Showing 27001 words to 30000 words out of 74305 words
Chapter 10 - MUJARRABI BOOK ONE BY SAYYADA BARRISTER.txt
kuma Alhaji Yusuf yana ƙoƙarin fitowa Mommyn shatu tana yi mai rakiya cikin girmamawa ta gaidasu ya yiwa Hamrah kuri da idanu har ta shige ta girgiza kai a ranta ta ce Allah ya shirya. A palour ta tadda shatu aiko tana ganinta cikin murna ta ce
"Ƙawata kamar kin san ko kina raina daman cewa na yi koman dare zan shigo"
Murmushi Hamrah ta yi tare da cewa,
Aiko ba zan ma jima ba a gajiye na ke zan wuce, daman mu gaisa ne.
"Duk da haka sai na shafa miki labarin"
A lokacin Mommyn ta tashigo tare da cewa
"Hamrah ki zauna mana"
A'a Mommy daga wajen aiki na ke zan wuce ma.
To Shatu yi mata rakiya ko.
Shatu ta miƙe suka fito, Hamrah ta ce
Kamar Mommy ta sauko kin yi yadda muka tsara ne?.
"Eh na yi tun washegarin ranar na baiwa Mommyn hakuri dashi kuma Daddyn sai dai jikin shiya yi sanyi amma bai fahimci komai ba"
Ai ba zai fahimta ba sai nan gaba.
Dariya sukai suna fira har ta rako Hamrah kusan gidan su Hamrah ta ce
Yauwa ƙawata wannan mutumin na Abuja mun yi dashi gobe zaizo.
"Kai amma na ji daɗi ki ce na shigo mu haɗa beta na taran baƙo"
Ke rufani ki sayani, a da ma da nayi yarinta ke ɗibata yanzu kam ba wanda zan mai wata beta in ya yi mutunci na bashi ruwa, ballema shi wani abun ne zai kawo shi innayi beta ma sai yaga rashin hankalina.
Nan sukai dariya sannan suka rabu, Hamrah ta shigo gida a lokacin ma Ammar ya dawo yana tsaye yana waya ganinta yasa ya kashe ya ce
"Ashe baki shigo ba sai yanzu, na yi tunanin kina ciki ai"
Murmushi ta yi ta ce
Gidan su Shatu na shiga, me akwai ne naga kamar da labari.
Murmushi ya yi ya ce
Muje ki girka mana abincin ki mai daɗi.
Ta ɗan buge shi a kadaɗa tare da cewa
A gajiye na ke yau sai dai ka siyo mana a bin taɓawa a waje.
"To ƙanwata kada ki damu harda choculate ma zan siyo"
Hararar shi ta yi ta ce
Ko mutum zayyi ya ya dai girma an fi shi.
Ta yi hanyar ciki ya yi dariya ya bi bayanta. Ɗakin Ammie ta shige ta gaidata amma bata kulata ba ta wuce ɗakin ta har dare tana kwance, Ammar ya shigo masu da kayan ciye² ya ajiye tare da kunna tv suka soma ci sai suna fira sai da suka kammala sannan ya tafi ɗakin shi. Wannan ɗabi an tun suna yara su keyinta har suka girma basu daina ta ba, shiyasa akwai kyakkyawar fahimta a sakaninsu kuma basa ɓoyewa junan su sirrin su.
_WASHEGARI_
A hankali ta buɗe idanuwan ta tare da ƙurawa farin slink ido, tunowa da tayi yau Friday ne yasa ta sauke numfashi ta miƙe ta gabatar da sallah asubah ta ɗan taɓa karatun Alkur'ani sannan ta koma bacci bata farga ba sai wajen 10:00am da ƙyar ta iya tashi ta ƙimtsa dakinta sannan ta wuce kitchen ta dafa indomie ta zauna a kitchen ta ci, ta wuce ɗakin Ammie ta zauna a lokacin Daddyn su yana shirin fita, suka gaisa ya fice ta kalli Ammie a hankali ta ce
Ammie, anjima akwai baƙon da zaizo ya ce yana son magana dani.
Ga mamakinta sai taga Ammie ta saki fuskar har da ƴar murmushinta ta ce
"To saura ki yi sake kamar yadda ki ka yiwa sauran suka tafi"
Kanta a ƙasa ta ce
Ammie ba saurayina bane, haɗuwa mu kayi ya ce yana so muyi magana.
"Ah in ba abinki ba haka kurum ai bazai ce zaizo ba, ni dai na faɗa miki kisan irin tarɓar da zaki yi mashi"
To Ammie na gode.
_____ cikin nutsuwa ta ke shiryawa ta sanya riga da skart ta lace mai background pitch da kuma ratsi blue ya yi dai dai da shape nata ta yi normal ɗauri ta fashe Jikinta da turaruka masu ƙamsha tare da yane jikinta da gyalle ta dau wayarta dake ruri ta yi sallama ya ce
"Na iso"
Ok ka shigo ba damuwa.
To.
Ya faɗa ya kashe wayar.
Ta juyo zata fito sai ganin Ammar ta yi a tsaye yana kallon ta, ta ƙaraso ta ce
Meyasa ba kayi sallama ba, kuma kasan bana son hakan.
Haɗe fuska ya yi ya ce
"Ya yi tsufa da yawa, please kada ki bashi fuska wannan kwalliyar ma ki sauyata"
Sosai ta ke kallon shi cikin ɓacin rai ta ce
Ina ruwan ka da sufan shi sannan ma ce maka ya yi yana so na ne?.
Sauke numfashi ya yi ya ce
"Da gaske na ke ni kwata kwata bai kwanta min ba"
Ta raɓe ta gefen shi ta wuce ɗakin Ammie ta sanar da ita yazo, sannan ta fito.
Tun da ta fito Alhaji Sama'ila ya saki baki da hanci yana kallonta har ta iso cikin sanyayar muryarta ta ce
Sorry, na jima ba.
"A'a ai girman kujerar ki ne"
Ya faɗa yana tsosa keyar shi, ta janyo farar kujerar zama ta ajiye mashi ya zauna sannan ta ce ina zuwa, ta shige ciki, ta ɗauko mashi gorar swan water ta fito ganin Ammar ta yi yana yi mashi magana bata ƙaraso ba ta ɗanyi jim kaɗan sannan ta ƙaraso ya bar wajen ta ajiye mashi tare da cewa
Sannunka da zuwa.
"Yauwa"
Duk jikin shi ya yi sanyi ba kamar ɗazu ba ya ce
"Waye wannan wanda yanzu ya fice"
Ta sauke numfashi a hankali ta ce
Ƙanina ne shi.
"Ƙani"
Ya faɗa yana kare mata kallo, ya sauke numfashi, ta ce
"Eh girman jiki gareshi amma yaro ne"
Ajiyar zuciya ya yi ya ce
"Hamrah bazan ɓoye miki, ina son ki kuma da aure, tun a ranar da na hango ki har na tsayar dake muka gaisa na kamo da sonki, in har kin amince min nan da karshen wata zan turo magabata na a sanya ranar biki, kin san ni ba mazaunin nan bane wasu abubuwan ne suke kawo ni amma kuma hakan ba zai hana na tsaya ayi komai dani ba"
Jikin Hamrah ya yi matukar sanyi ta ɗago ta kalleshi kwarjinin shi yasa zuciyar ta harɓawa, bashi da wani abin da za a koshe shi sai dai girma da kuma girman jikin da yake dashi ne ba kowacce mace bace zata amince ya aureta. Ta sauke numfashi ta ce
To zan yi shawara tukuna, bani nan da kwanaki biyu.
Murmushi ya yi ya ce
"Ko dai ganin na fara tsufa ne?"
Ta yi murmushi tare da cewa
A'a.
Ya ce
"To ba matsala zan jira amma kada ki ja lokacin ya yi tsawo"
To.
Sun ɗan taɓa fira ta ce dashi zata wuce wajen aiki, ya ce ta fito ya sauke ta, taƙi amma ya dage hakan yasa ta shige ciki ganin Ammie ta yi zaune a palour tana ganin Hamrah ta ce
"Da me yazo"
Jikin Hamrah ya yi sanyi kuma amma yadda Ammie ta sake fuskarta yasa taji sanyi ta ce
Ammie cewa ya yi da aure ya ke so na.
"Alhamdulillah me ki ka ce dashi?"
A hankali ta ce
Na ce zan yi shawara.
"Ba ga irinta ba hamrah wannan halin naki shine ya sanya saura gudawa, wacce shawara da ta wuce ki amince"
Eh Ammie daman wai muyi magana ne.....
"Ammie gaskiya basu dace ba, kin gan shi kuwa sai ka ce Daddyn...
"Ammar ka ci gidanku, manya na magana kana saka baki, tshoholo ko shi ya kawa tsufa duniya tunda ya ce yana so angama"
Ya turo baki ya shige cikin ɗakin shi. Hamrah ta ce
Ammie zan shirya na wuce wajen aiki.
"To Hamrah a dawo lafiya"
Ta ɗago ta kalli Ammie sbd rabonta da taji ta faɗi hakan a kanta ta manta, ta wuce dakinta ta dauko jakarta ta fito ta shige ɗakin Ammar ta taddashi ya cika sai batsewa ya ke a dole Alhaji Sama'ila bayi mishi ba ta ce
AMMAR.
Ya kalleta da jajayen idanuwan shi bai ce komai ba ya ɗauke kanshi. Ta yi murmushi a ranta tace su Umar hali ya motsa ta zauna kusa dashi tare da cewa
Ammar, dama ce ta sameni bai kamata mu bari ta kubuce min ba, baka ga yadda Ammie ta saki fuska muna magana ba, sannan menene in na aure shi ai ba wani matsala ni ma ai na tsufa.
Ya sauke numfashi ya fisgar da iska ya ce
"Na yi mai tambayoyi daga dukkanin alamu bashi da gaskiya....
Kai Ammar, shiyasa ya ke tambaya ta wanene kai a gareni ashe da abin da ka faɗa mashi, Please tell me me ka faɗa mishi?.
Ban ce komai ba kawai tambayar shi na yi waye shi, menene sana'ar shi sannan menene taka mammen abin da ya keyi anan...
Ammar wannan ba hurumin ka bane, kabar manya su yi magana, stay out of this, abin da ka keyiwa sauran suke gujemin shine abin da ka ke so kayiwa wannan ko kana tunanin ban sani bane, to kasani muddin ka zama dalilin tafiyar wannan mutumin to babu ni babu kai.........
Comments and share.
*MUJARRABI*
By SAYYADA ✍️ Barrister UMMUL UMMU ABIHA
09021706569
PG 21 & 22
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
________ Bankaɗo ƙofar ya yi ya shigo kamar wanda kura ya biyo shi yana huci tare da zazzare idanuwan shi da su kayi jajir yana kallon ta cikin ɓacin rai, ba a taɓa mashi irin abin da ta yi ba, ta zubar mashi da mutunci a idon ma'aikatan da suke shakkan shi, who is she da za ta ja dashi, tsayawa ya yi a kanta yana sauke numfashi ya nuna ta da yatsa, zuba masa idanu ta yi tana kallon shi duk ya fita hayyacin shi ya ce
"Ke Hamrah ki ke ko what so ever, ki fita cikin idanuwana na rufe har kin isa ki tuɓe min rigan mutunci a bainan nasi, har ma jina haɗa kai da ni to ki sani kin taro match sai kin yi regretting abin da ki ka aika yau sai kin yi kuka da ba a haiho ki duniya ba"
Yana ajiyar zuciya, Hamrah ta miƙe cikin nutsuwa ta ke ƙare mashi kallo sbd su ta ke ta tabbatar da cewa shin a hayyacin shi ya ke ko kuma ya yi marisa dan ba abin mamaki bane zai iya aikatawa ta ce
MD ni bana ja da kai kuma bana haɗa kaina da kai, amma kuma wasan da ka fara ne na ƙarashe shi sannan duk abin da za kuyi ku aikata babu ni a ciki.....
"Hold on Hamrah, mu me ki ke nufi da mu ni da waye kenan?"
Ta sauke numfashi ta ce
MD I have told you, ka aikata duk abin da ka ke so amma kada ka sanya sunana a ci, sbd I hate sharri, ba nayi kuma ban so amin dan haka do what ever you want amma kada ka sanya ni a ciki.
Murmushi ya yi yana zazzare idanuwana yana bin office nata da kallo ya ce
"Na fahimta takamar ki wannan office ɗin ne to ki sani kina ji kina gani sai kin barshi, sai kin zubar da kwallah kina begging ɗina akan na dawo dake amma kash a lokacin kin makaro sbd bakin alkalami zai bushe"
Murmushi ta yi ta ce
MD shi sharri ɗan sako ne, zaka iya aikashi duk inda ka keso amma kasani zai je ne kuma ya dawo, da Allah na dogara babu abin da bawa zai iya yiwa bawa ɗan uwanshi fa ce da izinin Ubangiji, kuma Allah ya haramta zalunci bisa kanshi kuma ya hana ayi shi dan haka ba zai bari ka yi galaba a kaina ba sbd bani da hakkin ka, kuma God forbid na roke ka akan wani abin dunya kai wannan aikin ya dama dan haka kai za kayi ta daga hankalin ka.
Girgiza kai ya yi alamun za ki sani, ki jira lokacin sannan ya fice, ta zauna tare da sauke numfashi ta lumshe idanuwanta kanta ya fara yi mata ciwo sbd tsawar da ya daka mata, ta mike ta wuce general ward ta jima acen sai bayan la'asar sannan ta dawo office nata. Bayan ta idar da sallah ta sake komawa genaral ward har da vip sannan ta dawo nan ta tadda OG da MD suna magana ta shige cikin office nata ta hau tattare kayayyakin ta kammala kimtsasu OG ya shigo cikin girmamawa ta ke welcoming nashi ya zauna tare da duban ta ya ce
"Dr Hamrah lokacin tashi ya yi ko?"
Ta sauke numfashi tare da cewa
Eh sir, da akwai abin da zan yi maka shine?.
"No, babu kawai na fahimta kamar akwai matsala a wannan Hospital ɗin ne shine na ke so mu zauna nan da kwanaki biyu mu samu mu gano matsalar sai mu san yadda zamu gyara"
Ta sauke numfashi cikin farin ciki ta ce
Ok sir, as you do.
To shikenan, ina son bayanai na wannan Hospital ɗin da kuma ya patients suke ji da abincin da ake girkawa har zuwa kan fitan kuɗi da kuma shigowar shi sannan da sabon list na staff's da matsayin su"
Ta jima tana so ayi irin wannan zaman dan haka abin ya yi mata daɗi ta ce
Ok sir, zan shirya komai yaushe ne zaman?.
"Eh to ko zuwa Thursday haka"
Ta sauke numfashi tare da cewa
Thursday.
Ya kalleta ya ce
"Ko da matsala ne?"
Akwai biki shine daman zan karɓi hutu na kwanaki biyu zuwa uku sai Monday na fito bakin aiki.
Shuru ya yi na wani lokaci sannan ya ce
"Kamar yaushe kenan?"
Thursday zuwa Saturday, tunda Sunday weekend ne sai na fito Monday.
"Ok ba matsala sai ki yi magana da partner nki na office da kuma na duty"
Na gode sir.
Ya miƙe ya fice itama ta ɗau jakarta ta fito ta sanyawa ƙofar key ta hango MD yana yi mata mugun kallo bata bi ta kanshi ba tayi tafiyarta har ta iso ƙofar fita ta ji muryar Dr Aliyu yana cewa
"Dr Hamrah shigo na kaiki gida"
Ta juyo ta ɗan kalleshi sai kuma ta ɗauke kai ta fice yana kallonta ta hau a daidaita ta wuce. Ta iso gida ta tadda Daddyn su zaune a farfajiyar gidan ta gaida shi sannan ta wuce ciki ta iso ɗakin Ammie nan ta gaidata bata ko amsa ba da safen ma albarkacin Daddyn su yana ɗakin ne har ta miƙe zata fice ta ce da ita
"Hamrah da fatan baki mance da abin da na faɗa miki ba ga me da fidda miji, nan da karshen wata kuma kinga lokacin matsowa ya dan haka ki je ki yi shawara tun kan lokacin yazo"
Kan Hamrah na ƙasa ta ce
To Ammie.
Sannan ta fice jiki a sanyaye ta shige ɗakinta. Ajiye jakarta ta yi ta faɗa toilet ta watsa ruwa sannan ta fito ta shirya cikin doguwar riga mara nawi ta zauna a bakin bed ta yi tagumi tana tunanin abin da Ammie ta ce, to ko dai kawai ta faɗawa Alhaji Sama'ila ta amince ya turo ɗin ba tare da ɓata lokaci ba, wata zuciyar ta ce to ya za ki yi da Daddyn da ya ce sai ya yi bincike....
Ƙirana sallah magrib yasa ta miƙe ta shige toilet ta ɗauro alwala ta idar tana kan dardumar sallah tana ta lazimi har lokacin sallah ishai ya yi ta idar, tana jin yunwa kuma bazata iya tashi ta ɗaura komai ba akan gas duk ta gaji, dabara ta faɗo mata ta ɗau waya ta kira Ammar ya ɗauka tare da cewa
"Yanzu zan iso gida....
In ba kayi nesa ba kazo min da abin taɓawa yunwa nake ji.
"Babu na siyo ma, zan ƙaraso yanzun nan"
Ta katse wayar, Alhaji Sama'ila ya ƙira da ta yi saving da Abuja ta ɗauka tare da sallama ya ce
"Na yi fushi ba a kira anmin ya gajiya ba"
Murmushi ta yi ta ce
Ayi hakuri ina niyya.
Ya sauke numfashi ya ce
"To ya zanyi in ba hakurin zan yin ba, da fatan kina lafiya?"
Alhamdulillah, ka sauka lafiya?.
"Alhamdulillah, lafiya lau, da fatan da zaran na dawo zan ji amsa daga gareki?"
Ta sauke numfashi tare da cewa
Eh Allah ya dawo da kai lafiya.
"Yauwa likita na gode, zan huta sai zuwa gobe"
Su kayi sallama. Ammar ya shigo yana sauke numfashi ya ajiye ledar tare da cewa
"zan je na watsa ruwa ki ci ki ajiye min nawa"
Tab aiko in ka jima sai dai biri ya ganka.
Ya yi murmushi ya ce
"Yanzu zan fito ki ci iya cin ki"
Ya wuce, ta buɗe ladar chibs ne da roasted fish sai kuma banana juice ta miƙe ta wanko hannu ta soma ci, ya jima sannan ya shigo sanye yake da bak'ar jallabiya wacce ta hasko fatarsa, kunna tv ya yi ya ce
"Yanzu kallon news ɗin ma ba kiyi"
Ya zauna ta ce
Kayya abin kaina ma ya sha min kai, ni mantawa ma nake da kallo.
Hannu ya sanya suke ci a nutse suna fira shikuma yana kallon Ball, ta zame hannunta ta miƙe ta shige toilet ta wanke ta fito ta zauna bakin bed tana kallon shi ta ce
Ammar ranar yaushe ne specific time or day na tafiyanka?.
Ya sauke numfashi tare da cewa
"Next Tuesday by the grace of God"
To Allah ya nuna mana.
"Ameen, me ki ke shirya min ne?"
Don't know amma sai na yi tunani tukuna.
Ya miƙe ya shige toilet na ta ya wanke hannu shi ya fito ya ce
"This coming Saturday ne ko auren mijin Ayshe?"
Ta sauke numfashi tare da cewa
Eh fah, zuwa jibi ma zan koma cen amma gobe na keso muyi magana da Ammie da kuma Daddy akan batun.
"To hakuri za tayi haka Allah ya ƙaddara, in ba abin Bukar ba me zayyi da mata har biyu wannan ai ɗaurawa kai pressure ne"
Murmushi ta yi ta ce
Baza ka gane bane Ammar you are still young, kai ma da ka kai irin age nasu haka za kayi ku maza ai sai a hankali.
Ɓata fuska ya yi ya ɗago ya kalleta tare da cewa
Ki daina faɗamin ni yaro ne, zuwa yanzu na girma kuma zan iya aure kawai dai baya agenda na ne amma ni nasan ba yaro bane"
Dariya ta yi tare da hararar shi ta ce
Do you know what you are saying Ammar, aure fa kace, ce maka akayi auren abin wasa ne, umm kai yaro ne mana da sauran ka.
Ya sauke numfashi cikin ɓacin rai ya ce
"Wallahi ki daina ce min yaro, zan baki mamaki ai ina dawowa na yi aure ko dan ki tantance ni yaro ne ko kuma na girma, ina su Ayshe ƙanne na ne to ai babba ne ni"
Murmushi ta yi ta ce
Kai da aure sai nan da 10 yrs.
Ya miƙe cikin kulewa ya wuce ɗakin shi, wai me Hamrah ta ɗauke shine da zata ce mashi yaro, zai je ya