Showing 18001 words to 21000 words out of 41738 words
Chapter 7 - Aishah-Saddiqa book 4 end complete by Takori Kabara .txt
Ba zai manta ba, Nani Oummana ce silar sayen gidan da yayi, a wani zuwa da yayi shekarun baya. Domin ta ce in yana so ya faranta mata dole ya sayi gida wanda iyalinsa za su ke sauka a Gombe, bazata yarda ta barwa Akannis shi bakidayansa ba, dole sai sun raba shi gida biyu an baiwa kowanne bangare hakkinsa, ko don ‘ya’yansa in sun taso su basu nasu muhimmancin na dangin Uwa domin kuwa lokacin da suka bada auren Nenne Sappa ga Akannis, sun ce, ‘ya’yanta dole su zo Arewa.
A wurin Uncle Abdulmajid ya sayi gidan da jimawa, kasancewar likita Abdulmajid din kafin komawarsa Morocco yana taba sana’ar ginin gidaje yana sayarwa tsakanin Gombe da Bauchi.
Duk da haka Malam Buhari bai wuce dashu gidannasa ba, ya wuce da shi kai tsaye fadar Gombe bisa umarninsa, yayiwa maigadin gidan a waya da yaron gidan yace a yi masa gyara yana iya zuwa yau ko gobe. Kai tsaye wajen Oummana ya sauka.
A sassan Uwar gari Hajiya Ummana, Prince ne zaune a gefen damanta, tanata zuba mishi hira cikin fulatanci. Sannan tana kokarin saka mishi abinci da fura, wadda ta ji kindirmo ga kananan kankara an zuba a ciki, amma Prince duk sonsa da fura, wadda yake yiwa shan gani kasheni idan ya zo Gombe, yau ko rabin kofi bai sha ba.
Nani ta ce, “Ai na san da zuwan nata, Nennenka ta gaya min komai. In shaAllahu za’a gyara komai”.
Prince ya ji dadi sosai, iyayensa da kakanninsa ba dai sanin yakamata ba da halin dattaku, duk abin da ya kamata su yi don saya wa ‘ya’yansu mutunci sun sani, bai san inda Taiwo ta debo bakin hali na rashin sanin darajar Dan Adam ba. Shi abin da ke daure masa kai da lamarin Taiwo, ta so Haseenah ma da bata da kowa, bata da nasaba, amma wai duk da haka ta kasa son Aisha. Aishar da saidai a nuna mata gadon mulki da sarauta kawai.
Ya nisa a hankali yana cewa cikin ransa, “Murjanatu baki kyauta min ba. Saida kika ga na samu sabon hope, wanda ya farfado dani daga suma na, na fada a wata korama da zaqinta yafi na zuma, gardinta yafi na madara, wadda ban taba fadawa ba a tsayin rayuwata, sannan ne zaki kore min wannan farin cikin dana nema na rasa (for over a decade), bisa wasu hujjojinki akan Aisha marasa ma’ana marasa makama. Aisha ki yafe mu!”.
Nani Oummana da yake ta san hakikanin matsalar da ta kawo Aisha Gombe. Nenne ta yi mata cikakken bayani a waya. Amma Oummana ta so ta tambayi Nenne me ya sa ta taho ita kadai? Ta tuna ana tsaka da bikinsu Fatima ne.
Ita ma ciwon kafa ne ya hana ta zuwa Ilorin, amma duk haularta da na Uban kasa wato yayan Nenne Sarki Ahmadu Jalloh ‘ya’ya da jikoki sun tafi suna can don yiwa Nenne kara. Da su aka yi komai, don haka Prince Malam Buhari ya sa a gaba ya yi masa jagora zuwa Jeka da fari.
Zuwan Prince na farko kenan gidan iyayen Aisha tun auren su.
Yana daga cikin mota mai duhun gilassai (tinted) yana nazarin gidan su Aisha da Malam Buhari ya yi parking a kofar gidan. Gidan karami ne, ko kuwa madaidaici, ya sha farin fenti mai santsi, sannan harabar gidan a share take tas. Soron gidan tsaf-tsaf da shi, tsafta ta zauna masa, ba dai gida ne na talakkawa can ba, don ko a layin gidansu Aisha ya fi kowanne fita da haske, kuma fentin da aka yi bai shekara ba, lokacin aurenta aka yi shi watanni tara kenan.
Buhari ya bude masa kofa ya fito, Prince yana sanye da yadin filtex sky blue, ya lankwasa hularsu ta yarbawa a kansa.
A fuskarsa yau ya dora farin glass, wanda ya dora a saman dogon hancinsa, Kamshin turarensa na ‘Baccarat’ tun daga soron farko sai da ya kai tsakar gidansuAisha. Malam Buhari ne ya zagaya ya bude masa kofa ya fito ya yi ta rafka sallama don bai ga yaron da zai aika ba. Wani matashin yaro ne ya fito daga gidan, wato Sunusi yaron da ke ma Umma aike. Buhari ya ce masa, “Ko Malam na gida?”
Sunusi ya ce, “Eh Malam na nan”. Yace “to don Allah ka gaya masa Abdulrasheed ne yazo daga Lagos”, Sunusi yace “toh, bari in gaya masa”.
Sunusi ya gayawa Malam Yunus zuwan bakon nasa. Malam Yunus ya dubi Umma itama ta dubeshi sai yace Sunusi ya shigo dashi.
Prince ya shigo ya tsugunna ya fara gaishesu, Umma da Malam Yunus suka karbi Prince hannu bibbiyu, fuskarsu ba yabo ba fallasa, Malam ya tambayeshi ya hanya da gajiyar biki da yadda ya baro su Nenne. Malam Yunus na cewa a ransa Prince baiwa Aisha laifin komai ba kuma ba shi ya zageta ba. ya gaya masa Aisha tana gidan Yaya Barau don shine waliyyinta daman, yace babu komai amman dai ka je ka samu Baba Barau magana tana hannunsa. In don ta ni ne ma Abdulrasheed nasan har yanzu akwai kuruciya a tare da Taiwo mace duk shekarunta ai baka rabata da halin yara. Kuma iyayenka su sun san su waye mu, ba don haka ba da bazasu matsa wajen nema maka auren Aisha ba.
Amman dai ina baka shawarar kaje ka samu Yaya Barau. Zan sa a raka ka yanzu”.
Prince yaji dadi sosai ya kara yabawa da dattakun iyayen Aisha. Ya sunkuya yana kara baiwa Ummanta hakuri, Umma tace “aibabu komai, banda rigimar Aisha ma in nice bazan kula ba”. nan Abdulrasheed yace “a’ah Umma, gara da tayiwa Taiwo haka, ni kaina bansan yaushe Taiwo ta zama mai wannan baudadden halin ba sai yanzu, kuma wallahi na mata iyaka da iyali na, koda wasa abinda ya faru bazai kara faruwa ba in sha Allah. Iyaye ai na kowa ne, wannan ba tarbiyyar da aka bamu bane, don Allah kuma ina kara bada hakuri”.
Malam Yunus yaji dadi sosai a ransa, ya tabbatar ya kuma kara yarda bai aurawa Aisha mijin banza ba tunda gashinan hakikanin gaskiyarsa yake basu hakuri, yake kuma Allah wadai da halin ‘yar uwarsa wanda shi kansa Malam Yunusya san tabbas wulakanci ba halinsu bane. Amma still he is so proud da Aisha ta nuna musu iyayenta ba abin wasa bane don haka bazata dau wulakanci ba.
Sannan kuma ya ga girma da soyayyar Aishaa idon YarimaAbdulrasheed wanda yasa ya kara jin dadi, amma duk da haka yace bazai shiga maganarsu da Baba Barau ba. gara yaje Baba Barau ya kara wana shi amma zancen kashe aure yanzu babu shi in sha Allahu.
Baban Aisha nan take yace da Sunusi ya raka su gidan Baba Barau din. Sunusi ya saka takalmansa ya shiga gaban mota, Prince na owner’s side, Malam Buhari yaja motar suka tafi, don gidan Baba Barau ba nisa sosai, layi biyu ne tsakaninsa da dan uwansa.
A zaure suka tadda Baba Barau yana cin abinci, ga fura mai sanyi a gefe an ajiye masa a kwanon silba a gefe. A nutse Prince ya yi sallama a zauren. Baba Barau ya amsa duk da bai taba ganinsa ba, don haka da fara’a sosai Baba Barau yake wa hamshakin bakon nasa da bai san ko waye ba barka da zuwa, ya ce.
“Zo nan bisa buzuna ka zauna”.
Prince har da cire hula bayan ya cire takalmansa ya ki hawa buzun ya zauna a kan kafafunsa tankwashe a gabansa. Ya fara gaishe shi da hausarshi da ba ta da kwari.
Baba Barau ya ce, “Ban gane dan nawa ba, daga ina kenan?”
Nan Prince ya gabatar masa da kansa da cewa shine Abdulrasheed daga Lagos. Baba Barau ya kara neman karin haske, don har lokacin bai gane ba, Prince ya kasa magana sai da kyar ya iya cewa “Mijin Aisha-Siddiqah”. Ai nan da nan Baba Barau ya hadiye duk wani annuri da ke fuskarsa, Prince ya kara gaishe shi a ladabce, ya bashi hakuri akan zuwan Aisha. don yana da labarin Baba Barau a bakin Aisha, wani Yayan babanta da ba ya daukar wargi kuma ba ya yarda ko Babanta ya bata mata rai. Yadda Baba Barau ya maida walwalar fuskarsa ne ya sa Prince jin wata irin shakkarsa. Amma hakan bai hana shi fadan abin da ke gabansa ba, ya fara da bada hakuri sannan ya ce masa wallahil azeem shi Aysha tafi karfin wulakanci a garesa. Dalilin ma da ya bari sai yau ya taho kada cece-kuce yayi yawa ne cikin taron bikin. Ya kuma tabbatarwa Baba Barau ya magance matsalar Taiwo. Kuma yayi alkawarin baza’a kara ba. a wannnan gabar Baba Barau kansa ya yaba da hankalin Prince. Ya ce “naji, amma dai a hakura kawai da aurennan, kaima daman ba so kake ba itama haka, to kuma kaga akwai mutunci tsakanin iyayenku mata kada auren nan ya zama silar matsalarsa”.
Murya na rawa Prince yace “Baba ni ia son Aisha…” Baba Barau ya dakatar dashi yace “Abduulrasheed maganar gaskiya yaranmu basa auren wulakanci, munada hakuri amman banda wulakanci, kuma abinda yasa Aisha dawowa gida haka to babba ne, inda duk za’a taba maka iyaye bazakaso zama ba. so ina bayan Aisha kan duk abinda ta yanke, kaje zan neme ka zanyi shawara”.
Jiki a sanyaye Abdulrashid yace “toh Baba, nagode, zan iya ganinAisha yanzu?” Baba Barau yace “a’ah”. Sai yayi shiru na dan lokaci cikin damuwa daga bisani yace “to shikenan Baba zan tafi nagode”.
Suka koma gida, ya kwashe komai na yadda sukayi da Baba Barau ya gayawa Nani Oummana.
Da kyar Nani ta rarrashe shi ya dan ci abinci ya yi mata sallama ya wuce gidansa.
Nani sai ta dau waya ta kira Nenne suka gaisa, Nani ta yi mata ban gajiyar biki da ta hidima, Nenne ta ce, ai har sun dawo Legos, ta kansile da yawan events din bikin da ba su zama dole ba saboda Taiwo data bata ciwon kai. Tana son kashe auren Hammansu babu gaira babu dalili.
Nani ta ce, “Amma Dadensu ya kyauta min da ya wanke ja’ira mai halinsu na yarbawa, mu dai kam Murja ba ta dauko mu ba, can musu cikin Akannin”.
Nenne ta ce, “Ai ko a Akanni babu irin Taiwo. Ita kadai ce da halinta, mijinta ma hakuri yake da nature dinta ba tun yau ba. Tun yana kawo kararta ana sulhu har ya gaji ya yi nesa da ita, sai ya yi watanni uku bai waiwayo ta ba”.
Nani ta ce, “Addu’a za ku dinga yi mata da nasiha ba fushi da ita ba. A shekarunta dai ta yi girman banza”.
Sun dade suna tattaunawa a kan sha’anin Taiwo, har Nenne ta ce, “Ban da abin Murja ma Aisha ba ta ki Hammansu ba saboda ratar shekarun da ke a tsakaninsu sai shi ne zai ki Aisha?
Aisha son kowa kin wanda bai samu ba, na bi sarauta da kudi da gudu, na kama wa Hamma Aisha ne saboda nagarta da iyaye na gari, idan kuwa har Aisha ta fada wa iyayenta abin da Murja ta yi mata, to abu ya baci. Don ba kowa zai yarda a taba mutuncinsa a wanye lafiya ba, shi ya sa daga ni har Dade muka ce babu mu a 'yan biko wai ido da kunya. Shi da ya bar Murja ta ke taka rawa cikin rayuwarsa sai ya nemo ta ta yi masa biko”.
Nani kuma ta ce, “Hamma meye laifinsa? Ana hora shi ne kawai da laifin da ba nashi ba. Ya je bikon ai ga shi ya dawo ba nasara, ya yi min shame-shame a falo kamar gawa. Duk sonsa da fura tunda ya zo bai sha ba”.
Nenne ta ce, mu kyale shi ya yi ta bikonsa shi kadai, ya fi sanin darajar wahalar da aka yi masa aka yi masa aurenta babu ko kobonsa”.
Nani kuma ta ce, “A’a za ta sa uban kasa ya shiga maganar, idan Abdulrasheed ya kasa.
Kwanan sa biyu a Gombe. Rana ta farko da yaje ga yadda suka kwashe da Baba Barau, don haka ya sake kwana a Gombe. Washegari ya sake komawa wajen Baban Aisha da Umman ta, ya gaya musu yadda sukayi shi da Baba Barau, ya Kuma roki Abban Aisha don Allah ya taya shi baiwa Baba Barau haquri.
Malam Yunus ya lallashe shi ya ce ya koma gida zai ma Yayansa magana, dan har ga Allah yaji tausayin sa.
Prince ya saki jiki da iyayen Aisha kamar ba jiya ya fara zuwa ba. Sukayi developing good bond. He is open minded, ga kuma hankali. Amman kana ganin sa kaga damuwa.
Abban Aisha yace masa kar ya damu yaje gida zai saka baki. Kuma kada yaje gidan baba Barau yau tunda jiya ya je, zai neme shi da kansa, yace yayi haq9uri har ya neme shi din.
Prince ba yadda ya iya haka ya dawo Lagos bai san makomar aurensa ba.
A daren ranar yana tareda iyayen sa a falon gidansu. Dade ya tambaye shi "toh ya akayi a gomben?" Nan Prince ya fada masa komai, yace murya ba kuzari "nidai Dade ba don Taiwo yar uwata bace da na mata Allah ya isa, finally i have a glimpse of happiness, ta lalata min shi, wannan wani irin rashin sa’a ne?" Prince ya fadawa Babansa in a heartbreaking manner.
Yasa hannu ya dafe kan sa. Sai ya ba Dade tausayi matuka. Suna haka aka kira shi daga Qatar, Dade yana jin sa yace musu bashi da lafiya su qara mashi 2 weeks.
Sai bayan ya aje wayar ne Dade yace masa "toh ka koma mana sai ka dawo daga baya? By then itama ta huce Aysha din".