Showing 42001 words to 45000 words out of 74305 words
Chapter 15 - MUJARRABI BOOK ONE BY SAYYADA BARRISTER.txt
to your mind and wake up from your deeply sleeping, a tunani na za kiyi musu nasiha amma shine ki ke so ki jefa rayuwar ki dumu² a ciki never, that'll never ever happen"
Dariya Zee ta yi ta kalli hauwa'u Jibrin suka tafa suna farin cikin samun nasa tabbas sun kusa mallakar makuɗan kuɗaɗe, Hamrah zata zame musu mukullin arzikin su.
Murmushi Hamrah tayi ta dubi a gogon dake ɗaure a hannunta ta kalli Hauwa'u Jibrin tare da cewa
Da kaina zan nemeku yanzu zan tashi na wuce ciki na shirya zan wuce wajen aiki ina da night duty.
"To pretty mungode da bamu haɗin kai sai mun jiki Please kada ki ɗauki lokaci mai tsawo wajen yin tunani"
Cewar Hauwa'u cikin farin ciki, murmushi Hamrah tayi ta ce
I promise you za ki jini nan da kwanaki.
Cikin farin ciki suka tafi, Shatu cikin ɓacin rai ta ce
"Bestie me ki ke nufi da hakan?"
Murmushi Hamrah tayi ta ce
I want to help.
"Which kind of helping is that, kina so dai ki sanya rayuwar ki cikin hatsari wajen taimakon wasu Please let them do whatever they want and ke ma ki yi rayuwar ki"
Shatu yin hakan da ake yi ne yake sanya bamu taimakawa, taimako yayi ƙaranta kuma hakan shine ke jefa yawancin mutane cikin wani hali. I'll do my best naga na ceto wasu daga cikin matan.
"May Allah be with you bestie, amma gaskiya ina tsoro.
Allah ya taimake mu dai dan tare zamu gudanar.
Tare suka shige ciki Hamrah ta shirya suka fito ta wuce wajen aikinta. Bayan ta idar da sallah ishai ne tana zaune kan dardumar sallah tana addu'a taji wayarta na ringing ta shafa addu'ar ta ɗauka sbd ganin Zeenat ke kira sai dai kuma da tayi sallama sai taji muryan mijin Zeenat yayi magana cikin sauri
"Dr Hamrah kina cikin Hospital ne?"
Ta amsa masa cikin sauri da
Eh, lafiya?.
"Zeenat ce jikin babu daɗi maybe haihuwa ce"
Ok to sai kun iso.
Ya katse wayar ta mike ta sanya white coat nata ta fito ta wuce labour room ta sa a shirya bed ɗin kafin su iso suna ko isowa aka shigar da ita baifi 30 minutes ba ta haihuwa cikin murna da farin ciki Hamrah ta shirya baby boy ɗin ta kwantar dashi babu jimawa yayi bacci. Zeenat jiki da sauki ta tashi ta zauna kamar ba itace wacce ta haihu ba, Hamrah na ta tsokanarta har Aunty maimuna ta shigo suka gaisa Hamrah na mamakin waya sanar da ita nan ta ke faɗa mata mijin Zeenat ne, babu jimawa Ammie ma ta iso nan Ayshe ma ta iso sai kusan 10:00pm suka koma gida amma Aunty maimuna yayar Zeenat wacce suka fito ciki ɗaya sune suke kanta har gari ya waye. Gari na wayewa Zeenat ta ce a bata sallama tunda bata jin komai da ƙyar Hamrah ta bata sallama suka wuce gidanta, nan ko baƙi suka dinga zuwa wunin ranar Hamrah a nan ta wuni sannan ta wuce hospital ta kwana. Sai da ta jera kwana biyu tana sintiri sakanin gidan Zeenat da kuma hospital da gidansu duk sai ta gaji.
_Bayan kwanaki biyu_
Tana kwance a ɗakinta kasancewar bata da aikin safe shiyasa ta kwanta tana hutawa, sai da tasha bacci sannan ta miƙe ta watsa ruwa ta shige kitchen ta haɗa breakfast mai sauki ta fito tana ci kuma tana chatting sai ga kiran Ammar ya shigo ta voice call ta ɗauka cikin sanyin muryar ya ce
"Nayi fushi tunda an daina kulani"
Murmushi tayi ta ce
Ammar iyayen rigima ina ni ina kiranka ai sai a zuƙemin kuɗina, da fatan kana lafiya?.
"Au ta kuɗinki kike bata ni ba shikenan na gode"
Uhm da wasa nake Ammar aikine ya sani gaba ga kuma Zeenat ta haihu shiyasa ka jini shiru.
"Masha Allah, ta sauka lafiya?"
Alhamdulillah, lafiya kalau, ta sami baby boy.
"Wow kice soja ta haihu to saura taki sanya min takwara tun haihuwar ta na fari ta ke min alkawari"
Kama cire rai ba zaka samu ba.
Nan ko yayi tayi mata fira daga bisani sukai sallama ta sauka a online ta miƙe ta maida plate ɗin kitchen ta dawo taji wayarta na ringing ta ɗauka cikin sanyin murya tayi sallama ya amsa tare da cewa
"Ina kofar gidanku ki fito"
Ok to Alhaji Sama'ila amma kashigo cikin gida.
"To"
Ta miƙe ta yafa gyalle ta fito ta taddashi zaune ya sakar mata da murmushi ganin yadda tayi kyau cikin shigar da tayi ta doguwar riga ta atamfa cikin sanyin murya ta ce
Sannu da zuwa.
"Yauwa likita, na kula yanzu ba a yina"
A'a ba haka bane aikin ne.
"To ai ko kirata a waya za ki iya yi ai mu gaisa"
To na amshi laifina zan gyara.
Murmushi yayi tare da cewa
"Ai bakya laifi, nazo ne na sanar dake next week on Friday zan turo magabatana suzo su saida ranar biki, naga gwanda ayi a wuce wajen kawai kada ina ji ina gani a kwace min ke"
Murmushi tayi ta ce
Allah ya nuna mana.
Ameen.
Sun jima suna fira sannan ya miƙe yace zai wuce nan ya ajiye mata envolope cike da kuɗi ta ce bazata ansa ba amma ya dage sai ta ƙarɓa haka ta karba sai dai yawansu yasa ta kasa kirgawa ta shigo ta ajiye ta shirya ta wuce hospital. jiki a sanyaye ta shige office nata ta ajiye komai kamar yadda ta saba ta zauna ta kunna system ɗinta tana dubawa Dr Aliyu yayi sallama ya shigo bata ɗago ba ta amsa ya ƙaraso cikin kusa da ita ya ajiye mata leda tare da cewa
"Special Doctor ki sanya min albarka ga snacks da kolanut and sweet na sanya ranar bikina"
Cikin farin ciki ta ɗago ta kallesa ta ce
Na tayaka murna Allah ya sanya alkhairi ya kuma nuna mana lokacin.
Cikin farin ciki ya ce
"Amin thanks"
Samun wajen zama yayi ya zauna nan suka shiga tattaunawa akan aikin da zasu gudanar a daren yau kiran magrib ne yasa ya miƙe ya fice. 11:00pm ta dawo office nata ta cire white coat ta rataye sa ta dawo kan resting chair ta zauna tare da cewa
Wosh na gaji, ba a gama wancan wani sai ya biyo baya gashi jibi sunan Zeenat kuma morning gareta ko ya zatayi....
Ya turo ƙofar ya shigo cikin sanyin jiki ya ƙaraso tare da yi mata sallama ta amsa ta ɗaure fuska ya zauna kan kujera yana kallonta itama shi take kallo ya sakar mata da murmushi ya ce
"Wai damman babu wata alaƙa soyyayya a sakaninki da Dr Aliyu, niyi tunanin saurayinki ne sai gashi ya kawo min chewing gum da auren sa shine nace bari na shigo na sake tabbatar da cewa ba to yaudararki yayi ba"
Murmushi tayi ta ce
In kuma yaudara ta yayi fa what are going to do?.
Murmushi yayi ya ce
"Sai na mai dukan cin amanar ki da yayi har sai ta gane kuskuren sa sannan na kyalesa"
Ah lallai naga alama, da fatan dai ba kwayar kasha ba kashigo min office.
Dariya yayi yace
"A'a ai yanzu ban cika shanye² ba kuma ina so na daina ko zaki dinga ganin mutunci na"
Uhm Dr Mahmoud Allah yasa ba tuban muzuru kayi ba, Allah ya kara shiryarwa.
"Amin Dr Hamrah bari na tafi ko"
To Dr Mahmoud.
Ya fice tana mamakin sa lallai wannan mutumin to Allah ya sake shiryar dashi.
Washegari da safe ta tattaro ta dawo gida ɗakinta ta shige saboda jin shuru gidan kamar bacci suke basu tashi ba tana shiga ta faɗa kan bed ta kwanta dan ta huta bacci ya ɗauke ta sai 10:30am ta farka ta miƙe ta watsa ruwa sannan ta fito ta shige ɗakin Ammie nan ta taddata cikin sanyin jiki ta sanar da ita sakon Alhaji Sama'ila akan zai turo da magabatan shi nan ta ce da ita taje ɗakin Daddynsu ta sanar da shi. Ta shigo ta riskesa yana danne² cikin laptop nasa ta duka har ƙasa ta gaida shi ya amsa cikin kulawa yake dubanta cikin sanyin murya ta ce
Daddy, daman wancan mutumin ne yace zai turo magabatan shi nan da next Friday.
"Wane mutumin kenan likita?"
Ya tambaye ta ba tare da ya ɗago ba yaci gaba da abin da yake yi.
Ta sudda kai dan kunya abin da ya dace Ammie tayi shine ita zata yi kuma nawin hakan take ji, jiki a sanyaye ta ce
Alhaji Sama'ila na Abuja.
Yayi murmushi tare da sauke numfashi yace
"Allah ya nuna mana"
Amin.
Ta faɗa ta sake duban sa a hankali ta furta
Uhm Daddy.
"Na'am likita, da akwai damuwa ne?"
A'a daman tambaya ce nake so nayi daga cikin babanninmu mata.
"To likita ina jinki"
Daddy wacece Baba Hajara?.
Chak ya dakatar da abin da yake yi cikin sauri ya ɗago ya kalleta yana mamakin meyasa ta tambaye shi, yace
"Hamrah a ina ki kaji ana ambaton wannan sunan kuma menene dalilin ki na tambaya"
Ajiyar zuciya ganin yadda ya tashi hankalin sa lokaci guda sanan ya jima bai kirata da sunanta kai tsaye ba sai yau cikin sanyin murya ta ce
A'a Daddy kawai na tambaya ne.
"A'a Hamrah haka kurum bazaki tambaya ba sai da dalili"
Ta ɗago ta kallesa kamar yadda yake kallon ta tace
Da gaske Daddy na komai.
Ya sauke ajiyar zuciya tare da cewa
Wannan maganar ki barta anan kada kowa yaji sannan kada ki faɗawa Umar ma ya sani kuma ki cire ta cikin zuciyar ki, kin ji"
To Daddy.
"Tashi ki tafi"
Ta miƙe ta fice, jiki a sanyaye ta wuce ɗakinta tana mamaki meyasa Daddy baya so tasan wannan matar Hajara, meyasa da ta ambaci sunanta taga tashin hankali a tare da shi, ta sauke numfashi ta faɗa kan bed, tare da rumtse idanuwanta ta jima tana bacci sai yamma lis ta shirya ta wuce wajen aiki.
Zaune suke ana ta hayaniyar gidan bikin suna iya danginsu ma kaɗai sun cika gidan balle kuma ace da sauran ƴan uwa da ake zumunci, kasancewar ba wani aiki mai yawa suke yi ba sbd contract na komai sun bada ayi musu. Hamrah ta fito daga ɗakin mai jego ta nufo inda sauran ƴan uwan su ke zaune suna yanka cabeji da dai ƙananun abin da ba a rasa ba. Sanye ta ke da riga da skart ta farin lace tayi normal ɗauri tayi matukar kyau, komanta fari ne hatta sarka da ɗankenne da ta sanya masu duwatsu suma dare ne, plat shoe ɗinma fari sai kuma ɗan karamin jaka dake hannunta ma fari ta zauna kusa da Ayshe tare da ɗauro wuka tana kankare carrots tana gaisawa da ƴan uwanta da suka shigo, Maryama ma ta fito ta zauna Aunty maimuna ta kalli Hamrah tare da cewa
"To Hamrah sai a dage a fidda miji abar zaɓe tunda kinga ƙannenki girma ya fara kamasu Ayshe ta zama uwar gida Zeenat kuma ta fara tara yara Maryama ma a ɗakinta Ammar ma yana dawowa zamu aurar dashi, kinga zaki rage ke kaɗai ce"
Hamrah batayi magana ba sai ma murmushi da tayi taci gaba da kankare carrots ɗin, ba wannan bane karon farko da take fuskantar irin wannan daga familyn su dan haka baya damunta. Maryama ce tayi caraf ta ce
"To da wani auren ba gwamma ta shekara dubu a gidan su ba, wasu da su suke ci da kansu da kuma ƴaƴansu kai harda mijin ma, wlh ba zan taɓa ci da gardi ba sai dai ko kasannayi"
Sittt.... Aunty maimuna tayi tasan da ita take mara kunya kawai Indai Maryama ce zata faɗi fiye da hakan, dan kaf gidan itace zakka...
"Ke Maryama babu son rashin kunya da fusara dan tayi wa yayar ki magana akan ta fidda miji itama ta samu rahamar Ubangiji ta dalilin aure aɗaga gawarta sama tayi daraja shine ki ke faɗin haka to kul ki iya bakin ki, ai takai shine take faɗa mata haka me yafi daɗi a duniya bayan aure.
Cewar wata daga cikin dangin Ammie, caraf ko Maryama ta turo baki ta ce
"Oh ni Maryama har dasu kaza a da cin danko in ana magana ta aure da masu jini a wuya ake yi, ba wai waɗanda mazajen su suke tatil da giya ba su lakaɗa musu na jaki kuma su zauna ba, da irin wannan auren ai gwamma batayi saba"
Sittt......... Akayi bakin kowa ya mutu suna kallon Maryama cikin ɓacin rai da ta kuncewa Innarta zani a kasuwa kowa kuma yasan halin da ta ke ciki da ta sani batayi magana ba......
Comments and share
*MUJARRABI*
By SAYYADA ✍️ Barrister UMMUL UMMU ABIHA
09021706569
PG 27 & 28
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
______Kallon shi ta tsaya yi sbd yanda ya wani firgita da jin zancen yana wani waro idanuwa waje, ta yi murmushi, tana mamakin meyasa Ammar yaƙi jinin Alhaji Sama'ila ne, mutumin bashi da makusa da farko tana jin fargaba a kanshi amma kuma tunda ya faɗa mata wanene shi taji sanyi a ranta, zata aure shi ko dan hankalin Ammie ya kwanta ta daina fushin da ta keyi da ita duk da ba laifin ta bane ƙaddararta ce jinkirin aure, amma tunda Ubangiji ya nufa ta samu mijin aure zata rufawa kanta asiri ta zauna dashi.....
"Wai kina nufin tsohon nan za ki aura da gaske, look Hamrah kada kiyi gaggawar yanke hukunci ki nutsu ki sake fahimtar shi kada kalaman bakin shi su yaudareki"
Ammar munyi magana ya faɗamin cewa yana da mata da kuma yara 7 shi ɗan siyasa ne kuma ita ke kawoshi Maiduguri so no need na sake damun kaina akan sai na sake tambayar shi wannan bazayyi making sense ba, kuma ga shi babban mutum ne.
Sauke numfashi Ammar ya yi ya ce
"Bana ƙinshi ni kawai na fi son ki aure mutumin kirki sannan wanda shekarun shi bai ja ba, amma kuma tunda kin ce ya yi magana da Daddyn mu that's okay, to amma kwa bari ai na dawo daga training ko?"
Eh to maybe.
Ya haɗe fuska ya ce
"What do you mean by maybe kamar ma ɗauki ki ke"
Murmushi ta yi ta ce
Ai ya zama dole ƙanina ya halarci taron bikina, za a jira ka dawo.
"Yanzu naji batu, to me za ki bani na tafiya?"
To mai kuwa zan baka da ya wuce na yi maka addu'ar Allah ya kai ku lafiya ya kuma bada sa'a a bisa abinda aka je nema, a kula da ibada ayi riƙo da gaskiya ban da kanza dabi'a ko tarbiyya.
Ya yi murmushi ya ce
"Na gode babbar yaya amma kuma amin kyauta ta musamman "
Ok, na fahimce ka kace na haɗa maka snacks kamar yadda na keyi in dai za kayi tafiya.
Dariya ya yi ya ce
"Yes, kin gano ashe kin san kuwa daɗin cake ɗin ki na keji kuma yana ɗauke min yunwa"
To zan yi maka sbd kace dani babbar yaya amma badan haka ba, bazan yi ba.
Sosai ya ke mata dariya wato dai wannan son girman ba zai taɓa ƙanzawa ba amma yana son ganin ranar da zata dauki girman ta bada ta dauki ƙanƙanta.
Bayan sun kammala shirya kayan ne suka wuce kitchen ta shiga shirya masa caka, donot greba sun jima suna yi sannan ta samu ta kammala dare ya yi sosai gashi duk sun gaji kuma tana so ta tashi da wuri ta yi mashi rakiya airport sannan ta wuce office a adaddafe ta shige dakinta ta kwanta bayan ta kammala shirya mashi ta bashi ya wuce dashi ɗakin sa.
_WASHEGARI_
Da ƙyar ta iya tashi daga bacci ta watsa ruwa tare da ɗauro alwala ta idar bayan ta shirya ne ta fito ta tadda Ammar, Daddy da Ammie suna zaune a palour suna yi masa nasiha ta gaidasu, sannan suka fito ita da shi da kuma Daddy a tare suka yi mashi rakiya airport Daddy ke driving nasu. Bayan ya yi parking a parking space na airport ne ya fito tare da ce musu yana zuwa ta ɗau waya ta kira Dr Aliyu cikin rawar jiki ya ɗauka ta sanar dashi bazata iso da wuri ba duk abin da ya dace ya yi, su kayi sallama. Ammar ya kalli yayarshi tare da cewa
"Na gode yaya Hamrah da ƙoƙarin ki na jiya i really appreciate it, kuma in dai ina dasu to bana zama da yunwa. Zanyi kewarka ku"
Murmushi ta yi ta ce
Muma zamuyi kewarka, ka kula kaji banda soyayya da masu jan kunne.
Dariya ya yi sosai ya ce
"Ni abin da ya kaini shi zanyi ba wata sabuwar alaƙa ba, burina shine na yi nasara"
To Allah ya dafa muku.
"Ameen"
Suna cikin fira Daddy yazo Ammar ya fito ya wuce suna gani har jirgin ya tashi sama sannan suka juyo Daddy ya sauketa wajen aiki sannan ya wuce nashi office ɗin yau ba Ammar dake taimaka mash.
Kai tsaye office nata ta shige ta fidda duk abin da zata buƙata ta sanya white coat nata tunanin ta baki ɗaya yana general ward, turo ƙofar Dr Aliyu ya yi tare da sallama ya shigo ta juyo ta kallesa ta ce
Dr Aliyu sannu da kokari, na yi rakiya ne da safen nan.
"Lah ai babu komai Dr Hamrah, na kammala duba patients ɗin ma sai dai ko zuwa anjima sai ki sake duba su"
Ok na gode.
Ya fice yana jin daɗi, Hamrah na da saurin fushi kuma bata da riƙo gashi duk abin da ya yi mata ta yafe masa, sai ya ji jikin shi ya yi sanyi. Tunda Dr Aliyu ya ce ya kammala duba patients ɗin sai ta miƙe kan resting chair sbd hutawa gashi daren jiya bata kwanta da wuri ba kuma ta tashi da wuri. Baccin 10 minute ta duk jikinta yayi mata nawi bata sami isasshen bacci ba a hankali ta tashi ta zauna sai kuma taja da baya ta haɗe da jikin kujera tare da waro idanuwa alamun mamaki da kuma tunanin me yake nufi da yi mata sanɗa, lallai wannan mutumin yana wuce iyakar shi, ba laifin shi bane amma za tayiwa tufkar hanci, ta nuna shi da yatsa ta ce
Kai Dr Mahmoud abin naka har yakai kashigo sbd ina bacci, ka aiwatar da nufin ka a kaina to ƙaryarka ta ci ƙarya, to bari na takaita maka kada kaga kana kwalɓewa ana yi maka uzuri wai baka cikin hayyacinka to kasani ba ƙwaya ka ke haɗiyaba ko durum na giya ka ke sha to wallahi baka isa kaci galaba a kaina, tashi ka fice min tun kan na tara maka ma'aikatan cikin wannan Hospital ɗin.
Ta ƙarashe maganar cikin ɓacin rai da kuma tsantsan tsana