Showing 33001 words to 36000 words out of 41738 words

Chapter 12 - Aishah-Saddiqa book 4 end complete by Takori Kabara .txt

24 Nov 2024

2298

zuwa kananan kaya farar shirt LV da bakin wandon Jeans. Yace "toh Oummana dare ya fara zan maidata" Oummana tace "Aisha nagode Allah ya kara albarka" nan Aisha ta mikawa Oummana sakon Ummanta. Ga Oummana da son Sandal da Oud. Nan tayi ta godiya,ta kuma sa aka miko mata babbar jakar data shiryawa Aisha tsarabar da zata tafi dashi gida.


A hanyarsu ta dawowa ma Prince na makale da kafadun Aisha Malam Buhari na tuki, ya sassauta murya yace "Ayshah! Kin ce bazaki je gida na ki gani ba ko? Koda akwai abinda bai miki ba a canza don shine gidanki da ‘ya’yanmu anan Gombe". Da sauri Siddiqah tace "Don Allah Hamma Abdul a'ah, ba sai naje ba, zan gani next time". Hammah yace "ai shikenan. Kin dade baki je ba.
Wanda ya jure yayi rainon Dan shillansa wajen shekara guda, ai jiran kwana bakwai bazai gagareshi ya fige abinsa ba".
Da haka suka kawo kofar gidan su Siddiqah.
Taimakon da Allah yayima Siddiqah ta fito nan da nan shine Malam Buhari dake cikin motar nan, wanda ya kure radio yana sauraron wata tsohuwar waqa ta Sani Aliyu Dandawo. Da Prince bazai barta hakannan ba sai ya kara cakudata.


Duk da haka cike da damuwa Hammah ya rike hannunta yace.
"Babyyyyy. I will miss you kin sani ko?"
Siddiqah ta dube shi idanunta narai narai tace dashi cikin harshen yarbanci "I will Miss you more Hamma....". Ba zato taji ya kai hannunta ga bakinsa ya sumbata. Da kyar ta samu ta zare hannunta daga cikin nasa ta shige cikin gida ba ko waiwaye. Don gabadaya Hamma ya saka mata wata irin kasala (by just mere looking into his blurred eyes).


Umma da Abba sun sha labarin Nani Oummana, irin kirkinta da karamcinta daga bakin Aisha. Ta fidda kayan da Oummana ta bata har da alkhyabba ta mata da manyan turamen super guda uku da manyan lesika uku. Ga bandir din filtex na Abban Aisha da Baba Barau.
A ranar sai can dare Siddiqa ta bar dakin Ummanta zuwa nata dakin, sun raba dare suna hira don ji suke kamar gobe-gobe ne Petel zata tafi ba kwana shidda masu zuwa ba.
Don Hamma ya tabbatar ma Abban Aisha in sun tafi zasu jima basu waiwayi gida ba, don hutun shekara ya kammala harda kari mai yawa.


Wajejen karfe 12 na dare Siddiqah ta gama komai na shirin kwanciyar ta. Hammah ya kira ta, Siddiqah ta daga hatta muryarta ta canza don barci take ji sosai tace.
"Hammah, baka kwanta ba?" Yace "na kasa barci ne Baby.... Ina missing furar kinnan da kindirmo..." Aisha ta rufe ido tana jin kunya kamar Hamma na kallonta, tana kuma tuna incident din na yau da ya kasa bacewa daga idanunta, feelings din kuma sababbi suka kasa barin ranta. Hamma yace "Baby you know what?" Ta girgiza kai kawai kamar Hamma na kallonta.
Hamma yace "ban taba jin eagerness a rayuwata irinna ranar da zaki dawo min ba. I will be patiently waiting for you and your annoying Jamb.”
Daga ranar da kika dawo ne zamu fara rayuwa. Kinsan rayuwar mu ta Argentina babu komai cikin ta sai introduction na AISHA zuwa cikin lonely and pitiful rayuwar KEHINDE.


I reserved the day for you only, as I reserved myself for 43 years waiting for the day. Please Baby, ki bani dukkan go ahead da juriyar ki da zan bukata, kinji?"


Kunya kamar ta kashe Aisha. Prince ya cigaba da kashe Aisha da kalamai masu dadi yana gaya mata irin tanadin soyayyar da yayi mata daga ranar data dawo, har zuwa karshen rayuwar su.
Ashe dai Ishaq da take ji a ranta akan yana gaya mata kalamai da suke zauna mata a rai bai iya komai ba. Ga inda kalaman fatar baki kadai ke neman narkar da zuciyarta a take. Har hakan ya saka mata (nervousness) akan zuwan ranar tarewarta dinnan da Prince ke ta maimaitawa, ba tareda Prince ya san ya saka mata nervousness din ba.


A daren yau Hammah ya gaya mata maganganu masu matukar nauyi. A ciki ya gaya mata cewa throughout the 43 years of his life he had never had a sex with anyone. Waiting for her…. his dream wife.
As a hopeless romantic, ya jira zuwan true love dinsa tsayin wannan lokacin, and today, he thank the Exalted Lord Almighty for bringing her to his life.
(Duk da Haseenah ta so ta saka Prince ya kauce hanya Kehinde bai taba yin abinda ya wuce kissing na shan minti da ita ba. Wanda a yau, wancan abinda ya dan gitta a tsakaninsu ma regretting dinsa yake yi, yana kara istigfari).
Ya yarda ba wata soyayya ta kwanciyar hankali da sakewa da jin dadi mara misaltuwa kamar ta auren Sunnah.


Da sanyin muryar Prince dake kasheta da dadadan kalamai cikin kunnenta Aisha tayi barci akan wayar, sai ji yayi numfashin ta ya canza a hankali mai nuna tayi barci ta bar shi da wayarsa, batareda ta san lokacin da barcin ya sace ta ba. Shine dai yaga wayar na cigaba da reading kuma bai kara jinta ba. Dole ya kyaleta ya kwanta shima. Amma kam yau Prince yayi wahalallen barci na azaba wanda ko zamanin samartakarsa dana tashen balagarsa baiyi irinsa ba.


Firdaus ta taba gayawa Nenne a cikin gorin da Maman Kiki tayi wa Aisha harda na 'Lefe'. Ashe Nenne bata manta wannan ba abin yana tsaye a ranta.
Don haka tun ranar da suka koma Lagos ta kira Hamma Abdulrasheed suka gaisa.

Nenne tace "Hammansu akan zancen lefen Aisha ne, na maka aure da dukkan hidimarsa amma lefe na al'adar Hausa Fulani na tuna ba’ayi ba na bar maka kayi da kanka. Zaka fi sanin irin dawainiyar dake cikin aure da wahalar sa".
Prince yayi murmushi yace "Nenne kenan, ai da kin fada tuntuni da tuni an yi. Yanzunma bata baci ‘better late than never’. Nawa zan bayar?" Nenne tace "da yawa. Don sawa zanyi a hada komai cikin kwana uku kafin Aisha ta baro Gombe ta dora hannunta akan lefen nan" shi ya san Aisha sarai bata wani damu da abin duniya ba balle wani lefe, kuma ita a wurinta maganganun Taiwo sun dade da wucewa bata kara waiwayarsu, amma yasan Nennensa sarai tunda ta rike shi a ranta to fa sai anyi. Hamma yace,
"to Nenne bakomai, ayi amfani da 'Black Card' dina dana baki ajiya kafin na taho, ba limit a cikinsa. In ce ko shikenan?"
Nenne tayi murmushi bata yi magana ba. Prince ya sake cewa "in ma kin karar da abinda ke ciki Nenne dana iso zan bada ‘dollar card’ dina a karasa, ince ko hakan yayi miki? Ayi lefe lafiya".


Yana sauka a Lagos kuwa gidansu ya zarce. Yace "Nenne yaya an gama lefen?"
Tace "an kusa dai". Har ya fita zai tafi gidansa ya dawo. Ya baima Nenne dollar card dinsa yace "in case wancan ya kare" Nenne na dariya a ranta tace Hammansu da Dade dinsa ‘are real Yoruba Demons’ akan son matansu basu da na biyu.


Nenne da Taiwo suka hada lefe na gani na fada ranar Friday Taiwo ta taho da lefen Gombe.
Sai Nani Oummana tasa wata Aunty dinsu da matar Uncle Abdulmajeed da tazo a lokacin tareda Taiwo suka kawo lefen gidansu Aisha da daddare.


Sai ga Taiwo har dakin Aisha yau, tana cike da 'guilt' mai yawa, Don gani take hatta lefen nan sabida ita aka yi shi. Ta kara jin nadama mai yawa. Sai ta bige da yiwa Aisha hirar Kiki, ta gaya mata Kiki na tafe sati biyu masu zuwa, kuma da tazo za'a saka ranar aurenta da Tosin.
Nenne kuwa taji dadi da akayi hakan, ko ba komai anyi drawing attention dinsu zuwa ga abinda yake cikon al'adar aure ga Hausa/ Fulani.


Taiwo ta sanar da Haj. Zainab sakon Nenne na cewa ita zata wuce Lagos da Aisha idan ta gama jamb dinta ranar asabar, to lahadi sai su tafi.
Haj. Zainab dai basu gaya mata zasu kawo lefe ba, don haka duk a dame take da rashin shirya musu komai bisa al'ada su kuma Nenne sun yi haka ne don kada su tasheta tsaye inji Nenne, duk da haka sai ta aika Sunusi ya kira Baba Furaira ta karbi lefen. Suka bada tukuici na kudi Inji Baba Barau. Aka rabu cike da farinciki da godiya ga juna.
Don haka Umman Aisha ta dukufa da yiwa Aisha gyaran da tuntuni take son yi mata cikin kwana biyun daya rage musu. Tasa an yiwa Aisha halawa da Dilka mai kunshi kuma tazo har guda ta rangada mata irin black and red henna dinnan. A gefe kwararriyar mai kitso tayi nata aikin, kitso yiri-yiri ta yiwa Aisha kamar da allura ta tsaga shi irin na 'yan Maiduguri.
Sai ga Aisha ta fito tas a cikakkiyar amaryarta tana sheki da sparkling. Abubuwa ne da tun wancan lokacin Haj Zainab taso tayi mata bata samu dama ba sai yanzu. Don haka Aisha ba karamin gyaran amarci ta samu ba, ta fito tayi das da ita.
Washegari Asabar Malam Yunus da kansa ya kai Aisha yin Jamb a location din da zata zana, Jamb dinda Aisha ta kallafawa rai yau Allah yayi an zana ta. Tun 7:30 suka fita karfe 8 suka shiga kuma kafin 10 Aisha ta gama. Abbanta ya jirata har ta kammala ya dawo da ita gida.


A daren Aisha suke sallama dasu Umma. Sun raba dare suna hira, Nenne ma ta bugo taji yaya Shirin tahowar tasu ta gaya mata ta gama shiryawa, sallama suke itada Umma. Aunty Taiwo tace sai 11 zasu zo su dauketa su zarce airport.


Hakan kuwa akayi. Malam Buhari da Taiwo a kofar gidan su Siddiqah 11 na safe tayi musu. Aunty Taiwo ta shigo suka gaisa da Umman Aisha, sukayi sallama, Sunusi ya kai kayan Aisha mota, ta rungume Umma, ta sake rungumeta. Har ta fita soro ta dawo ta sake rungume Umma ido fal kwallah. Umma dariya da dauriya duka, tace.
"Petel dina, zanyi kewarki! Allah ya tsare yayi albarka mai yawa".
**** **** ****


Su Aisha sun sauka Lagos da tsakar rana, nan suka tadda tarbar Nenne ta alfarma. Ga abinci (Yoruba traditional food) da fresh juice din kankana da apple Nenne ta shirya musu. Ga yoghurt da ta yiwa Aisha na musamman. Aisha na bude warmers din taga Ewedu ta hau dariyar farin ciki, tasan tayi kewar kalolin abincin Hamma har mafarkinsu take amma ashe Nenne ta fita sanin su take marmarin ci. Nenne kamar tasan me takewa dariyar, tace “shiyasa nayi miki su ai, na san rabonki da Yoruba food tun barinki Lagos”.


Prince ya gama yiwa Aisha duk wani shirin tafiyarta Qatar tuntuni, a yadda ya tsara washegari Litinin zata bar Lagos ta sameshi a Qatar. Amma sai Nenne ta ce ta daga tafiyar Aisha Qatar sai alhamis, saboda zasu tafi Umrah ita da Dade alhamis din, kuma Qatar airways zasu bi. So zasu taho da ita kawai su kawota da kansu, dama last time bataso tafiyar Aisha ita kadai ba babu 'yan rakiya don dai umarnin Emir ne.
Don haka yanzu da kansu zasu taho da ita su kawota sannan su wuce Umrah.
Prince ko kadan bai so hakan ba, amma dai yace "toh Nenne Allah ya kaimu".
Wannan daga zuwan na Aisha daga Monday zuwa alhamis da Nenne tayi ya baiwa Prince damar yin settling sosai, bayan komawarsa Qatar, don ashe aiki ne damqam yake jiransa bai sani ba, wanda zaiyi in ba shi ba. A cikin ayyukan da ya tarar akwai zuwa consultation na aiki kasar Singapore sati mai zuwa. Kuma in yaje sai yayi sati biyar acan. Tafiyar ta kama masa sati daya da dawowar Aisha gidansa, tunda sai upper week.
Har ila yau, daga zuwan nata da Nenne tayi zuwa alhamis sai ya karawa Prince wani irin dokantuwa da zuwan Aisha fiyeda na baya. Don haka ya shiga gyaran gidansa domin taren Siddiqah. Yasa aka fidda duka furniture din gidan tun daga gado har kujeru ya saka sababbi farare sol. In bai manta ba Kiki ta taba gaya masa ya kamata ya sakawa Aisha sababbin furniture, a wancan zuwan nata Argentina. Tace amarya komai sabo ake saka mata.
Ba furniture kadai ba hatta curtains din gidan da rug carpets saida Prince ya canza da samfurin zamani kirar jiya-jiya (latest arrivals).
Kayan cefane kuwa ba abinda bai sa an ajiye mata ba, tun daga kan gishiri har tsinken sakace, kai har da wadanda Aisha bazata bukata bama daga zuwanta, duk Prince yasa yaron gidansa na Qatar wato Zaid ya ajiye mata.
Wato bayeraben miji in ya tashi soyayya da dukkan zuciyarsa yake yin ta musamman mai shekaru da cikar hankali irin na Hamma Prince, don babu rawar kan kuruciya a tareda shi da zuciya daya yake son Aisha yake kuma hidimtawa soyayyar.
Kai lallai shiri ba dan karami ba na hango Kehinde na yiwa Aisha. Sai mu ce amarya Aisha Allah ya kiyaye hanya ya kawo kazantar daki.


Ya shirya mata lafiyayyen dakin barci dab da nasa, bayan master bedroom da zasuyi sharing. Babu abin da babu na bukatar mace ‘yar gayu a dakinnan na Petel Siddiqah.


Wannan gidan da Prince yake ciki is not a Ranch House, gida ne da Qatar Refinery suka bashi don ya zauna yayi musu aiki. Gidan 'penthouse' ne. Ranch House da Polo Horses dinsa duka suna can Argentina.


To dama Qatar wajen da yake aikinsa ne kawai, baya Polo a Qatar sai ya haura kasashen turai ko Argentina yake yin abinsa.
**** **** *****


Nenne ta gama ma Aisha duk wani shiri da ake yiwa amare 'yan kabilar Yoruba wadanda za'a kai gidan miji karo na farko, har ciccibin nagge Nenne ta dafa mata ta cinye ba tareda ta san ko menene ba. Aisha ta sha mamakin ganin Aunty Taiwo bata koma gidanta ba tun saukarsu, ta tare ma a dakin Princess Fatima.
Kuma da alama zaman gida take. Bata tambayi komai ba amma ta gane akwai matsala a auren Aunty Taiwo yanzu, shiyasa ta dawo gida.
Ranar Alhamis kamar yadda suka alqawartama Prince Nenne da Dade da surukarsu Aisha Siddiqah Yunus, suka daga cikin Qatar Airways, daga filin jirgin saman Murtala Mohammed na jihar Lagos.
Tun jiya Dade ya gaya masa lokacin tasowarsu da landing time.

A cikin jirgin, Dade da Nenne suna a first class Q suites na Qatar Airlines (aisle seats), so sun rufe kofar ya zama kamar daki suna hirarsu, Aisha kuwa na jikin window ta kwantar da kanta akan wuyan seat dinta, tayi shiru cikin tunani, tana tuna waccan tafiyar tata ita kadai zuwa Argentina, da abubuwan tarihi da suka faru cikin tafiyar. Har gobe bata san hikimarsu Dade ta tura ta ita kadai da farko ba a wancan lokacin, saidai da yake Nenne ta gaya mata daga baya cewa Allah ya jikan rai Emir ne yayi umarnin hakan.
Ita da kanta daga baya take tunanin watakila hikimar Maimartaba Emir of Ilorin na yin hakan shine basa son tursasashi yayi welcoming dinta, wato ya zamanto ya karbeta karba irin ta ganin idonsu, su tafi ya canza mata zuwa true colour dinsa, sun barshi yayi deciding yadda zai karbeta don radin kansa.
Bata san meyasa ba tafi jin dadi da kwarin gwiwa har ma da karin ‘self-confidence’ na isa ga Hamma yau, da fara sabuwar rayuwar meaningful aure tare da shi, da ya zama cewa su Nenne ne suka kawota da kansu yanzu.


Har sukayi landing a Qatar, Aisha bata jin me suke cewa cikin hirarsu, wadda suke yi da yarbanci, wani lokacin su cakuda da harshen fulatanci, duk dai suna tattaunawa ne akan sha’anin rayuwar ‘ya’yansu da matsalar auren Taiwo. Da alama a irin wannan trip din kadai suke samun lokaci su tattauna extensively akan ‘ya’yansu irin haka.
Ita daga karshe ma barci tayi, bata farka ba saida aka ce cikin bututun magana kowa ya daura belt, jirgi zai sauka a Qatriyyah.

Prince daga office dinsa kusan duk bayan minti biyar sai ya duba agogon swatch din dake hannunsa, tun kafin lokacin saukarsu ya cika ya yanke duk abinda yake yi ya taho filin jirgin daukarsu Nenne. Jirgin su Aishah na sauka shima yana shiga reception na tarbar baki, don haka Prince baiyi zaman dogon

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login