Showing 3001 words to 6000 words out of 41738 words

Chapter 2 - Aishah-Saddiqa book 4 end complete by Takori Kabara .txt

24 Nov 2024

2289

girki na”. Sai kawai ya janyota ta fado cinyarsa duk ta daburce tana kokarin tashi kawai sai taji yayi hugging dinta ta baya gabadaya.
“Don Allah Uncle ka sake ni….” yai shiru, jin baida niyya itama ta share tayi shiru, baka jin komai sai bugun zuciyoyinsu. Can kuma Hamma yace (in a cool tone).
“Yes, Haseenah was my girlfriend, naso aurenta, amma (she did something bad) da ya raba mu. The worst thing da kika sani za’a yiwa masoyin gaskiya.
Kuma a kanta ne na rufe babin mata a rayuwata, wanda hakan yasa I feel Kaman duka daya suke, dalilin ma kenan da yasa ban kuma neman wata ba, kuma ko an bani cikin ‘ya’yan ‘yan uwana a family sai ince banaso….
Toh Aisha har saida Nenne ta nemomin aurenki da kanta, aka yi ban sani ba, don ta san inna sani bazan yarda ba, amma tun ranar dana je asibiti duba Nenne, na ganki, na yaba dake a raina Aisha, har na gayawa Nenne, nace wacece wannan yarinyar mai hankali haka….
Kinga dai kudin goro na yiwa mata, but you stood out, I was impressed with you”.
Long story short, tun a lokacinma da bansan ke matata bace, naji kin burgeni da attributes dinki, kuma zama dake da nayi na dan lokaci na sake ganin me Nenne ta ganin min.
Aisha naga meyasa iyayena suka nemo min aurenki suka aura min. Kamar yadda kikace addu’ar Nenne a filin Arfah ce ta fado a kanki wannan haka ne. don haka ke zabin Allah ce a gare ni.
You are a light in my life and I am telling you you are shining so bright. Kinga duk ciwon dana ji na rashin Haseenah? To yanzu godiya nakewa Allah da nayi wannan rashin nata, don I wouldn’t have met you…
So don Allah ki cire maganar Haseenah a kanki, babu abun fushi a wurin, You my Dear kin zama ‘ife mi, orun mi, iyawo mi’ kinji Aisha?”
Sai ta daga kai. A zuciyarta wani sanyi na zuba, ashe haka ake ji in mijinka ya fifita ka kan kowa? That’s the Yoruba husband in action. Sai taji haushinnan yanata tsiyayewa… yana bin rariya, ta gyara zata tashi ya kara riketa, yace,
“kin fahimceni yanzu?” Tace “yes Uncle” yace “Uncle ya dawo dai? Don Allah ya koma.
Ni ina murna kina ce min Hamma, daga nan in zama honey, watarana in dawo Sweetie, shine kuma za’a koma Uncle dinnan, haba babyn Nenne da Dade”.
Sai kawai Aisha ta saki murmushi.
Tace “naji Ya Hamma” yace “ko kefa?” Sai tace “me kace dazu da yarbanci?”
Sai yace “ashe kina ji? To ki koya ki fassara mana”.
Aisha tayi dariya, sai lokacin Hamma yaji sanyi a zuciyarshi har da ajiyar zuciya.
Bakinsa daidai saitin kunnenta yace “Babyn Nenne da Dade kuma Babyn Hamma ko?” Prince ya fada yana jin wani cool feelings for her, sai ta tashi da karfi zata wuce kitchen don kunya sosai ta lullubeta, tana ‘yar dariya.
Hamma yayi maza ya dawo da ita jikinsa. Yaji dadin yadda yana mata bayani ta sauka, kuma da gani har ranta abin ya wuce. She’s a very understanding person.
Sai Prince ya sake rungumeta sosai ta bayanta, yayinda take zaune a kan cinyar sa. Itama Siddiqah sai tayi mukus…. Hamma ya kwantar da kansa bisa masangalin wuyanta… yana sunsunar kasan wuyanta, duk sunyi shiruuuu na wani lokaci, kamar ruwa ya cinyesu. Bugun zuciyoyinsu kawai kake ji wadanda ke bugawa a lokaci guda.
Murya a sanyaye Aisha tace "Hamma, thank you for the explanation, nasan ba dole bane kayi min bayaninnan, amman naji dadi da kayi min din, domin ya wanke min zuciya.
In sha Allahu kuma nima bazan qara fushi ba kan maganar nan".
Prince yayi murmushi, voice dinta yana caressing din sa, gabadaya wata kasala ce ma ta sauko masa, yana ta kokarin dannewa.
Ya dai kasa magana yai shiru, ya rufe ido, listening to her soft sound, tana masa wannan maganar cikin lumana da gamsuwa da abinda yace mata, and the softness of her skin dake kwance a jikinsa yana kara tasiri a tare dashi.
Sai Hamma ya samu kansa da dan murza hannunta …. jin shirunsa yayi yawa bai amsa ta ba, sai Aisha ta juyo kadan haka ta dubeshi. Sai ta ga Hamma da ido a lumshe, kamar mai jin barci.
A tsanake tayi kokarin tashi daga cinyarsa, ya kuwa rike ta gam, ya dan bude idon yace "ina zaki?" Aisha tace "abincin zan qarasa" yace "kashe gass din, we will eat out today, just stay here…".
Aisha tayi shiru, ta koma jikin Prince ta kwanta tayi lamoo! Yace "please Aisha..... muje outing din?" Tace "toh ai bacci kake ji naga", Hamma yace "bacci? Did i say so?" Ta ce.
"To ai Hamma idonka rufe yake fa tun dazu, ina ta maka magana bakaji ba, gashi ma muryar bacci kake yimin".
Prince bai san sanda wani kasaitaccen murmushi ya kufce masa ba, he so much loves her naivety. And she is observant, but totally ignorant ga halin da yake ciki.
Yes, yanayin sa gaba daya ya canza, wata muguwar sha’awa ce ta saukar mashi. It seems with every word she says kara yayyafa ma wutarsa petrol take, amman babyn Nennen bata gane ba. Wannan childishness dinnata yana kara burge shi.
Hamma yace "Ayshaaaaa…" tace "na'am Hamma" yace "ba bacci nake ba, I am just in a mood!" Ya fada yana mata wata kallo, mai shiga rai da sanya kasala.
Har sai da Aisha ta tsargu don ya kara jawo ta jikin sa sosai, this time around juyo da ita yayi tana facing dinsa gabagadi. Aisha tayi shiru, yace "baza ki tambayeni what mood ba?" Tace "toh Hamma bacci kake ji, kuma ka kafe kai baka ji" ta dan turo bakin ta gaba, tana fada cikin shagwaba 'yar gaske.
Ai kuwa Prince ya sa ido yana kallon bakin da take turowa so soft and luscious, bai san sanda yace "I really really want to kiss you saddiqa… "ya matso dab da fuskar ta, har suna jin numfashin juna, ya kalle ta, cikin idonsa kadai ta ga tsantsar al'amuran dake cin zuciyarsa da gangar jikinsa. An yi sa’a itama ta juyo kenan sai kawai Hamma ya hade bakinsu wurin guda ya soma kissing Aisha-Siddiqah in a serious tone and passionate manner.
Da kyar Aisha ta samu ta zame daga Hammah, ta mike jikinta yana rawa a daburce tayi hanyar kitchenette. Hamma da kyar ya iya mikewa yanakokarinsaita kansa. Yabi bayanta yana cewa cikin basarwa,
“you know what? Jeki shirya kawai ki bar girkinnan, we are going out, ma ci a waje”.
Tace “toh”, sai ga Nenne ta sake kira.
Tace “ni Hammansu dazu maganar bikinsu Princesses na kira zan maka na manta, an saka rana, kwanaki goma masu zuwa. Don Allah ka taho da Aisha, kuma kuzo da wuri. Asabar ne daurin aure wato ranar addu’ar arba’in din Sarki”.
Prince ya ce “toh Nenne, in sha Allah”.
Itama Aisha sai murna lokacin da Hamma ya gaya mata zasu tafi gida Lagos sati mai zuwa, tace “bikinsu Firdausi za’a yi?”
Yace “eh, za’a hada da addu’ar arba’in na Emir. Shine babban burinsa kafin rasuwarsa wato auren twins din gidanmu”.
Siddiqah tayi ta murna har ‘yar rawa ta shiga takawa a wajen, ta manta shaf a gabansa take, irin murnar zata gida dinnan, after a long while.
Hutun Prince ya dade da karewa, zuwan Siddiqah ne yasa ya kai har wannan lokacin a Argentina.
Sun fita a daren sun shakata, suka ci abincin dare a wani Arabian Cuisine sannan suka dawo gida.
Aisha ta nufi dakinta tayi wanka ta sha rigar barci mai dan kauri purple ta fesa turarukanta masu dadin kamshi ta nufi dakin Prince.
Nan ta tadda shi daga shi sai short nicker akan sofa yana shan ‘chamomile tea’ kafin ya kwanta. Ta na shiga Hamma ya dago yana dubanta da wani kallo da bai taba yi mata ba, domin sha'awar matarsa ce zallah yau cikin idanunsa da duk abinda yake yi. Aisha ta juya da sauri zata koma ganin ba suttura a jikin Hamma sai gajeren wando, ga kunya data kamata sai ya aje kofin hannunsa, yace Aisha wait, ya taso ya isa gareta ya kamo hannunta ya shigo da ita cikin dakin yana cewa.
"Ya kinzo turakar miji neman albarka kuma zaki koma?"
Aisha duk ta daburce ta rikice tarude, sabida yanayin da Hamma ke mata magana yau ya sha banban dana koyaushe. Ba don ta kasance mai karfin ji bama, da bazata ji shi ba.
"Dama-dama... zuwa nayi ince maka Hamma saida safe".
Hamma ya dora hannuwansa biyu bisa kafadun Aisha hagu da dama yana murzawa. Ya dan mutstsuka jijiyar wuyanta cikin wani salo na tasowar muguwar sha'awar da baisan akwai a tareda shi ba, saida Aisha ta runtse ido sabida tasowar tata sha'awar ta diya mace, kafin hannunsa ya kai kansa saman kirjinta.
Yace "saida safe dinma ai irin haka ake fadarsa Ayshahhh, ba da fatar baki ba. You my dear I want to kiss you again today!".
Hamma ya fada admiringly idanunsa akan siraran lips din Aisha, yana musu wani inviting looks. Aisha ta kusa narkewa bakidayanta domin a lokacin Hamma ya matsota sosai ne a jikinsa, ya isa cikin nutsuwa ya hade bakinsu wurin guda ya soma sumbatar Aisha a tsanake, sannan ya koma kissing hungrily.
Ashe namiji duk dadewar sa babu aure, ba sai an koya masa sumba ta auratayya ba? Ko da kuwa ya fidda rai da ita, ko bashi da sha'awar ta, sanda zata sameshi zai ji tane tana sarrafashi.
To hakan ce ta faru da Prince Abdulrasheed yau. Da ya samu kissable lips din Aisha yau ya dinga tsotso tamkar Allah ya aikoshi, saida ya ajiye kishirwar shekaru masu yawa na kuruciya dana shiga girma.
Aisha kyale Prince tayi ya yi yadda duk yake so yau, ya jagwalgwala ta iya son ransa a duk ta inda yake so. Ya tsotse duk abinda yake so. Kuma shi da kansa yayiwa kansa limit. Don yana ganin in ya kauda budurcinta any moment zata iya conceiving, shikuma yana ganin kamar bata yi kwarin da zata haihu ba. Tunda har ya samu wannan access din zai iya karawa Aisha lokaci.
A kwanaki goma da suka biyo bayan wannan ranar, wata wawuyar shakuwa ce ta shiga tsakanin Hamma da Aisha. Suna kwana a gado guda, Hamma saida ya san yadda yayi ya fara raba Aisha da dukkan sittirun jikinta in zasu kwanta, yana rabar Aisha da dabara da wayau da simple hugs, da light kiss masu sawa ta saki jiki da shi, su yi barci manne da juna. Tun Aisha matukar jin nauyi da tsoro har ta soma sakewa da Hamma sosai. Don ta lura ba shi da nufin abinda take tsoro. Kusan sati biyu kenan irin rayuwar da suke yi a cikin gidan kenan, full of understanding, intimacy and love, Hamma ya zama baya iya barci bai raba jikinsa dana Aisha ba, bai sumbaci bakinta da kirjinta yadda yake so ba amma bai taba wuce hakan ba yake takawa kansa birki, don a ganinsa har lokacin Aisha bata yi girman data isa ya dora mata hidimar dake cikin aure yanzu ba kada tazo haihuwa ta samu matsala.
Amma me? A na I gobe zasu tafi Lagos komai kwace masa yayi, ya kasa controlling kansa yadda ya saba duk kuwa da yana tausayawa Aisha, da kyar da roko da magiya harda kuka Aisha ta kwaci kanta a hannun Prince domin kuwa gani take duk ranar da hakan ta faru ba wata wata mutuwa zatayi, in tayi la'akari da irin yanayin da Prince ke shiga a irin wadannan lokutan akanta.
A satin dasu Prince zasu dawo Lagos Dade yasa aka je aka shirya gidan Prince na Banana Island, wanda ke daura da gidan mahaifinsa, Prince ya jima da sayen gidan bai taba amfani dashi ba, tun kafin saukarsu Dade ya gayawa Nenne in sun zo a gidansu zasu sauka. Yasa aka gyara gidan aka shigar komai da zasu bukata.
Tun saura kwana uku daurin aure suka sauka a Lagos. Gidan ya debi murnar zuwan su ba babba ba yaro, kowa murnar zuwan Hamma yake yi, ga ‘yan biki sun soma isowa daga sauran jihohi. Kiki ce kawai bata samu zuwa bikin Aunties dinta Princesses ba, don tana shirin rubuta jarrabawarta ta karshe a Informatics a lokacin.
Aunty Murjanatu Taiwo tana Ilorin, sai bayan addu’a zata taho Lagos tare dasu Nenne in sun je. Dade yace su Hamma su fara sauka a Lagos su huta kwana biyu, in yaso sai su dunguma duk gidan zuwa Ilorin su samu adddu’ar Sarki ranar asabar, wadda ta kasance kuma ranar daurin auren su Fatima.
Nenne ta rasa ina taka saka ina taka aje da surukarta Aisha, wata sabuwar kauna da soyayya Nenne take yiwa Siddiqah musamman data gane suna zaman lafiya itada Hamma, Aisha ta samo kansa shima ya samo nutsuwarta, Nenne bata taba jin Hamma cikin farin ciki da nishadin data ji shi ciki ranar da suka yi waya itada su, tana tsammanin Siddiqah ciki gareta ba. don haka tun kafin saukarsu a Lagos yau Nenne da kanta ta shiga kitchen ta shirya abincin tarbar Hamma da Aisha, ta hada dana Dade, girki tayi masa na musamman data tabbatar Hamma ya dade bai samu irinsa ba, wato (Locust Beans Stew) da suke kira Dindin da (Ofada Rice).
Bayan saukarsu da kadan Dade yace ma Prince a gidansu zasu tare, yasa an shirya musu komai da zasu bukata. Don haka ana gama cin abincin dare Dade yace Firdausi ta dauko keys din gidan ta baiwa Hamma, ta yiwa Aisha rakiya kuma.
Anan Nenne tace “a’ah Dade, ita kam Aisha ta zauna ta huta anan, a bari sai bayan biki sannan ayi tarewar. Ta jima bata nan akwai bukatar ta huta tukunna”. Ai kuwa nan da nan Prince ya canza fuska. Domin a yau kam yayi niyyar angwancewa da amaryarsa Siddiqah babu daga kafa. In yaso idan ciki ya samu ya tayata nakudar. Yanzu kuma Nenne tana wani zance wanda zuciyarsa ta gaza dauka, wai Aisha ta zauna da ita har bayan biki, duk kokarinsa na rainon da yayi tayi wata da watanni ba’a gani ba, sai rana daya da ya saka ran hutawa.
Har dai rashin jin dadin hakan ya gaza boyuwa a fuskarsa, ‘yar damuwa ta nuna a fuskar Prince, amma dai bai yi magana ba. saidai tuni Dade da yake shi namiji ne ya ramfo shi.
Lura da yanayinsa da Dade yayi, sai yace.
“Kehinde kodai kafi so ku tafi tare yanzu ne?” Zuruf! Aisha tayi tace “Dade ayi hakuri don Allah ni nan zan zauna gun Nenne har a gama biki, nayi kewar Nenne for long”.
Taki dago ido balle Prince ya kalli kwayar idanunta. Domin ta riga ta san Prince ya gama kaiwa kul a a dalcinsa. Daren tahowarsu da yaya ta tsira? Balle yanzu a gidansa na gado? Takaicin abinda Ausha tace yasa shima ya hadiye, yace “a’ah Dade, ba wata matsala a kyaleta ta sha zamanta”.
Amma Kai da ji kasan shagube ne yayi. Ya ajje spoon ba don ya koshi ba, sai don bazai iya cigaba da ci ba’a gane ransa ya baci ba, da abinda Aisha tayi masa a gaban kowa ta nuna bata damu dashi ba, ya mike yace zai je gidansa ya huta. Bai sake kallon inda Aisha take ba ya nufi hanyar fita falon.
Anan ne Nenne ta dubi Aisha tace “raka shi zuwa mota mana Aisha” Hamma, wanda a lokacin har ya kai bakin kofa cikin matukar kulewa zai fice, yace.
“A’ah Nenne na yafe, ta zauna kawai, na gode”.
Wannan gwasalen da Hamma yayiwa rakiyar Aisha, duk ya faru akan idon amare Princess Fatima da Princess Firdausi, don tare aka zauna cin abincin har dasu gabadaya.
Abin yayi matukar yiwa Fatima dadi, na yadda Prince ya nuna bai damu da Aisha a gaban kowa ba. ita bata fahimci haushi yaji don Aisha tace da bakinta bazata bishi ba. Har ta samu abin adarwa a gaba.
Fatima na komawa dakinta ta kira Aunty Taiwo, tana mayar mata da yadda aka yi, da irin gwasale tayin binsa gidansa da Prince yayi ga Nenne da Aisha, sai Taiwo tace da Fatima, “ewo, to dama nifa na san Kehinde sarai, nafi kowa saninsa, saninda ko Nenne bata yi masa ba, ba son zama da yarinyar nan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login