hade da hular nan tata. Hakan ne ya hana shi yin ihu duk kuwa da cewa ya ji zafin dukan. Ta kai shi gefe ta zaro wata siririyar igiya ta daure hannayensa ta baya ta koma kai masa wani naushin a fuska, wanda ya yi sanadin dakatawar numfashinsa. (Ya suma) ta jefar da shi gefe ta budewa Ab'ha gate din ya shigo da motar ya fito, suka nufi cikin gidan a tare.


Daya bayan daya suka fara bude kofofin da suka tarar suna shiga kafin daga bisani suka tsinci kansu a cikin gidan. Gida mai tarin dakuna da kofofi, dole suka shiga bin dakunan daya bayan daya. Duk inda suka shiga sai sun ci karo da 'yan mata uku ko hudu a gado daya suna sharar bacci. A ko wane daki Ab'ha ne yake fesa musu wani sinadarin saka bacci mai nauyi, sai su buge. Su kuma su ja su ratai-ratai su kai su mota. Haka suka dinga yi har Allah ya basu iko suka kwashe duka matan dake gidan-nan su goma sha bakwai.


Sannan suka tayar da motar suka tafi. A hanyar su ta komawa kam kamar an share babu kowa a kan titunan, kasancewar dare ya kara tsalawa.


Cikin sa'a da nasara suka isa gida, nan ma daya bayan daya suka jido su zuwa cikin babban dakin dake gidan, wanda ba komai a cikinsa sai Capet. Kamar matattu haka suka jere su, sai baccinsu suke a natse, sannan suka fice suka rufe dakin da kye. Ko-wannensu ya nufi dakinsa fuskokinsu dauke da farin cikin samun nasara.


Washe gari da safe, kamar ko wane lokaci haka ta fito ta shirya musu abin karyawa, Ab'ha bai tashi da wuri ba, saboda rashin sabo. Bayan sun kammala karin ne suka fara sabon shiri yadda zasu sato ragowar matan da suke a daya gidansa dake Maagana. Kamar dai wan-can haka shima suka tsara yadda aikin zai tafi.


Sannan ko-wannensu ya mike suka koma dakunansu dan kara samun hutu.


*02:30pm*
Labari ya gama baje ko-ina cewa "a daren jiya an sace wasu mata masu zaman kansu guda goma sha bakwai a cikin garin Kano". Tashin hankali! Lokacin da wannan mummunan labarin ya riski Shugaba, sam kasa tsayuwa da kafafunsa ya yi. Al'amarin da ya tashin hankalin uwargidansa Hajiya Laurat da yaranta duk da basu san takamai-man dalilin hakan ba. Kawai dai suna kallon labarun rana a tashar BBC ne suka ga ya fara kyarma daga tsaye yana neman faduwa.


Nan da nan su Baffa suka kinkime shi suka kai shi dakinsa, da hanzari aka kira likitansa Dr. Yakub. Ba jimawa ya bayyana a gidan, ya kuwa dukufa wajen ganin ya shawo kan matsalar domin Shugaba abu sai sama yake yi. Jiki na karkarwa. Likitan ya samu nasarar samo dai-daituwar numfashinsa. Sai dai yana cikin mawuyacin hali kamar yadda yace. Ya korawa iyalan nashi jawabin musabbabin ciwon na shi wato, damuwa. Domin kuwa jininsa ne ya hau. Irin mummunan hawan nan da ba a cika so ba. Wanda yake yi a lokaci daya. Ya kare da cewa "a irin haka ne in ba sa'a ba sai kuga mutum ya kamu da mutuwar barin jiki farat daya."


Hankulan yaran da matarsa suka kara tashi. Auta Anisa sai kuka take. Likitan yace "ba kuka zaku yi ba addu'ar samun sauki zaku yi masa. Insha Allah nan da dan wani lokaci zai tashi." Ya bukaci daya daga cikinsu ya biyo shi asibiti ya karbowa Alh. Magani. Auta ta mike tana share hawaye. Faisal yace "ki zauna kanwata barin je in karbo". Ta girgiza masa kai alamar aa ita zata je. Baffa ya share mata ragowar hawayen yace "to ku je". Likita ya fice ta rufa masa baya. Sauran kuwa sun kasa fita dakin uban na su. Sun yi cirko-cirko suna kallon yanayin fitar numfashinsa domin ya dan jima da yin bacci.


A asibitin Mai jama'a private hospital. Likita ya faka motarsa ya fito. Anisa ma ta faka tata ta fito ta bi bayansa zuwa ofishinsa. Jikinta kana-nan kaya ne riga da wando. Pink in colour. Rigar iya guiwa wandon kuma pencil ne sai siririn mayafin dake sakale a kafadarta, kamar ba 'yar musulmi ba. Likita ya tura aka kawo masa maganin ya bata tare da addu'ar Allah ya bawa mahaifinta lafiya. Ta amsa da "amin". Ta fita.


Ta shiga motarta ta tayar ta kama hanyar komawa gida. Ta dan yi nisa sosai har ta sauka daga babban titi, ta kama kebabbiyar hanyar unguwarsu. Sai ta ji muryar mutum a motar yana cewa "ki tsayar da motar nan". A razane ta taka birki a tsakiyar hanyar ko gefe bata iya sauka ba saboda tsorata da ta yi. An gode Allah hanyar ba ababen hawa. Ta juyo da sauri dan ganin mai magana a bayan motarta. Juyowarta ke da wuya aka fesa mata wani abu a fuska, daga nan kuma bata koma gane komai ba.



Wanda ya yi mata hakan din ya gaggauta fitowa daga baya ya zauna a mazaunin direba ita kuma ya tura ta a bari daya. Ya tashi motar ya yi ribas ya fice daga unguwar.



Ab'ha kenan. Tun shigowarta asibitin ya ci karo ita, a lokacin shi kuma ya zo siyen sinadarin nan mai saka nannauyan bacci da suke amfani da shi ne a asibitin. Ganin haka yasa ya siyi abin da gaggawa ya fito ya yi wa kansa masauki a motarta, kasancewar hankalinta a tashe bata tsaya kulle motar ba.











*Nasmat* ✍
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)

πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€




πŸ‘¨πŸ»β€πŸ’»πŸ‘©πŸ»β€πŸ’»
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
​​WΙ› Ι‘Κ€Ι› Ι¦Ι›Κ€Ι› tΡ³ Ι›Ι—ucΙ‘tΙ›, MΡ³tiΡ΅Ι‘tΙ› Ι‘Ι³Ι— Ι›Ι³tΙ›Κ€tΙ‘iΙ³ Ρ³uΚ€ ʀɛɑɗɛʀร​.
_____________________________________

Β©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________







```page 12```







*Gidan Shugaba*
Abu wasa-wasa har dare babu Anisa babu labarinta. 'Yan uwa sai kiran wayarta suke bata tafiya. Hankula sun tashi saboda an kira lokita ya kuma tabbatar musu da cewa tun da suka je ya sallame ta ta tafi. Zuwa lokacin Shugaba ya farka amma babu kwarin jiki. Uwar ce ta gargadi yaran da kar su sanar da shi halin da ake ciki na batan'yarsa saboda ganin halin da yake ciki.


Hakan kuwa aka yi. Can tsakaninsu suke ta bulayin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login