Showing 24001 words to 27000 words out of 64206 words
Chapter 9 - HARAMTACCIYAR SOYYAYA Compelet Book by Nafisa Sani Hussein.txt
kukan da yadawo mata tace Aunty lafiya?
Cikin dauriya tace Zazzabi ne kawąi kuma nasha magani tace sory Aunty tace uhm tnx
Ya akayine Menal? Aunty kinji Wai bros zaiyi aure? Cikin bugawar zuciya tace eh, meya faru? Amma shine banda ko labari saida naga Akwatuna yanzu
Akwatuna? Ta tanbaya eh Adakin Aunty shine take fadamin Na Auren brother ne
Ciki Sanyin jiki ta tashi zaune tace Allah yabasu zaman lafiya kiyi hakuri Menal kinji kema Allah yakawo miki naki wanda zaisoki da gaskiya
Cikin jin dadin Addu ar ta tace Amen ni Aunty nama hakura dashi tun ranarda naga yakawo mace cikin gidan nan
Ras gaban Safeena yafadi tace mace kuma? Tace eh Aunty Dâdy yace inkirashi iʼna zuwa nasamu dakinshi Arufe Yabude yanamin magana yaki bari inshiga Ashe Akwai mace Aciki ne
Bayan yarufe nadawo nasa kunne na A bakin kofar domin inji ko ďa gaskene wallahi naji muryar mace tundaga ranar nake jin tsoronshi
Wallahi bros daņ isakane Aunty, tayi wani wawan Ajiyar zuciya don ta dauka da gaske macen yakawo
Takuma godewa Allah da Menal bata ģane ita bace Aranar Hmmm da akwai kallo dón bakin yarinyar baya shiru kokadan
Bayan tafita Adakin ta daure cikin zuciyarta tace dole ne itama ta daurema zuciyarta tunda yafita hanyarta ko son ganinta bayayi yana ta zancen Aurenshi yanzu
Ta mike cikin karfìn zuciýa tanufi baya wurin garden tana kallon ruwan dake gefen lambun wato swiming pool Ahankali tamike tareda zame doguwar rigarda ke jikinta sanin bakowa ke zuwa wurin ba tarege daga ita sai guntuwar shimi iya gwiwa
Dama ko bra babu cikin jikinta na shanunta kamar zasu faso shimin tsabar kunbura da tsayuwarsu kamar Anhura baloon
Cikin hankali take taka step din tana shiga ruwan har ta shige duka tafara nutso aciki ita dai tana kaunar ruwa sosai saida takai tsakiyar ruwan taji kamar taci karo da Abu
Ta dago takuma kallon inda tabugi Abun cikin zare ido tareda saurin mayarda jikinta cikin ruwaņ tana mamakin yaushe yazo nan? dama yana ciki?
Ya akayi bata ganshiba ko sai yanzune da yaganta yashigo cikin ruwan cikin jin haushin kyaletan dayayi kwana biyu
Tace meye haka cikin tsaʼnanin fushi da kuma kishi meye na biyoni nan kuma? yayi wani murmushi kodai ke kika biyoni? Salon intabaki ki ce aa shine don ki dauki Alhakina kika biyoni har cikin ruwa ko?
Tace banason haķa fa malam kafita don Allah yace saidai ke kifita, cikin jin haushi ta juya tafara iyo zata fita hartakai bakin ruwan ta tuna yanda jikinta yake kuma gashi tashiga ruwa
Tasan tana fita zaiga komi na jikinta, Abinda bata saniba koda tafito daga cikin gidan yana kallonta harta tube rigarta wanda yayi sanadiyyar daukewar numfashin shi na wucin gadi
Wanda shine sanadin nutsewarshi cikin ruwan kafin tashigo
Cikin shagwabe fuska tace please kafita don Allah, me kike gudun ingani ? Komai nariga nagani tun lokacinda kika tube rigarki cikin jin kunya tayi saurin juya mai baya
Tace don Allah kabari mana kafïta kawai jin hannunshi tayi Akan kirjinta.......
Cikin daukewar numfashin su Alokaci daya tayi saurin yin baya yarikota baby kinaso ki kasheni ne um? na nisanta kaina dake gudun Abunda zai iya faruwa kenan
Amma me kina Azabtarda zuciyata da kuma gangar jikina gaba daya kinriki tamin kwakwal wa kin hanani tunani mai kyau
Ta kara matsawa yakuma janyota yarungume bayanta still suna cikin ruwan yafara shafo kugunta daga kasa zuwa mararta yana me lumshe idonshi
Cikin matsanan ciyar bukatar kasan cewa da ita yafara shafo kirjinta dàkyau ta cikin shimin jin shimin nason hanashi sakewa da jin taushin Abinda yaki daukar hankalinshi yafara kokarin zameta....
Ai a sittin tafito Aruwan ko tsayawa bata lokaci batayiba ta yayi rigarta tayi cikin gidan da gudu saida tafada dakinta hankalinta yakwanta Allah yasa bataci karo da kowa ba
Shikam ai yashiga uku bama huduba don yama kasa natsa kanshi
_Niko nace waya aikeka Sageer kafara wuce gona da iri fa_
Bata kuma bari sun haduba shima kawai yafara shirin tafiyar shi zuwa new york gashi bikinshi nakara towa
Washe gari jirginshi yadaga zuwa new york saida yaje filin jirgin kafin ya turo mata text _ni natafi new york zanyi kwana biyu so zaki iya fitowa yanzu kidaina boye kanki saboda ni_
Jikinta yayi mugun sanyi don gwara ace suna gari daya ganinshine batayi da ace baya kasar kwata kwata cikin mutuwar jiki ta daure ta tura mai text kamar haka
_wush you a safe journey_
Yaji dadin ganin masage dinta for the first time tunda suke da ita yakuma turo mata wani
_i will missed you my pretty take care of yourself for me i love you somuch and i will always do_
Cikin jin dadi take karanta message dinshi sai duk ta manta damuwarda take ciki Alokacin
Kusan satin da ya dauka A new york yayishine cikin rashin jin dadi yakuma yardar ma kanshi is imposible ya iya rayuwa batareďa itama duk runtsi duk wuya bazai iya rabuwa da Safeena ba
Don tunda yaje baya iya awa daya batareda yakirata ba itama koda yaushe tana makale da wayarta Akusa da ita basu san sunayima juna irin wannnan soyyayar ba sai yanzu da baya nija
Gaba daya sun manta da zancen wani Aurenshi Amarya tayi naci harta hakura ita dai burinta zai cika na mallakar burin ranta so duk koma yayane oho mai itadai Adaura
Yau saura kwana biyu yadawo daga new york yana makale da waya shida pretty dinshi yace baby idan nadawo mezaki bani cikin zakuwa tace yaushe zaka dawo?
Yace tell me me zaki bani idan nadawo? Cikin tunani tace me kake so? Yace ke nakeso pretty !
Hmm tayi Ajiyar zuciya tace ni dama takace yace no kina min rowar jikinki bayan kinsan ina sonki sosai ina kuma bukatar kasan cewa dake,
Tayi shiru don itã batada Amsar tanbayarshi yace jibu zan dawo wace irin tarba zakiyi min? Tace Allah yadawo dakai lafiya kit takatse kiran
Duk jikinta yayi sanyi tasan tana dakon son wahala ne kawai saboda Aure zaiyi tasan yanayin Aure yasamu kwanciyar hankalinda yake nema zaimanta da ita
Ita kukama yanzu baya zuwa a idonta don tagaji da yi
A yaune Sageer zai dawo daga new york wanda yayi daidai da saura sati daya adaura mai Aure da Humaida
Tun jiya ya Aika mata da text cewar ta tar beshi A yau don ita yakeson fara gani da yashigo nija don haka su hadu Agidanshi da suka taba zuwa idan kuma taki zaiyimata Abinda yayi niyya koma Agaban waye......🖊
*Opps hannuna ciwo fans Afuwan muhadu Next page*
[2/19, 3:21 PM] Aysher D Yuguda: 🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵
*HARAMTÃCCIYAR SOYYAYA*
🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵
(romantic love story)
Story writing by
_NAFISA SANI HASSAN_
Maman Ammar
💫FAGEN MARUBUTA WRITERS
ASSOCIATION💫
_(gidan zaman lafiya da yarda da juna🤝insha Allah)_
Dedicated
_To you my love my happyness, you Alone my hubby may Allah s.w.t protect you every were you go_
2⃣0⃣
Yau gaba daya ta tashi jikinta Amace tsabar far gabar Abinda zai biyo baya "
Ga shi Aunty Nena tace Anasa ranzuwan yan uwan baban Sageer din, saboda Auncle ya fada musu saboda fita daga hakkinsu,
Tayi ta mamaki Alokacin da Aunty take bata labarin Sageer don ita bata taba tunanin ba jininsu bane,
Sai kuma yabata tausayi sosai da jin labarin yarasa iyaye tun yana karami, yan uwan babanshi nacikin gari Amma sun manta da dan dan uwansu guda daya tilo daya mutu yabari"
Sai Amininshi yarikeshi kamar dan cikin shi gaskiya sai yau ta ji mutumin ya kara kima a idonta,
"Kuma yaka mata tarufe ido kobata so tayimai biyyaya ko baʼnza yakula mata da wanda takeso Arayuwa"
Karfe goma sha biyu naranar ya sauka A garin na Abuja jirginsu na landing yatura mata da text cewar ya iso"
'Gabanta ya mugun faduwa, tsabar tsoro da firgici don gaskiya bazata iya fita daga gidan ba saboda kasan cewar jumu a ne duk sun dawo gida da wuri"
Ta tura mai text _am sory i c'nt_ yayi murmushi domin yasan bazata taba yarda tajeba da ganģan yakeyi"
Ita dai duk A tsorace take da lamarin don tasan halinshi bayada shakkar yin Abu idan yace zaiyi"
Sunata shirya Abinci A dining table ya iso gidan cikin takunshi irin na maza masu ji da Aji dakuma hatimin nasara"
Gabanta ya mugun faduwa jin takunshi da kuma kamshin jikinshi' cikin lallausar sallamar shi yashigo Aunty tace maraba da yan New york,
Itakam ko juyowa takasa yi tsabar tsoron kar yaja musu magana" yaran suka fito da gudu tareda rungumeshi şuna oyo yo"
Menal ma tafito daga nesa take cemai welcm bros' yace tnx little" kingirma ke yanzu bakya mun oyoyo ko ?lallai little ta zama big girl"
Aunty tafara dariyarsu ita ko Menal Azahirin gaskiyatsoronshi takeyi yanzu" shikuwa duk maganar da yakeyi rabin hankalinshi na gefenta,
Cikin salonshi yace Aunty ita wannan bata gaida mutane nè? Aunty tace wai Safeena? Son ai kai yakamata ka gaisheta" saboda matar Auncle dinka ce,
Cikin basarda zancen yamatsa daga inda take tsaye ta juya musu baya tanarikeda kujerar dining, saida yakai gab da ita yarage murya"
"Am back my pretty ware is my promise? Cikin kaduwa tayi saurin juyowa don ganin ko ba a ganin me yakeyi saitaga Aunty tabar falon saidai yaranda ke tsakiyar falon,
Tayi saurin fara tafiya domin barin wurin, yariko gefen doguwar rigar datasa cikin rada yace pretty bakiyi missing dina ba gaskiya kamar yanda kika ce"
Tayi saurin kallonshi tace please stop it za a iya ganin mu fa" i dont care, idan bakyaso Aganmu muje dakina kihada min ruwan wanka if not i will hug you hare"
Cikin zaro idanu tace please Sageer! Yakara matsowa yace wow !! Please say it again, tace what? My name. Cikin sauri ta kama hanyar dakinshi taʼna waige.
Tunda ta juya yake faman binta da kallo ko ina najikinta na motsawa kamar da gayya ma takeyi" duk ta saukar mai da kasala da kyar yaja kafarshi yabi bayanta,
Yana shiga tana fitowa daga bathroom din cikin sanyin jiki tace na hada" tajuya zata tafi yana kallon ta har yanzu taki yadda ko ido suhada.
Tasa hannu Ajikin kofar zata bude yamanne Abayanta kamar mayen karfe' tareda sauke Ajiyar zuciya yace preety! Bakiyi murna da dawowana bane?
Look at yanda kiketa dauke kai kina shareni menayi miki? Cikin sanyinta tace please stop it "yayi saurin juyo da ita suna faciñg juna,
Yace Safeena!meya faru? Tafara hawaýe cikin sauri yace oh no baby what hapend? Tace bakai bane, cikin sauri yace menayi ?
Aurefa zakayi shikenan kamanta dani takarasa cikin kuka, Hmmm yasauke ajiyar zuciya tareda cewa imposible' idan har zan iya mantawa dake that means zan iya mantawa da kaina"
Safeena kinsan irin yanda sonki yashiga jini na bansan yanda zan iya fassara miki yanda nake jinkiba, dole ne inyi Aure Safeena dole ne takamani.
Inbakyaso ki rasani ina Azabtuwa" cikin wani irin yanayi tadaga kai ta kalleshi tana mai kallon nice kenan bana Azabtuwa?
Abinda takeso tafada mai kenan Amma takasa saboda tanajin kunya' ta fisge hnnuņta da yarike zata fita ya kuma fisgota yamanneta da kirjinshî
Kibarni inji dumiñki baby i realy missed you tace leav me kaje wurin Amaryarka kadaina tabani, nima kabarni inje wurin nawa mijin tajuya yakuma fisgota cikin fushi"
Bana fada miki banaso ba kidaina kiramin mijinki Agabana banaso" oh nice kake min zancen Aurenka Agabana yanzufa kace.....
Saikuma takasa taji kunyar abinda tafara fada, nace me? Yafada cikin murmushi
Ta sunne kanta yace inajinki kikarasa mana.
Tasamu dakyar ta gudu daga dakin cikin Ajiyar zuciya ya koma yakwanta tareda runtse ida nunshi ba Abinda yake tunani sai ita,
Hayaniyarda sukaji Agidan shiyayi sanadin fitowar su gaba daya daga cikin dakunansu ganin wasu mutane su ukû da wata tsohuwa sai maza magidanta guda biyu
Matar nata sababi tareda cewa ina jikanta dama jikanta na raye? Aka rufeta akace mata danta yamutu dashida jikanta guda daya duk suka fito sunata mamaki wannan kuma wacece ga Alhaji mu azzam nagefe Azaune
Cikin sunkuyarda kai yace baba kiyi hakuri nayi kokarin cika Alkawarinda na daukar wa Amini na nacewar kobayan ranshi zankula da Abinda yabari ďa kuma dukiyarshi"
Domin gudun kar anakasa mai yaro Akan dukiyar da yabar mai kuma kobayan mûtuwar tashi naje har gidan naku domin In yimuku bayani Akan komai sai nasamu bakya nan
Kinje kauye nakuma yima bala gashinan bayanin komai har adreshina nabashi koda kundawo Amma banga kowaba sai bayan kwana biyu yazo min da zancen wai inbasu dukiyar dan uwansu da kuma dansu
Wanda Alhamdulìllah margayin kafin yarasu saida yabar komai Arubuce har lauyanshi yasa hannu Akai ,
Don haka yarodai yanzu ya mallaki hankalin kanshi idan kunjashi Ajikinku falillahil hamdu idan kuma kunki nidai nayi kokarin sauke nauyin da ke kaina,
Cikin kuka tsohuwar nan take cewa Amma dai bala kaci Amanar dan uwanka duba iriņ wahalar dayayi daku Arayuwa Amma Abinda zaku sakämai dashi kenan?
Kai kafadamin dana yamutu shida iyalinshi" nasan narasa dana mai son farin cikina don me zan bibiyi dukiyarshi mezanyi da ita? Wanda yatara tama yatafi bare ni kwana nawa yarage min?
Tace mu azzam kacika Aboki nagari karike Amana da Äminta karike maraya iya karfinka Allah yasaka maka da mafificin Alkhairi"
Su Aunty dake zaune sukace Amen shikuwa Sageer tunda yafito yake sauraren wannan tatsuniyar. dama danginshi na nan Araye ? Suka barshi yataso kamar wani wanda baida kowa
Sai wa innan bayin Allah tsohuwar takuma cewa ina jikana? Cikin doki Aunty tace Sageer zokaga kakar ka gaba daya jikinshi ya mutu cikin sanyi yakaraso cikinsu yasamu gefen tsohuwar ya zauna
Tace masha Allah yaro ya biyo mahaifiyarshi da farin fatar da komai Allah yama Albarka dan nän duk suka Amsa da Amen tanuna mai maza biyun tace kannin babanshi ne su
Ga bala shine babba sai Ibrahim gashinan binsu kawai yakeyi da kallo cikin jin mamaki bayan yatashi da sanin danginshi basa kusa Ashe anboye mai gudun Abinda zai iya faruwa ne
Tace yanzu kai bala tunda kaga bikin ya matso sai kaje wurin dangin mahaifiyarshi suma Afada musu don sunyita jelen zuwa sunada zumunci sosai kobayan ran yar uwarsu sukawomin Abin Arziki
Allah dai yajikan dannan da matarshi Suka Amsa da Amen duk mamakin yaki sakinshi har dangin mamanshi nagari?.......🖊
_To sukuma suna ina? Suwaye dangin momyn nashi?_
*Yakamata duk suzo Akwaso shoki dasu ranar Auren Sageer*
[2/19, 3:26 PM] Aysher D Yuguda: 🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵
*HARAMTACCIYAR SOYYAYA*
🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵
(romantic love story)
Story writing by
_NAFISA SANI HASSAN_
Maman Ammar
💫 *FAGEN MARUBUTA WRITERS*
*ASSOCIATION*💫
*_(giďan zaman lafiya da yarda da juna🤝insha Allah)_*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
2⃣1⃣
*Bismillahir rahamanir rahim*
Har suka gama surutansu baice ko maiba yana sauraren su ne kawai.
Safeena daman dataga zancen bai shafetaba kawai ta sulale ta koma inda tafito.
Şhima miķewa kawai yayi yafice Abinshi tsohuwar nata shimai Albarka da kuma jin dadin ganin jikanta na danda tafi soshi duk da yana dan fari.
Direct wurin Amininshi yanufa wato Yusuf yana bashi labarin Abunda yake faruwa, cikin tayashi farin ciki yace”
“Dude baka farin ciki ne?.”
“Yace ni gaskiya banji wani fariñ cikiba namafi bukatar ganin dangin momy na saboda sanadin su ne, na nisanta da yan uwan mahaifiyata Akan banzar dukiya.”
Yusuf ya dafashi yace”
“Dude ka gane wani Abu, kai bazaka san dalilinsu na yin hakan ba, Amma ni ina ganin Akwai dalili mai karfi tunda kuma yanzu ka mallaki hankalin kanka zaka fahimci komai Ahankali”.
Tunda yafita suke cigaba da shirya yanda zasukai kayan Auren A tsakaninsu.
Alhajin yace”
“Yaka mata Ayi bikin A wajensu suma Afita hakkinsu.”
Kakar tace “A‘a saboda me?”
“Ai har gobe kaine kafi kowa cancantar wakilta komai Akan Sageeru.”
Yace “nagode”
“Amma nima Inada dalilin yin hakan, ku gafarce ni Da farko nayi gaban kaina Amma yanzu dole ne insanar muku.”
“Wato tun lokacinda ya mallaki hankalinshi yaki zaman nigeria gaba daya sai ya dade bai shigoba saidai ni inje inganshi gaba daya yana rayuwane ba walwala narasa Abinda yasa A zuciyarshi.
Shine nafara yimai zancen Aure sai yafara yimin yawo da hankali, daga karshema da ya samu yabar kasar saida nayi fushi sosai kãfin nasamu yadawo Amma maganar gaskiya.
Na daura mai Aure batareda saninku ba shima batareda yasani ba don haka nake son yanzu inbashi hakkinshi sanin danayi ita wannan yarinyar ita kadai nake ganin suna tare tun suna school,
Shiyasa na bashi damar ya Aureta saboda gudun shiga hakkinshi kuma maganar gaskiya baisan da zancen Auren danayi maiba na farkon kunji dalili na
Don haka yanzu idan ya Auri zabinshi sai insan yanda zanyimai bayanin ita dayar matar tashi'
Haka sukaci gaba da tattaunawa Atsakaninsu Har suka tsayarda magana A tsaka ninsu kuma shima yarokesu da don Allah kar wanda yayimai zancen Auren da ko Aunty Nena yanzu takeji"
Tana kwance ba Abinda takeyi sai Aukin chat Ahakane Aunty Zaliha takirata take mata magana Akan Abinda ummi ta fada mata yanzu cewar Anga yaron yayar ummi,
Tafara tanbayar bata ganeba? Dama Haliya mama nada yarone? Tace no yaron sistern su data rasu aikinada labarï ko duk danima bawai nasan komai Akai bane,
Sun dade tana mata bayani wanda ita sam bata dauki zancen da wani mahimnci ba saida suka rabu Awaya sannan tafara tunanin how comes?
Yama za ayi hakan tafaru bayan Ance tare sukayi hatsarin da iyayenshi? Ta tabe bakinta irin she don't care,
Wayarta takuma yin kara taduba taga mai kiranta cikin mamaki tadaga kiran tareda slm cikin sanyin jiki yace pretty!
Yar taji har tsigar jikinta natashi tadan kara kishin gida "ya kuma cewa kina jina kuwa? Tace" eh Ahankali
"Kizo please ke nakeson gani Akusa dani please i need a shoulder to cry, kinsan ke kadaice farin cikin Sageer please come to me.
Gaba daya yabata tausayi musamman data tuna Abinda yafaru taga kuma yanayinda yashiga"
Ga mugun sonshi dake cikin zuciyarta da kuma begen kasan cewa dashi kawai tasamu kanta da cewa Am coming ware are you?
Cikin jindadi yace tnk you kifito kisame ni Awaje ina cikin mota batareda tayi tunanin komaiba ta mike tareda sanya dogon hijab dinda tacire ,
Domin kana nan kayane Ajikinta kuma wandon ya dameta sosai kuma rigar komai ta bayyana shiyasa taķeta yawo da hijab gudun dan rigimarta kar yariki ce mata
Ga kuma mutane tasanshi da mugun kishi saikace shike Aurenta? Ta kofar baya tafita don tanajin hayaniyar mutane Afalon har yanzu
Tunfitowarta yake kallonta cikin híjab din yamata kyau sosai Azuciyarshi yasan dalilin sa hijab din don yasanta da zancen sa kana nan kaya,
Yayi murmushi ganin yanda taketa famar kama hijab diň harta iso wurinshi ta bude gaban motar ta zauna batareda ta kalli ko gefenshiba kallonta kawai yakeyi"
Jiyake kamar ya dauketa yagudu tsabar sonta da kuma yanda