Showing 27001 words to 30000 words out of 60233 words
Chapter 10 - AUREN FARI Complete by Maman Abdallah.txt
duk abinda kika gani.
Ta karba *Au yo ai ke lissafin naki hada riba ya dora* nake ga dubu Dari ne.
Tabb wallahi baki basu sarka zan siya miki dasu.
Sarka? To ke kuma fa me zaki dauka?
Tayi murmushi wallahi bani taba miki kudi kinji na rantse. Wadancen ma suna nan zamu ajiye tsaron lalura. Daga wannan watan idan ya baki zan fara miki siyayyar kayan kitchen ina ajiyewa, ki ringa basu dubu biyar din.
Allah yana tare da maraya. Kuma kayanki nacan duk na bayar dunki saura leshi da atamfa na ajiye zuwa gaba.... Wallahi nabarwa farida nima na rantse bazan karba ba.
Ta rasa me zata ce mata .
Tayi saurin canza zancen *kuma Hajiya zata sanyani makaranta.* ta kamota ki bari don Allah, Allah har an fara mun lesson ma Dana gama fahimta zan fara zuwa. Amma tace inyi shiru ,
Nima abinda zance kenan. To Alhamdulillah ai kyawawan dabi'un ki umaimah bazaki taba wulakanta ba.
Suka sha fira, umaimah ta fito zuciyarta fes! Duk wata damuwa ta rageta.
Lokacin da ta shiga kowa ya kwanta, itama tabi lafiya, amma jiya wayau, barci sama sama tunani ya hanata runtsawa.
Goggo ce ta tada ta karfe biyar da rabi, *Barcin ubanwa kikeyi* ta kai mata duka tayi firgigi, shegiya kafaffiya duk gargadin da yayi miki shine yau ma kika gyara kwanciya? Idan ke zaki janyo wa kanki da sauki muma tana iya shafar mu ja'ira mai taurin kan tsiya. Ki tashi kiyi man wanke wanke da shara.
Haka ta yi sallah ta hanzarta kada ta makara,
Daga bakin gate ya hango shigowarta tana ta uban sauri rataye da jaka, yana tsaye sama yana kallon ta har ta shige ciki. Yayi murmushi ya koma daki ya kwanta.
Ko da ta shiga babu kowa falon tayi ciki tana gunani, masifa ce kawai ko nazo ko banzo da wuri ba ina abinda ya dameshi tunda ba jirana yakeyi ba. Idan ta gaskiya ne ya zauna falo mana.
Mtsew taja tsoki.
Tana shiga mamee ta tashi zaune 'yar halak kinki ambato wallahi yanzu nake shirin kiranki a waya.
Tayi murmushi gani ta samu ne?
*Dan kifin nan* zaki siyo mana irin na rannan kiyi mun faten dankalin ki......hahahaha lallai kinji dadin sa. Kuma kamar wasa na kwatanta dana gani a *Arewa 24*
A a da dadi kam, ki siyo mun tumatur irin manyan nan. Tayi murmushi kwadon ne ko?
Kin tuna mun da *lansir* ....ai fa ta fada tana laluben inda kudin suke, ta dan juyo nawa zan dauka don zan siyo kwakwa da danyar citta...... Dauki dubu biyar ai lissafi yanzu kika fara.
Duk sukayi dariya, kifin na nawa?
Dubu daya ko yayi kadan?
Kuma zan dauki har dubu biyar? *lansir* din da na hamsin ma mugun wajiba akeyi dashi?
Ta yi yar dariya kedai dauki hakan nasan yalo, soyayyar aya duk suna can suna jiranki, suka kara dariya.
Yi sauri ko kya dawo.
Saboda duk kasuwan kowa na sammakon siyayya saboda juma'a ce sai goma saura ta dawo, tana shigowa ta tarar dashi zaune ya hada gabas da yamma. Simi simi zata wuce ya daka mata tsawa...
*Daga ina kike?*
Ta yi chak!
Ko ba kya ji?
Kasuwa, ta fada kai sunkuye
Ya banka mata harara tare da yamutsa fuska *kasuwa?*
Ya mike , ta yi sauri ta bude jaka wallahi kaga mama ta aikeni na siyo kifi, tumatur, lansir ta fara fiddo kaya ruwan kifin duk sun bata jakar da na tumatur.
Ya zaro ido *What?*
*Umaimah kina hauka ne jakar *200+ kika sako wannan shits din*????
Barkan mu da rana
*Maman Abdallah*
😘😘😘😘😘😘😘
[1/26, 9:59 AM] +234 813 180 9991: 💑 *AUREN FARI* 💑
0⃣1⃣9⃣
...... Kayi hakuri ledojin ne sukayi mun yawa shine naga meye amfanin jakar....
Ya finciko ta baki fahimci me nace ba? Kin San kudin jakar nan kika sako mata wannan tarkacen?
Ya girgizata *dubu dari biyu da hamsin* Ta zaro ido na shiga uku, ta zazzage kayan da sukayi ragowa tana kyarma, *dubu dari biyu da hamsin* kudin kawai take maimaitawa duk ta gigice sai kawai ya rungume hannu yana kallon ta cike da takaici,
Tabar jakar nan ta shiga kwashe kayan tana kaiwa kitchen, sannan ta dawo ta dauki jakar tana dan sayar kallon sa,
Ta tarar komai an hada mata har dankalin an fere, ta shiga hadawa,
Koda ta gama ta kawo musu bisa table bata tsaya ba sai tayi ciki. Ya bita da kallo, *yarinyar nan muguwar bagidajiya ce mtseww*
Mamee ta kalleshi cike da kulawa lafiya?
Ya ce ba komai,
Ta zuba faten zata fara sha, ya kalleta
Meye ke kamshi haka?
Faten dankali ko zaka sha?
Ya danyi jimm, eh kamar hakan.
Tayi murmushi kilibabbe,
Wasa wasa sai da ya share plate biyu, a lomar karshe ya kalleta mamee dama shi kika mun tayi last time na bar dadi haka?
Tayi yar dariya au kajiye ma bakin ka kenan.
Gaskiya ya mun dadi ayi. 'Yan aikin nan naki na bada wuta kwanannan.
Na lura masu kalacin safe sunfi sauran iya abinci fa, last week ma na ci wani Dan bread da SOS ya mun dadi a office kamar na kuma waya.
Ai uwani na kokari kam don yanzu kalaci inba ita ta hada mun ba bana jin dadin sa saboda yan makulashen nan.
Uwani? Ya bukata,
Uwani fa ai karambanin ta ya wuce inda duk kake tunani, duk abinda ta ga wani yayi sai ta kwatanta.
Ga tambaya, ai tana da kwalwa.
Lallai idan akwai saura zanci da dare a ajiye mun.
Ta kalleshi da sauri *a ajiye ma Kana nufin a *dumama*? Yayi murmishi haka na ce mamee,
Umaimah kuwa tana baya ta debo uban *klin* ta zuba a katuwar roba tana ta gurzar jaka, mamee ta kwala mata kira,
Ta antayo da gudu hannun ta duk kumfa,
Ya bita da kallo duk ta jike hijab dinta,
Naga hannunki kumfa me kikeyi agogo? Mamee ta bukata tana kallon ta cike da kulawa.
Tadan murza hannun kumfan ya fado kasa tana satar kallon sa, jaka nake wankewa...... Ya dago *what a ruwa kika saka ta?*
Mamee yar nan taki wallahi duk abinda nayi mata kar kiyi magana.
*Da tayi maka me?*
Ki tambayeta gata nan, ya nuna ta da yatsa,
Uwani me kika mishi?
Ta dan kara kame jikin ta tana dan in ina....... Uwani matso nan saki jikin ki. Ta kalleshi wallahi bani son takurawa yarinyar nan da kake yi madaki tsoron ka takeyi kamar me dubi yanda jikin ta duk ya rikice da kyarma ina dalilin wannan azaba?
Ta kamota me kikayi mishi?
Jiya ne ya ban jaka ban san cewar mai tsada bace shine....... Ki faro mata daga farko.... Ya katseta.
Kai bana son shiga uku kai ka fada man mana.
Mamee yarinyar jiya zan tafi stadium na hadu da ita hanya zata je gida na taimaka mata na rage mata hanya na ganta da kudi a hannu na ce bata sawa jaka ta ce bata da ita, na biya na siya mata mai tsada shine yau ta yo cefane da ita duk kifi da karikitan data siyo ciki ta zubo shine......... Shine me?
Ina ruwanka idan wuta ta saka ta Ina ce kai dai ka bata ko?, zai yi magana ta daga mishi hannu kai bani son rashin gaskiya, daman ka siya ne don ka uzzura mata, duk tsadar ta ina ita zata san haka?
Ta kalleta kin rage dan faten? A a duka na juyo shi sai Wanda na diba a plate...... Sai ki ajiye mun shi kar ki taba.
Mamee ta bishi da kallon takaici,
Ko bakiji ba? Ta ce to zata juya, mamee ta kamota je ki ci fita batun sa,..... Haba mamee ....... Zakayi mata kurulla ne?
Sai kawai ya mike ya nufi kitchen din ya dauko. Wai madaki meke damunka?
Ai mamee idan na zauna gidan nan wata rana ma cewa zakiyi ba ki haifeni ba sai uwani ya wuce sama da plate din.
Ungo wannan je karasa cinyewa kyaleshi. Kullum ganin kansa yakeyi yaro karami shi yasa nake burin yayi *Aure* gaban umaimah ya fadi *wai ya zanyi naga madaki da wata?*
Tayi ciki tana karasa wanke jakar,
Ta ringa jiyo hayaniyar mutane, ta sami mamee daki ta ce, kamar baki nakeji falo.
Wannan fitinannen ke meeting ai shirin zuwan su ne jiya na wuni baya ina gargadin su mansurah, manya manyan manajojin sa ne,
Au, ta fada a takaice.
Firatan ya ki hawa sama duk ya takura kowa.
Madaki kuwa yasan yau wuni zaiyi tare dasu gashi baya son umaimah ta tafi bai sani akwai maganar da zaiyi da ita.
Karfe uku aka fara shirya musu abinci kamar yanda ya tsara, umaimah an dage aiki baji ba gani, magana yakeyi amma hankalin sa na gunta idan ya hangota ta fito.
Ashe shima cikin manajojin shi daya ya hangota nan da nan hanakalin sa ya dauku. Ya dan juyo yana sosa keya,
'Yallabai ni fa na hango iri.
Ya maida hankalin sa gareshi sosai saboda shine babban manager da yake ji dashi a Lagos yake,
Iri na me?
Dai dai ta fito ya ce waccen yarinyar....... Ya sha mur *Bana son maganar banza* abinda ya kawo ka kenan?
Nan da nan ya kame kansa saboda suna bala'in tsoron sa.
Suka tafi zuwa dining, Sun fara cin abinci kenan sai gata da tray an nado kaji gasassu. Rashin sani ta ajiye gaban manager ya dago kai tare da dan murmushi ita ma ta mayar mishi, ya ce sannu....... Wata fizga yayi mata sukayi ciki ya kaita har kofar dakin mamee ya ingizata *wallahi kika kara fitowa sai na bata miki rai* ya juya.
Ta bishi da kallon takaici, su manager na ganin haka jikin kowa yayi la'asar ya dawo yanata mazurai ya nuna ma kowa plate *serve your self*
Kowa sukuku ana ci ana tattaunawa. Yana sauraron kowa yana kurbar lemu yaki cin komai.
Umaimah kuwa tana shiga ta ce mamah mun gama bari na dan huta , suka fara fira,
Bayan sunyi sallah suka dauko gyada mai bawo soyayya data siyo kasuwa ta juyo ta a tray suna ci.
Gashi an rufe kofar baya ya ce kada Wanda ya bude, ga shidda ta wuce tana son tafiya gida, ta rasa yanda zatayi. Kamar mamee ta karance ta, Uwani yau ko fira za a mun naga baki fara wannan saurin naki ba gudu gudu.
Ta danyi murmushi, na ga har yanzu suna falo kada ya ce ina mishi sintiri.... Ke kama hanya ki tafi gida kinji gobe kin san akwai lesson kuma na safe.
Taji wani kwarin guywa ta fito simi simi *ya daka mata tsawa bana ce karki fito*.......tayi baya guje
Mamee ta ganta kamar an jefo ta. Ke lafiya waya biyoki?
Tayi shiru tana kallon kofa.
Ya mike tsaye, kowa na iya tafiya gobe ma karasa by 8:00am. Yana gama fada ya haye sama da sauri.
Mamee ta ce muje ta taso ta a gaba. Ba kowa falon umaimah tayi turus.
Kama hanya ki tafi gida yanzu kyaji kiran sallah.
Ta ringa hada kafafu don sauri gudu gudu ta fito tana rufo kofa taga mutum tsaye.
Ya figeta sukayi wata hanya, me yasa ke kullum kin fi so kiga ina miki hayagaga?
Ta sunkuyar da kai.
Ya bita da kallo wai yarinyar nan yanzu bata biye mun?
Da ke nake magana . tayi shiru, idan kika kara fitowa nayi baki sai ranki ya baci daga yau.
Ta ce toh a hankali. Ya kalleta sosai, ko bakiji ba?
Naji, ta ce kanta a kasa.
Ya dan saketa ga jakar ki can da kika ki karba ta tsaraba na ce maikudi ya kaiki gida kije yana jiranki...... Ta kalleshi da sauri maikudi drivern sa da baya tuka kowa?
Ta girgiza kai bana shiga.
Dalili?
Haka nan,
Idan na ce dole fa?
Malam bafa zan shiga motar ka ba, kawai sai aga cewar waccen motar ta ajiyeni wane kallo za ayi mani?
Zai kara magana ta hada hannuwa don Allah ka kyaleni haka nan na kai makura..... Har jakar bazaki dauka ba?
Ko na karba zan raba ka da su ne ba tare da nima na amfana dasu ba to meye amfamin amsar?
Ya kalleta har zaiyi magana ya ingijeta ya wuce....
Ta bishi da kallo ohh wannan akwai bahagon mutum ta wuce tana yan tunane tunane.
Ya wuce masallaci yana magana kasa kasa cikin fada, gidan nasu zan je in kyare masu warning duk shegen da ya yi amfani da kayan inci uwashi. Ai na karanci matsiyata tun jiya.......
*Mukwana lafiya*
😘😘😘😘😘😘😘😘
[1/26, 9:18 AM] +234 813 180 9991: 💑 *AUREN FARI* 💑
0⃣2⃣0⃣
....... Tana shiga ko zama batayi ba goggo jummai ta nuna mata tulin kayan wankin ta ita da yara,
Ko sallar magriba batayi ba ta shiga yi don ko hijabi ta nufi cirewa ta tabbatar sai ta daketa,
Karfe takwas da rabi taci dunin wankin sosai, duk suna bisa tabarma ana ta shewa ita ta basu baya.
Tsit taji gidan yayi kamar wuta ta dauke ta juyo da sauri, katti ta gani ko wane da bakaken kaya tadan ware ido nan da nan ta gane ko su waye, ta mike zumbur dai dai shi ma ya shigo wasu na binsa a baya.
Duk su goggo suka makure sun kasa ko motsi ganin ko wane da bindiga,
*Sannu da zuwa*..... Ta fada hannunta jage jage da kumfa, ya kalleta Tun daga sama har kasa sannan ya fara waiwaye ya hango tulun wankin da ke ajiye da kuma Wanda ke a robobi manya.
Ya sha mur *Zuwa na yi in miki gargadi na karshe*
Tunda mamee ta na ce sai kin mata aiki to babu yanda zanyi domin duk abinda takeso bana kin sa matsalar bazan taba daukar *Kazanta ba* duk yan aikin gidana babu kazama irin ki, ya nufeta kamar zai shaketa tayi baya ya dan bita, *Kinga wannan jakar?* kaya ne a ciki Su zaki ringa sakawa kina zuwa aiki na san ko kala nawa ne don ni na siyo, ko wane turare, sabulu, mai da duk abinda ke ciki nasan kamshin sa da adadin da zaiyi.
Ya fizgota na sanki da *Taurin kai* ki bada ko toothpaste ne kiga yanda zan *halaka ki da Wanda kika ba din*
Su goggo kowane ya zaro ido tare da hadiye wani dunkulallen miyau.
Ya kalli lubabatu dake bakin tabar ma *Ina ne take kwana?* ya daka mata tsawa. Ta tsira hannu *Gashi can*!
Ba tare da yayi magana ba cikin kattin wani ya yi ciki da jakar.
Ta kalleshi cike da takaici wannan mutum akwai wulakantacce ni zai kira *kazama*? Ji yanda yazo yana mun hayagaga har gidan mu ban tsira ba. Kai ohh ni umaimah na jefa kaina a jafa'i.
Ya kalleta sosai *Ki rufawa kanki asiri ki bi doka ta* ya juya kawai duk suka bi bayansa.
Ta bishi da harara ta wuce wurin wankin ta.
Lubabatu ta saki ajiyar zuciya, goggo jummai ta ce yau naga masifa, wannan matsiyaciyar yarinya zata janyo mana bala'i.
Kowa na tofa albarkacin bakin sa amma goggo hansatu ko motsi sai da luba ta lura sannan ta tabo ta *inna*..... Tayi firgigi ta ce *Wayyo mun shiga uku*....... Duk aka kwashe da dariya ta mike da gudu ta suri buta tayi kewaye.
Umaimah me zatayi ba dariya ba. Ta ce su goggo manya wannan 'yar barazanar ta firgitata da sune yake ma wujijjigawar da nakesha wataran mussai zasuyi. Ta kara tuntsirewa da dariya sai kawai ta ganta tsaye gabanta tana nishi idanu duk sun fito, kyayi dariya don ubanki hankalin ki ya kwanta ki kawo mana ajalinmu har gida.
Ta shiga bambami kowa ya dunga zagin umaimah.
Ta waigo goggo haka fa yake da wannan masifar ta babu gaira, saboda Allah luba bana tsafta idan zan tafi?
Duk suka kwalalo ido *Anya yarinyar nan bata tare da aljannu?* firar yau batayi tsawo ba kowa ya shige daki.
Sai goma saura ta gama tayi salloli, ta kura ma jakar ido gabanta ya fadi *Ohh ni umaimah*
Ta juya luba kinyi barci?
A a ido na biyu.
Au, kuma kikayi lamo? Tashi mu danyi fira bana jin barci wallahi.
Ta janyo jakar ta bude sai kawai ta dafe kirji *Na shiga uku* wasu irin kayana ta gani ta ce luba zo ki gani.
Mi? Tabb um um , sai kawai ta bata baya kada ma ta hango wani abin ya birgeta. Tayi murmushi ta dauka wasa takeyi sai ma tayi mata banza.
Duk sai taji babu dadi *wannan ai mugun hali ne* ta fada a hankali. Kiri kiri yazo ya firgita jama'a. Dogayen riguna masu kyau wasu matsattsu wasu budaddu, turaruka, Mayan shafa wani abin ma bata San ya ake amfani dashi ba,Gyaluluwa kai kaya barkatai , kunya ta kamata ganin brezias mtsew ta buga tsoki ta rufe jakar.
Luba dai na jinta tayi lamo.
*Madaki* kuwa suna fita yaji kamar ya koma ya dauko umaimah su tafi gida. Yarinyar nan tana wahala gidan can. Wanki hada na yara?
Amma mutanen nan akwai matsiyata, zasuci ubansu, ya kuta.
Sai na gama ci masu uwa sannan in dauketa in mayar da ita gidana zan fara nemo waye uban tukun shima dayan *shashashan*
Yayi dan murmushi Matsoratan banza duk sun rikice ganin bindiga. Sai na mayar dasu ma'aikatan ta a gidan *nasu wasa ne*
Da safe ta fito da shirin ta normal zata tafi , tayi karo da goggo lami, ta kalleta sama da kasa Sai kawai ta fizgota ta fara bugu, duk mutanen gidan suka fito lafiya?
Ta kallesu tana nishi Ku dubi duk