Showing 36001 words to 39000 words out of 52988 words
Chapter 13 - HAYAR MACE! BOOK COMPLETE BY OUM HAIRAN.txt
short da yawa na yini banida charge ne da?yar na samu 30% don kar kujini shiru ayi uzuri kamar yanda aka saba Please......._
[8/11, 9:00 PM] Am Oum Hairan: *_HM 43-44_*
_Littafi na na ku?ine sis kiyiwa Allah karki karanta in baki biya ba, 300 PC 700 view acct details 3184512451 first bank or 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank._
_Ko kati MTN ta WhatsApp number na 09013718241_
_?an Niger zaku tura kati Airtel na 500f ta waccan number dake sama_
Wata hargitsattsiyar na razana Safiyyah tayi har tana fatali da flat na abincin wajen mi?ewa tayi baya da sauri idanunta na zarowa ta bu?e baki zatayi magana Alh Halil ya mi?e ya tako gabanta yakai hannu zai riko hannunta ta janye yayi murmushi tare da cewa.
Kafin zuwana gareki Saida nayi tunanin irin wannan yanayin ?asansa ko kuma mafiyinsa saidai zuciyata tanata karfafamin gwiwata akan ?udurina na alkhairi Safiyyah kinada hankali a zahiri tun dawowata kike karakaina a zuciyata saidai na kasa samun kwarin gwiwar tararki domin fallasa Miki sirrin zuciyata, na sani kinajin kamar bazai yuwu ba saboda idanunki yana kallo Miki irin tashin hankalin da uwar ?akinki zata shiga idan ta samu wannan labarin, amma Ni a tunanina sai nake ganin tunda kun fahimci juna zamanku matsayi ?aya bazai ?agawa kowaccenku hankali ba musamman Salima tunda tariga ta sani na fa?a mata tsayin zamana da ita shekara goma sha tara banta?a jin ina muradin ?ara aure ba sai a ?an kwanakin nan na tabbatar mata zanyi aure kuma ta amince tare dayi mani fatan alkhairi....."
Tunda ya fara maganar sai yanzu Safiyyah tayi yun?urin katseshi da cewa “Koda yake ka sanar da Mom kanason ?ara aure amma zakaji kunyar sanar da ita wannan yasasshiyar gantalalliyar mara asalin data bawa rayuwarta tallafi da ku?inta da lkcnta itane shai?an ke ?awata maka ka massheta matsayin kishiyarta bayan ta gama ginata, Dad ina masifar ganin mutumci daraja da ?imar mutum me siffar kamala da dattako irinka don girman Allah kada ka sake bari zuciya ta ayyana maka irin wannan gingimemiyar ?arnar domin aikatata sake maida rayuwata cikin kwa?on lalacewa ne....."
Ji tayi an rufe mata baki ta sauke idanunta kan hannunsa ya lumshe idanunsa yace “Please ki daina irin Wa?annan kalaman ki zama jaruma wajen fuskantar duk abinda zai faru nikam nayi niyyar aurenki don Allah kuma don ceto rayuwarki data ?anki daga halin da zata iya fa?awa a gaba so duk ma meye zai faru saidai ya faru"
Hanya ya nufa zai fice daga ?akin tayi saurin taroshi ta dur?ushe gabansa tace “Ka ceci rayuwata wlh tsaf Mom zatayi layya da namana indai akanka Ni bayan hakan Nima banaso wlh banasonka Ni uba na daukeka kada ka zama ?aya cikin mutanen da keson tabbatar min da duniyar yanzu don kai da neman mafitar kai akasa a gaba don Allah karka za?i rabani da ?ungushen arzi?in da nakeci harma da tagomashin gyaran rayuwa da ya?ar jahilci Dad kayimin rai kaji ?aina ka barni naci gaba da rayuwa a haka nikam ban za?eka ba....
Rufe mata baki yayi yace “Ni na za?eki bada da?ewa ba komai zai kammala idan kinso ya yuwu cikin sirri idan kinso kuma kiyi kwakwazo" ficewa yayi daga ?akin Safiyyah ta zube kasa cikin mugun tashin hankali da ?aurewar kai na rashin abinyi Amjad ya tako gurinta yazo ya shige jikinta yana wasa da jelar dogon gashinta dake ta yayeshi, ?an?ameshi tayi ta rushe da kuka cikin tausayin kai tace “?arshen zamana dasu yazo Amjad inason zama da Dr Salima amma mijinta yasa takobi ya datse dole nabar masu gidansu....."
Ita da yaron da baya fahimtar komai take wannan surutun taji wayarta tayi motsi alamar an ta?eta ta mi?a hannu ta ?auko Number Dr Salima tagani, aikuwa gabanta yayi kwance? ya fa?i ta kasa ?agawa har ta yanke can ta kuma kira tasanta bata ?aunar tayi ta kiran waya a?i ?agawa hakan yasata ?agawa cikin dasasshiyar murya tace.
“Hello Mom" da fara'arta tace “Ko nemana bakiyi Safiyyah ya gidan da Amjad?" A sanyaye kamar mara lafiya hawaye na zubo mata tace “Amjad yana lfy" da sauri Dr Salima tace “Ke fah meye ya sameki naji muryarki kamar ba daidai ba?" Rushewa tayi da kuka batare da ta iya cewa komai ba, nan hankalin Dr Salima ya tashi tace “Ya Salam Safiyyah meye hakanne meye matsalarki da zaki dagamin hankali ko wani abu ya faru?" Girgiza kai tayi Mom tace “kiyi magana mana" cikin sautin kuka tace “Bab....ba komai Mom don Allah...." Shiru tayi Dr Salima taja numfashi tace “kiyi mgn mana ko kuma kije ki fa?awa Ambassador nasan zaiyi Miki mafita kafin na dawo"
Kashe wayarta tayi cikin tausayawa kanta da Dr Salima ta ?auki yarda ta bata ta bawa mijinta ?aukar ?a da mahaifi takeyi musu ashe shi kuma ba haka ya ?auka ba ya ?auki wani abu daban a zuciyarsa.
Haka ta ?arasa yammacin ta batada wata walwala komai yinsa takeyi a dole da safe ma kasa fita parlourn tayi kamar yanda aka saba ayi break wajajen goma da rabi taji ana knowking tunaninta ko Nanny ce tazo ?aukar Amjad shiyasa ta mi?e ta bu?e gabanta ya fa?i ganin Alh Halil tayi saurin tura ?ofar ya turo tare da shigowa yace “Haba amaryata yada fushi haka ni ba fushinki da ?oye?nki ne zai dameni ba zama da yunwa, Amjad ne ya diro a gado ya ?aukeshi yana masa wasa yace “yarona yau aunty batakaika ka gaisheni ba why?" Nuna Safiyyah Amjad yayi ta kawar dakai tare da tsugunnawa tace “Ina kwana Dad" murmushi yayi yace “Lafiya lau Allah yayi albarka a tashi aje a karya zan fita me zan taho Miki dashi?"
Kawar dakai tayi jin ba maganar zatayi ba yasashi aje Amjad yace “Ok kin bani za?i kenan bye" ita gaba?aya ma wani takaici yake bata in yana wani abun, ya jima da fita sannan ta mi?e ta fito parlourn ta isa dinning ?in ta ha?a kunun gya?a da madara sai ?osai da yaji hanta da kwai ta zauna taci duk sonta da wannan cima yau kam bata iya cin ta kirki ba ta ture ta koma ?aki.
Da yamma kuwa sai gashi da uwar siyayyarsa ni?i? ya tura Nanny takai mata bata yarda Nanny ta gane wani abu ba ta kar?a ta ajiye tana fita tayima ?akinta key don dama Amjad ba gurinta yafiye kwana ba.
Tanaji bayan Isha ana ta?a ?ofar ta lafe a gado taki motsawa haka ya juya ya koma ?akinsa ya ?auki wayarsa ya kira layukanta duka a kashe yayi ?wafa ya lura ita da gaske fah takeyi dole yayi gaggawar yin abinda ya dace kafin ta ji?a masa aiki, washegari duk nacinsa na son ganinta d magana da ita ta?i yarda ta ?ule ?aki gashi bayason yin motsin da zaisa barorin gidan su gane abinda ke faruwa haka ya h?r ya ?yaleta, da yamma Dr Salima ta dawo lkcn baya gidan itama a ?aki ta samu Safiyyah a kwance ta kafawa selling idanu tana karanta wasi?ar jaki.
Har ta zauna a gefenta bata sani ba Saida ta ?ora hannunta a goshinta tace “Kodai kewar Kumbo ce ta sa?ali ruhinki har kika zurma haka kwana biyu?" Ajiyar zuciya tayi ta tashi zaune tace “Sannu da dawowa Mom ya hanya?" Numfasawa tayi tace “gajiya da ita Safiyyah ina ambassador ya tafi?" Gabanta ne ya fa?i tace “ni yau banma ganshi ba tun safe lkcn dana fito ya fice" jinjina kai tayi tace.
Ai na Turo masa number ?anin Kumbo dake Tawa a Niger don suyi magana dashi da?yar aka samu number a gurin matar Mal me Almajirai shi Mal ?in ya rasu" sosai Safiyyah ta kokawa mutuwar Mal me Almajirai tayi masa fatan dacewa da rahamar ubangiji sannan ta kar?i number da akace mata ansamo tasa a wayarta amma kiran duniya bata tafiya ta kalli Mom tace “Number bata tafiya" jinjina kai tayi tace “Hakane Nima na kikkira bata tafiya shiyasa na turowa ambassador in bata shiga ba aje Niger din a bincika andai ?an samu tudun dafawa"
Duk da damuwar da take ciki Saida ranta yayi haske ta kwantar da kanta jikin Dr Salima tana hawaye Dr tace “Gsky banason kuka inda wani abu gara ki fa?amin Safiyyah iyakar sanina bamu rage ki da komi ba to meye zaisa ki rin?a neman daukar damuwa ki ?orawa kanki"
Yanda ta hakikice tana fa?a sai ta ?ara Bama Safiyyah tausayi matar tana gwada mata ?auna amma idan mijinta bai janye ?udurinsa ba dole zasu ha?ura da juna zatabar musu gidansu don tana ganin barin gidan shi zaifi alkhairi da abinda zai faru a gaba tabbas maza basuda kara ko kunya akan duk abinda suka sanya a gabansu gara wata kunyar da wata.
Da?yar Dr ta samu taga Safiyyah ta saki ranta suka koma parlour tanayi mawa Dr tsifa Dr na bata labarin irin wada?ar da akayi a sunan tanata murmushi a haka ambassador yazo ya ishesu yana shigowa walwalar Safiyyah ta ?auke shikuwa ganinsu a wannan yanayin yasashi jin wani happy ya zubanta Idanu a kaikace ya zauna yace “Gimbiya kin dawo kenan?" Murmushi tayi tace “ka shiga busy da yawa nayita kiranka fah wayarka bata shiga" shafa kansa yayi yace “Wlh mun shiga meeting ne da shugaban ?asa akwai yuwuwar zan bar Faris zan koma Germany, ranki shi da?e babu kulawa ta Mom akeyi ko?" A kunyace tace “sannu da shigowa Dad"
Numfashi Dr Salima tayi tace “akwai abinda yake damun zuciyar Safiyyah nikam ta?i fa?amin" cire hularsa yayi ya sanya handkerchief ya share gumin dake cikin sumarsa yace “zata fa?a idan abin ya dameta"
Yana fa?in haka ya tashi yabar gurin tabisa da wani lalataccen kallo tare da ta?e baki ta saki gashin Dr Salima ta mi?e don tasan zai iya dawowa Dr tace “au haka zaki barni da kai rabi da rabi?" Murmushin ya?e tayi tace “Ki sallami Dad saimu ?arasa" bata jira amsa ba ta shige kofar da zata kaita ?akinta tana shiga taji wayarta na Ring ta ?auko ganin number Sakina tasata ?agawa suka gaisa Saknah tace “Ina cikin damuwa Mom Amjad" da mamaki tace wacce irin damuwa kuma?" Ajiyar zuciya tayi tace “Wata rasuwa akayi a fam na mijina Shine ranar Friday na tafi wlh yana garin amma bai yarda mun ha?u ba dana takurawa ha?uwarmu saboda Allah ya sani ina feel kasancewa dashi wai da naje nake nuna masa bu?atata sai cemin yayi shifa tunda ya rasa Fiyyah ya rasa feeling na duk wata ?a mace dake duniya....."
Dam gaban Safiyyah yabada wani irin sauti tace “wace haka?" Cikin raunin murya Saknah tace “Bansani ba Safiyyah nidai nasan ba auren soyayya mukayi da Maina ba to amma kuma banta?a samun labarin yata?a soyayya da wata mace ba bare ince ko ita yake nufi" Gwauron numfashi Safiyyah ta sauke tace “To ko aljana ta auri Mijinki ne?
[8/12, 9:25 PM] Am Oum Hairan: *_HM 45-46_*
_Littafi na na ku?ine sis kiyiwa Allah karki karanta in baki biya ba, 300 PC 700 view acct details 3184512451 first bank or 0255526235 Fauziyya Tasiu gtbank._
_Ko kati MTN ta WhatsApp number na 09013718241_
_?an Niger zaku tura kati Airtel na 500f ta waccan number dake sama_
Sake kwantar da murya Saknah tayi tace “Idan har hakane kuwa da aiki ja a gabana banason rayuwar nan da nakeyi Safiyyah nayi tunanin daga lokacin da akayimin aure komai zai wucce zan fara rayuwa me kyau me tsafta amma sai akasin haka, mijina da kansa yake cemin yasan inabin maza shi ba haushi zaiji ba don yasani dama duk abinda yayi zai iya maimaituwa akansa har ?ara bani dama yakeyi ta naje nayi rayuwata kawai yadda zanji da?inta na barsa da ciwon da yake damun ruhinsa"
Numfashi Safiyyah ta sauke tace “Ta? kina ruwa Allah ya kyauta nikam duniya da mutanen cikinta suna bani tsoro Saknah mazan da matan duka mun lalace kowa abinda yayi masa da?i yake aikatawa babu me yiwa wani tsawa Saknah kina cikin jarabawa amma tawa tafi taki idan mun ha?u gobe a school zamu tattauna wlh idan ina hasaso irin abinda ke tunkaroni gabana fa?uwa takeyi"
Sallama sukayi kowacce jikinta a mace Safiyyah ta zauna tana sa?awa da warwarewa ta ?an ji da?i tana tunanin kamar dawowar Dr Salima zaisa Ambassador Halil ya saurara mata amma maimakon haka sai ta fuskanci shi lamarinsa gaba ma yakeyi gashi Dr Salima ta koma aiki a sabon asibitin da ambassador ya bu?e mata anan Lagos idan ta fita takan kai dare sosai bata dawo ba wannan ya bama ambassador damar uzzurawa rayuwarta shi kenan a turo mata sa?onnin soyayya da manyan kyaututtuka.
Daren ranar da zata gama yankewa kanta hukunci Dr Salima ta tafi Maiduguri tun safe Safiyyah take aiki dake asabar ce baya gida wajen ?arfe uku ta gama soya kajin da aka kawo ta zuba a freegde tana gyara jan naman taji wayarta ta buga alamar shigar alert, share gumi tayi ta ?auki wayar ta duba wani firgici ya shigeta ganin alert na first bank manyan mikilai ne har Naira miliyan hu?u da rabi da sunan Halil Adam, bata gama rarrabe da gaskiyar abinda take gani ba sa?o ya shigo wayar ta bu?e jikinta na rawa ta fara karantawa kamar haka.
_“Cikin sirri batare da wadda kike tsoro ko wani da zata samu labari ta gurinsa ya sani ba Safiyyah naje na nemi dangin mahaifinki a ?asar Niger har mun gama magana game da aurenki gobe idan Allah ya kaimu za'a ?aura da misalin ?arfe biyu na rana, so sakamakon abin Sirri ne bazanyi Miki lefe ba shiyasa na yanke shawarar turo Miki wa?annan yan canjikan kila suyi Miki amfani sadakinki kuwa goben zan bayar......_
Cilli tayi da wu?ar hannunta ?irjinta naci gaba da bugawa kiransa ya shigo taki ?agawa ya kuma shigowa ta katse ta sa?i Amjad dake shigowa kitchen ?in ta nufi ?akinta hawaye nabin kuncinta ta kulle ?ofar tare da ?aukar akwati ta fara zuba kayanta Saida ta cikata taf da duk wani abu da tasan zata bu?ata sannan ta ha?awa Amjad nasa ta ?auki kayan ta fita tasa a motarta takuwa yi Sa'a babu me ganinta dake yamma ce duk yan aikin gidan kowa yanacan yana hutawa abinsa.
Ta juya kenan zata shiga ciki taji ana bu?e get ?in ta kalli gurin ganin motar Ambassador Halil yasata jin fa?uwar gabanta ta ?aru ta shige ciki tana shiga kuwa shima ya shigo har ?aki yabita tana latsa wayarta zaune kan gado yace “bakiga sa?ona bane?" ?agowa tayi masa wani ?an iskan kallo ta kawar dakai, sosai baya ?aunar wannan kallon da takeyi masa yace “kin gani kuma Kinga kirana?" Sai yanzu ta gyara zama tace “Na gani wani abu kakeso nace?"
Zuba mata idanu yayi ta cikin madubin dake idanunsa har kamar zaiyi mata magana yadai juya ya fice taja ?aramin tsaki tace “Kayi da wata badai Ni ba" tashi tayi ta zuge Glass na window ta le?a tana duba me shiga da fita can wajen biyar taga yana zuba huhun goro a bayan motarsa tayi murmushin takaici ta koma ta ?auki biro da takarda ta fara rubutu kamar haka.
_“Naso kasancewa da wannan ahli me ?umbin karamci da sanin darajar ?an'adam saidai kash..._ _Wata ?addara ta sawo kai me wuyar ?aukewa wacce zata zama sanadin barina cikinku don ?orewar kwanciyar hankalinku, bana fatan na zama silar yankewar farin cikin wanda ya sanya rayuwata farin ciki inason saka alkhairi da alkhairi bana fatan zamowa butulun da duniya zata taru tayiwa tofin Allah tsine._
_Mom inata zagaye Miki na kasa fitowa nayi Miki bayani a zahirance, ba komai ne yasani yanke hukuncin barin gidanku ba sai kasancewar_ _Mijinki ya za?i hakan, tun kwanaki masu dama da suka wucce ya bayyanamin yanason na amince masa muyi aure nace masa bazai ta?a yuwuwa ba, to na fahimci idan ban ?auki matakin matsawa daga gare ku ba abinda nakejin bazai yiwu ba zai yiwu domin Dad ya tabbatar min da gobe zaije Niger a ?aura masa aure dani gudun tabbatuwar wannan ?azamin kwa?o yasa nakeyi muku fatan alkhairi da fatan zamu sake ha?uwa a duniya._
Tana gama rubutawa ta ?auki system da wayarta da key na motarta ta sa?i ?anta ta fice ta shiga mota taja ta fice a gidan bayan ta shiga ?akin Dr Salima ta ajiye mata takardar.
Tayi tafiya me tsayi tsakaninta da unguwar sannan tayi parking ta ?auki wayarta.
Ta kira number Saknah bugu biyu ta ?aga Safiyyah tace “kina ina yanzu haka?" Cikin mayen bacci tace “Ina Astanght hotel" ajiye wayar tayi tana ?wafa kiran Saknah ya shigo ta ?aga Saknah tace kamar bakya cikin nutsuwa meye yake faruwa?" Numfashi ta sauke tace nawa ne kudin kama ?aki anan Astanght ?in?" Murmushi Saknah tayi tace “Meye yayi Miki zafi da kama Hotel?" Katseta tayi da cewa “Ba wannan ba kawai koma mene inason ganinki yanzu" kwatanta mata tayi ta nufi Victoria Island ?in tayi horn a get ?in suka bata past ta kar?a ta shiga Saknah ta tareta tare da rungumeta ta kar?i Amjad ta zubawa yaron Idanu gabanta na fa?uwa tace “Yaron nan bansan meye yasa duk sanda na kalleshi sai gabana ya fa?i ba" itadai Safiyyah bata kulata bata nufi hanyar da taga ta ?ullo Saknah ta aje Amjad ta cire doguwar rigar jikinta ya rage daga ita sai rigar bacci tace.
“Dama naji a raina saikin baro gidan Ambassador Halil Adam saidai naga gangancinki ki samu dama a hannunki ki bari ta kufce nifa Banga dalilin da zaisa ki hanawa kanki luntsuma cikin wannan daular ba saboda kawai tunanin wata mace da ?ila da itane ta samu damar da tuni ba mgnr da ake yi kenan ba....."
?aga mata hannu tayi cikin hassala tace “Ya isa Saknah ai komai lalacewar ?an halak ya kyautu ya nuna halacci wlh indai ina cikin hayyacina bazan bari wannan abin kunyar ya faru ba kawai abinda naji a raina rabona ne ya rantse a jikinsa shiyasa har yaji zai aureni ya turomin milikain Nairori don hidimar aure nikuma na baro masa gidansa yayi da wata"
Jinjina kai Saknah tayi tare da yarfe hannu tace “yanda kikaga dama amma na tausayawa rashin saarki wlh any way yanzu meye abinyi?" Murmushi Safiyyah tayi tace “Mafaka nake nema har sai sun gaji ko nace ya gaji da nema na sannan zanci gaba da rayuwa babbar damuwata Yanda zan ?acewa ganinsu shin ko