Showing 21001 words to 24000 words out of 41738 words
Chapter 8 - Aishah-Saddiqa book 4 end complete by Takori Kabara .txt
Prince yace "Dade ko na koma bani da nitsuwar yin aikin, gara dai inyi ta fama ko zata haqura. in kuma taqi haqura sai na koma din.
It seems that’s the life my own twin thinks i deserve, a lonely, sad life, unworthy of pure happiness… and apparently you and Nenne too....".
Prince ya furzar da numfashi me daci a kasalance ya tashi zai wuce gidansa. Dade yace "why will u say that?" A marairaice Prince yace "toh ba cewa kukai ba ruwanku ba Dade? Ni iyayen aysha basu sanni ba ku suka sani. And if we are being honest I am nothing but good to Aysha.
Ita in yarinta ya debe ta ba se a duba ni ba. Ni da ba ni nayi laifin nan ba and also ba ni nasa Taiwo ba. Amman duk laifin ya dawo kaina kuma kunyi shiru kunce ba ruwanku. Gaskiya i won't forgive Taiwo for this Dade she really did hurt me…." ya tashi zai tafi ya juya kenan sai kuwa sukayi ido hudu da ita. Taiwo. Jikinta yai sanyi, tazo ne immediately don Dade ya aika a kirata dazu.
Ko kallonta Prince baiyi ba ya fita ya tafi gidan sa.
Nan iyayen sukayi mata tatasss, don Nenne ma taji me yace ma Dade tana daga dakin Dade din, kamar yadda Taiwo taji itama tana shigowa. A ranta ta fara nadama. Ga nasihar da iyayen ke mata suna kuma nuna mata ta butulcewa son da Kehinde yake mata in har itace zata saka shi a wannan halin.
To duk wannan ya taru yasa Taiwo ta damu, a lokacin ta baiwa iyayensu haquri ta koma gida ta wuce ta sai tiket din tafiya UK.
Bayan fitarta ne Dade da Nenne suka kara tattauna maganar, suka aje lallai Friday zasu je Gombe takanas suyi bikon nan da kansu. Alamu sun nuna fa Hamma yana ta iyo a kogin soyayya. Babansa kuma yasan basu iya so ba, gara ya taimaki magajin sa. Nenne har sallahr nafila tayi ranar ta godiya ga Allah ganewa data gama yi Hamma Abdulrasheed yana son Aisha, ga kuma irin matakin da ya dauka kan Twin dinshi Taiwo da cikinsu da ita kanta Taiwo din babu wanda ya zaci zai iya hakan akan Taiwo. Ta san ko da wasa bazai kara barin wani ya taba Aisha ba, dan haka zasu shirya nan da kwana uku suje Gombe, yau talata, toh ranar Friday ko Saturday zasu je gombe.
Shi Prince bai sani ba ya tafi gidansa haka ya kwana zuciya ba dadi. Sai asubahi ma bacci ya dauke shi, yana tashi yaga ba amfanin zaman Lagos. Bari kawai ya koma Gombe din sai yayi jiran hukuncin Baba Barau a can.
Nan Hamma ya hada 'yar akwatin tafiyarsa ya kira nenne a waya yace zai koma Gombe. Nenne tace ko lafiya ince ko? Prince yace "toh Nenne ai gara ina can in yi ta matsa musu kawai Nenne. Idan Kuma har lokacin basu yarda ba zan tafi inyi reporting wurin aiki…
Tawakkaltu Alallah… na fawwala wa Allah".
Nenne sai taji ta kuma jin tausayinsa masa je ka Hammansu Allah ya ba da sa’a kaji, Allah kuma yai albarka albarka Annabijo".
Prince yace amin Nenne". Ya tafi a ranar ya hau jirgin Gombe.
Oummana sai gani tayi baqon shekaranjiya ya dawo. Tace "yaya dai Abdulrasheed?" Sai yace "nan zan zauna, sai an bani matata" Ommana sai ta fashe da dariya tace, "ah lallai Indo ta murza kambu, sarauta ta fadi" Prince yace "ai Oummana warwasss! Sarautar nan ta fadi. Aisharku itace mai mulkin".
Me Oummana zatayi ba dariya ba. Tace "sai ka shirya kaje ai" Prince yace "dole ai Oummana… ki mun addu'a ni ko ganinta ma na samu nayi yau". Zuciyar Oummana fessss! Yau ace Abdulrasheed yasan martabar mata a gare shima babbar nasararsu ce. Prince yana fita tasa ai mata kiran uban kasa.
Da Uban kasa ya tashi fada sai ya zarto sassan mahaifiyar tasa, nan Oummana ta fada masa komi da ya faru har dawowar Hamma Gombe yau. Uban kasa yace "wannan ai abu ne me sauki Oummana, ai dan nasan abinda ya faru kenan dana aika tun ranar da tazo. Wulaqanci ba dadi amman sai ayi la'akari da ba laifin sa bane. Ayi masa afuwa".
Oummana tace "ai ina sane da ban fada maka ba. So nake shima yaji a jikin sa, kuma inga gudun ruwan iyayen sa, in har zuwa karshen mako naga babu wani canji se kuje da auta (Abdulmajeed) dan Allah ayi mana bikon Aisha".
Uban kasa yace "bakomi Oummana ".
Shi kuma ya tafi ya sake daukar wanka, yau ma cikin brown filtex yadi, ya daura hular manyan matasa na zamani wato 'Tonak' kalar kayan, ya yi fes cikin shiga ta kamala, zati, haiba, kwarjini da kamala duk sun bayyana tare dashi, ko makiyin sa ya ganshi a wannan lokacin sai yace "fatabarakallahu ahsanil khaliqeen".
Domin yau Hamma a ruwa biyunsa ya fito, Malam Buhari ya daukoshi zuwa Jeka da fari.
Prince yai sallama a gidan su Aysha Baba yunus ya fito yace "laaa Abdulrasheed kai ne tafe?" Yai murmushi yana dukar da Kai, suka gaisa da Baban Aisha, yai masa iso zuwa ciki, Abba ya tambayi su Dade. yace "inace shekaranjiya ka tafi ko baka tafin bane?" Yace na tafi Baba. dazu na dawo". Yace ina Ummanmu?" Abban Aisha yace ta je gidan Baba Barau bikin 'yar sa Maryamu akeyi. Jibi Jumaah za'a daura auren bayan sallar Jumaah. Sun tafi jere wai.
Malam ya dubeshi Yana murmushi ya ce "ka san mata da hidima".
Prince yayi shiru. Cikin damuwa. Malam Yunus yace "Abdulrasheed ba nace zan kira ka ba?". Yace "Babanmu kayi haquri wallahi ko na zauna Lagos bani da nitsuwa, gara dai in dawo Gomben in zauna jiran hukuncin Baba Barau". Malam Yunus yace "ba ance ana ta kiran ka wurin aiki ba?" Yace "na basu excuse sun qara min sati biyu, shiyasa nace gara na dawo nan din". Sai yayi shiru.
Malam Yunus ma duk sai yaji wani iri, yace ba damuwa in an jima zani gidan nasa daman, zan masa magana kaji?"
Prince yace "toh Baba. Nima wai da zuwa zan yi in gaishe shi". Yace "toh babu laifi".
Yana barin nan yace wa Buhari ya kai shi gidan Baba Barau. Ai kuwa ya samu gida makil da jamaa ana ta hidimar jere yau da kawo lefe.
'Yan uwan mijin sun tafi kenan Prince yai sallama, dan Baba Barau ya fito yaje ya fada masa mijin Aisha yazo. Nan aka masa iso zuwa ciki.
Wato duk hayaniyar da ake a gidan Malam Barau Hamza, jikake kamar anyi ruwa an dauke tsit!!!!! akayi. Lokacinda Prince ya keto jamaa ya ya wuce zuwa falon Baba Barau, kwarjinin nan na masu sarauta, gashi dai ba girman kai, amman ana ganin sa an ga basarake, haiba, mulki ado, kai komai ma!!!
Hamma yayi tsugunno a gaban su Baba Furera yai masu gaisuwa jama’u (in general). Auwalu babban Dan Baba Barau da ya shigo dashi yace dasu "mijin Saddiqah ne"". Ga dangin Aisha gabadayansu sun hadu, nan aka sake gaisawa, ya miqe zuwa cikin falon Baba Barau. Nan aka bar 'yammatan family dinsu Aisha da kawayen amarya da santi da lashe miyau, Saddiqah na tsaye jikin window taji muryar sa, ta juyo tana kallon sa ta tagar, har wata rama taga Hamman nasu Firausi yayi, amman ya zuba kyau Masha Allah.
Tana ganin yadda 'yan banzan cousins dinta sai kallon sa suke tace kamar mayu, a ranta ta ce "mayu kawai, mtsw". Da taji ya Auwalu yace mijin SIDDIQAH ne she was proud!!!!
Sai daga baya ta tuna tace fa ta gama auren. Sai ta koma ta zauna a gefen gado, ta fara tunani.
Prince ya isa palon Baba Barau ya zauna a kasa ya gaishe shi cikin girmamawa, shima ya amsa. Ya tambayi su Nenne yace suna lafiya suna gaishe shi ya sunkai da kai. Baba Barau ya dauka zai masa maganar Aisha yaga bai ce komi ba.
Yace "Babanmu ashe biki ake yi". yace "eh wallahi, wa ya fadi maka?" Yace "Baba ne ya fada min dazu. Allah ya basu zaman lafiya. Yaushe ne daurin auren?" Baba Barau yace "jumaa ne in sha Allah". Prince yace "toh Allah ya kaimu. Allah yasa ayi damu", Baba yace "Amin".
Zuwa can kuma Prince yace "Baba inzo daurin auren?" yace "ah me zai hana in kana nan kazo". yace "ai ina nan ma in sha Allah".
Baba yace "toh Allah ya kaimu". Yai shiru dai, can kuma yace "Baba zan tafi kuma dan Allah ina kara baka hakuri. Waman gaddarallahu hakka qadrihi…. Allah ne ya qadarta faruwar abinda ya faru kuma wallahil azim bazan yi kaffara ba, bazai kara faruwa ba. A gafarce ni don Allah. Baba kar kayi min hukunci da laifin yar uwata. Allah ya Kara hakuri Baba sai jibin in sha Allah".
Ya tashi zai tafi, Baba Barau sai yaji duk ya daure shi da jijiyoyinsa, yayi murmushi yace "Abdulrasheed kenan, ni zaka daure ko?" Yayi murmushi shima yace "ah ah Baba".
Su duka biyun suna murmushi suka rabu.
**** **** *****
TAIWO
Ta sauka gidan mijinta a Lancaster da yamma lis, ta isa ga kofar shiga tana ringing bell. Ana bude kofa taga wata kyakkyawar bafullatana da mijinta Toufeeq a bayanta, ga yaranta biyu dasu, da wani kyakkyawan Baby din dauke a hannunta.
Wani irin shock ne ya kama Aunty Taiwo, tace "Toufeeq what is this?" Yayi mata kallon rashin tsoro ya ce mata "matata ce itama. Sunanta Hauwa-Maijidda".
Ya dubi Maijiddar yace mata "Maijidda this is Taiwo, Maman Kiki da Abdulhakeem".
"What???"
Sai ga Murjanatu ta sulale ta zauna a dandaryar kasa a bakin kofa.
Ta daga ido ta kallo matar, sannan yaran, in zata tuna ta taba ganin hoton yaran yace mata yaran abokin sa ne, wanda suka je auren sa a Yola….
A nan komai ya dawo mata, zuwan sa Yola auren aboki, ashe nasa auren ne.
A cikin ranta sai tana ayyana alhakin aisha ke bin ta…. Taiwo tace "hasbunallahu wa ni'mal wakil… Toufeeq......". Sai kuka wiwi.
Toufeeq ya soma yi mata bayani cewa "he doesn't want to hurt her ne, shi yasa yai aure bata sani ba, don yasan ta da bala'i. He needs peace in his life da matar da zata damu dashi.
Yace ta dawo UK tace baza ta bar aikin asibiti ba, toh shikuma he needs someone close to him, wadda baza ta ke bashi ciwon kai ba.
Taiwo ta kara jin muguwar nadama, nadama mara misaltuwa, tace komawa zatayi, Toufeeq yayi ya lallashinta ya kuma fada mata in zata kwantar da hankali ta zauna toh, if not zabi ya rage nata, amman aurensa da Maijiddar sa ba fashi.
Taiwo a cikin satin ta dawo Nigeria. Koda ta sauka. Gidanta na Lagos ma kasa shiga ta yi tunda dai Toufeeq ne mamallakinsa. Dole gidan iyayentan dai ta dosa da tarin nadama a tare da ita, don ta kira wayar Kehinde ya ki dauka, ta je gidansa maigadi ya ce mata ya yi tafiya Gombe.
Zuciyar Taiwo bugawa ne kawai ba ta yi ba, da abinda Toufeeq ya yi mata, ta zama tamkar zararriya, har magana zaka ga taan yi ita kadai, tana ta gaya wa kanta alhakin Aisha da Abdulrasheed ne ya hana ta kwanciyar hankalin zaman aure, ya tagayyara nata farin cikin auren.
Domin don wulakanci irin na Baban Kiki ma cewa ya yi saura ta je ta hada masa bomb a gida, don ba wanda ya san ya yi 'secret marriage', ko a nashi family din kuwa, don yarinyar zuri’arshi bazasu barshi ya aureta ba, kasancewar diyar talakkawa ce sosai a garin Yola ya aurota, shekarun baya yaje yin wani project daga European Union ya ganta tana talln fura da nono ya aura. Babanta ma baduku ne.
Don haka daga Nenne har Dade babu wanda ya san dalilin zuwan Taiwo gida rana daya, a taurin zuciya irin nata, da rashin tsoro ko shakkar kowa da kowa ya sani, suka ganta duk ta sauke kai, ta zubda izza, yanayin da suka ganta a ciki ya basu mamaki sosai.
Kuma tana zuwa gida ranar Friday da sassafe taga ana ta shiri su Nenne zasu Gombe. Taiwo ta fashe da kuka ta roki su Nenne suyi hakuri tun ba'a je ko'ina ba taga me tagani.
Nan ta fada ma Nenne komi tas, ai kuwa Nenne batayi mamaki ba don yasan Toufeeq yayi hakuri da Taiwo ba kadan ba, nan ta sake yi mata nasiha mai kashe jiki da huda zuciya. Tace zasu je ne su yi bikon Aisha, Taiwo tace zata bisu tunda itace tai laifin zata je ta basu hakuri. Su Nenne suka ce "toh".
Da hantsin ranar jirgin DANA Air ya tashi dasu Gombe.
A gidan Oummana aka sauka. Oummana se ganin su tayi daga sama dukkansu, tace "daga ina haka?" Nenne tace "sunzo biko" Oummana tace "ai ni daman ido na saka muku, da baku zo ba daman anjima zanje gidansu Aisha da kaina inyi ban hakuri".
Nan Oummana ta hangi Taiwo, aiko Oummana ta ciwa Taiwo mutunci son ranta, tace "Ashe tareda tabbatacciyar kuke tafe?" Oummana tayi Mata tatas. Uban kasa ma da ya shigo ya ci wa Taiwo nasa. Taiwo tai kuka har ta gode Allah idon nan sun kumbura pummm.
Sai ga Prince nan ya shigo around 11am, yana zuba wani irin kasaitaccen kamshi, ya sha fararen kaya, yana riqe da babbar rigarsa a hannu, da hular sa Tonak ash colour, wato kalar zaren da akai aikin kayan, gabadaya suka juyo suna kallon sa.
Surprise yaga Nenne da Dade bai ma kula da TAIWO ba. Nan ya shigo ya gaishe su, har suna hada baki sukace,
"ina zaka je haka?"
Prince yace daurin aure zai je, uban kasa yace "a ina?" Hamma yace "Baba Barau ke aurar da diyar shi" Oummana tace kace "biko kake tayı. Wannan ado haka Hammansu ai dole a baka Aisha Indo yau!".
Prince ya saki wani kasaitaccen murmushi yace "Allah ya amsa bakin ki Oummana" duk suka ce "amin".
Dade yace "muma biko muka zo ai, amman tunda biki ake yau zamu bari sai gobe sai muje, Prince yace "ah ah Dade, yaya kunyi niyyar alhairi zaku fasa kuje kawai yanzu" duk suka hau dariya, uban kasa yace ban san ka da gaggawa ba, yau da gobe ai duk daya ne. Yana juyawa sai yaga Taiwo duk tayi zuru-zuru. Sai yaji ba dadi, yace "lafiya ke kuma haka?" Sai kuwa Taiwo tasa kuka, tazo ta rungume shi tace I am sooo soo soo sorry Kehinde. I love u so much, I became selfish and possessive ban ma sani ba.
I am extremely regretful of what I did, and i will do anything to make it right. Kayi hakuri.
Iyayen na kallon su da Kakar su, da zuciya daya ya riko hannunta, yace "Allah ya yafe mana bakidaya Taiwo, Allah yasa kin canza hali kenan har abada", duk aka ce Amin. Sai suka baiwa kowa tausayi musamman Prince, don yana son yar uwarshi.
Kehinde akwai yi wa mutane uzuri. it was an emotional moment tsakaninshi da Taiwo dinsa yau. Yana yi mata murmushin afuwa itama tana masa na godiya. Daga bisani ya kalli agogo yaga lokaci ya tafi, yace "kai bari in tafi kar nayi latti". Ya saka hula yana musu sallama. Uban kasa yace "ah ah, ai baza ka tafi haka ba, yace da Kawunka zaka tafi ya raka ka. Yau a basaraken ka zaka je musu, ko Baban Aisha Indo ya daina ja maka rai".
Sarki Ahmadu Jallo Umar yayi gyaran murya sarkin dogarai daga bakin kofa ya ce "Ran sarki ya dade, ina kusa", Sarki yace "a kira azo a daura masa rawani, a hada mota, kuma a kira Galadima da Waziri Abdulrashid ya wakilce ni a daurin auren da zashi yau, a hada convoy, a hada dogarawa!!!".
Sarkin dogarai cewa yake "an gama Uban kasar Gombe, maganarka doka ce!".
Nan ya buga babbar riga ya wuce zuwa cika aikin Sarkin sa, jikinsa na zikiri.
Hamma ya bata fuska ya dubi Kawunsa Uban kasa yace "is it necessary? Kar