Showing 9001 words to 12000 words out of 47397 words

Chapter 4 - MEENALYN DADDY Complete Book By Fadila Sani Bakori.txt

06 Jan 2025

2937

kanta tana tunanin yadda zasu kwana agidan suci abinci ,ganin sauran shashinan da suka baro kaca-kaca ,ga kwanonin cin abinci nan ko ina anbaza atsakar gidan.Hakan yasa mommyn meenal taji dad'in ganin inda aka saukesu saboda can fes yake babu alamun katsanta,daga gani dai matar shashin mai tsabta ce.






Zuk'unne suka sameta tana alwallah.Cikin fara'a ta tari mommyn Meenal ta ce"Barkan ku da zuwa hajiya".Ta fad'i maganar tana mai amsar jakar hannun hajiya Mariya,tayi musu iso izuwa cikin d'akinta".






d'akine guda d'aya kamar yadda dai kukasan d'akin kyauye,sai gadaje guda biyu na k'arfe ,angyaresu tsab,d'akin irin babban d'akin nan ne watacce.Maryama tabarma ta d'akko ta shimfid'amusu tana mai cewa"Barkan ku da zuwa hajiya ku zauna".Mommyn Meenal zama tayi tana mai cewa"Yauwa sanninku ,mun sameku lafiya".Nan dai suka gaisa sosai kamar sunsan juna,inda Meenal ko kallo mata bata isheta ba,ita kuma da fara'arta ta ce"Sanninku da zuwa"."Yauwa ".Meenal tace can cikin mok'oshi.Ruwa mai sanyi na randa ta kawo musu .Dama koda Sarki ya aikomata da tayi abinci yayi bak'i da take tana saida taliya 'yar murza ita ta d'ora musu tai musu jaloup d'inta.Bayan ta aje ruwan taliyar ta kawomusu sannan ta basu waje ta tafi d'akin yara ta tada sallar acan".Hajiya Mariya da ke son taliyar hausa cigaba da cin abinta tayi ta kalli Meenal ta ce"Meenalyn daddy kinga ni ko'ina fes matar na da tsabta sosai kici kinji".Meenal fuska ta ya mutsa ta ce"Mommy nifa bazan iya cin abincin nan ba,kika sani kodan an aikomata ne anyi bak'i ta gyara gidan,sannan duk "yan kyauye k'azamai ne,masu girki da ruwan kogi,nikam bazan iya ciba, keda za ki'iya kici".Mommyn meenal kallan Meenal tayi ta ce"Meenal kenan,nan ai bawani shahararran kyauye bane,bikiga sunada da tuk'atuk'a ba da wutar Nepa?"."Uhm".Meenal ta ce. Hajiya Mariya haka taci taliyarta ta k'oshi Meenal ko tak'i'ci.Hajiya Mariya na gamaci ta d'auki buta tayi alwallah tayi sallah,Meenal ma tashi tayi tayi alwallar ta tada sallar itama.Bayan duk sun idar ne Maryama wato mai shashin tazo ta zauna ,tana mai kara musu sannu da zuwa,ganin abincin da takawo musu sunci kad'an ta ce"Hajiya abincin beyi dad'i ba ko naga kunci kad'an".Murmushi Hajiya Mariya tayi ta ce"A'a wallahi da yake ni inama son taliyar hausa naci sosai,Meenal ce bataci ba"."Ayyah tom ko fura za'a samo mata ne?".Hajiya Mariya tasan Meenal na son fura sosai,amma ganin sunan taraina musu wayau hakan yasa ta ce"A'a batajin yunwa ne aniima zataci".
Haka dai su kaita fira sama_sama ,har almuru ya gabato ,Maryama tashi tayi ta d'ora tuwan dare,tanayi suna hira da Hajiya Mariya.Kub'ewa Maryama ta d'akko zata yanka hajiya Mariya ta amsa ta yanka mata duk da tak'i hajiya Mariya ta nuna dole sai ta yanka hakan yasa ta bata.Ana sallar magriba ta tuk'a tuwan dawarta ta d'ora miyar, dama sarki ya aiko da zakaru biyu da yasa aka yanka yace ajuye su duka amiyar,da yake Maryama akwai iya girki da sarrafa girki hakan yasa ta raba uku tasa Kashi d'aya amiyar, Kashi biyu kuma ta yi musu farfesu da shi,aiko take b'angaran yahau k'amshi ,Meenal da bajuriyar yunwa gareta ba,take yunwa ta sata baccin dole.Hajiya Mariya bayan ta'idar da sallar magriba ne ta tadata akan tayi sallah,Meenal sosai tayi mamakin k'amshin da takeji azuciyarta sosai ta yaba da k'amshin dake tashi agidan,haka dai tayi sallah ta idar ta tashi ta tada sallar issha'i da ake kira.Itama hajiya Mariya sallar ta tashi tayi,dama maryama ta kawo musu tuwan ta aje musu harma da ruwan sha ,suna idar da sallah aka kawo Nepa ta haske wajan .Hajiya Mariya tana idarwa ta fara cin tuwanta dan tana marmarin tuwan dawa sosai,kallan Meenal tayi dake zaune tana kallanta, dagani kuma yunwa takeji,hajiya Mariya dai banza tayi da ita taci gaba da cin tuwanta dan sosai tuwan yayi mata dad'i.Meenal kallan hajiya Mariya tayi ta ce"Mommy kamar tuwan honey Well ko?"Hajiya Mariya Dan Meenal taci dan tasan indai tace mata irin tuwan da in sukaje Kano wajan Yayarta takeyine bazataci ba yasa ta ce"Eh Meenal shine".
Meenal kallan Mahaifiyarta tayi ta ce"Mommy Allah yana kama da tuwan da kike cewa Mommyn Aisha taimiki in munje Kano".Dariya hajiya Mariya tayi ta ce"Tom kici kiji mana". Meenal hannu tasa tana turo baki kamar anmata dole taci.Loma d'aya taci tayaba da dad'in girkin kuma dama gaskiya ta yaba da tsabtar matar sosai.Sosai tuwan yayi ma Meenal dad'i dan har da cewa"Mommy da kad'an kika fita iya tuwo".Hajiya Mariya dai batace komai ba,murmushi tayi ta ce"Kin ma fad'i gaskiya.






.Haka su hajiya Mariya da Meenal suka ci tuwansu sosai dan sun yaba da dad'in tuwan.Bayan sun gama ci ne nan Maryama ta dawo ta nuna musu inda zasu kwanta ,itama tai musu sai da safe taja musu k'ofar ta fita"








B'angaran su Alhaji ko suma bayan sun gamacin tuwan sun dad'e suna santin shi.Sarki d'akin d'an juma ya kai Alhaji Abba ya ce ya kwanta su kuma zasu kwanta shi da Alhaji tare .








Da daddare Alhaji wato kakan Meenal ya ce"Malam Haruna wato zan iya cewa tafiyar nan tamu gaisuwa ce da rok'on iri mu kai,wato Amina yarinyar wajan Sani,jikata kenan wadda kagani d'azu, Wallahi malam yarinyar nan in ra'ayine in ma ciwo ne dai tom ta gado wajan mahaifinta,in bazaka manta ba na dad'e ina amsar addu'a awajanka ina ba Sani dan hankalin shi ya juyo akan maganar aure,tom itama yarinyar nan da kagani Amina haka take kaganta dai babu maganar aure akanta,tom duk da mu acan Amina ba wata babba bace wadda za'aima surutu dan ba tai aure ba,amma ni gaskiya awajena tuni ta isa aure inda bamu manta al'adar iyayan mu ba,da kuma koyarwa ta addinin musulinci,tom shine fa na had'o abin biyu mu sada ziminci kuma aima Amina addu'a itama kamar yadda akaima Mahaifinta kafin ya auri mahaifiyarta".Shiru sarki yayi ,ya ce"Tom Malam garama ku can sai ace birnine babu mai maka surutu,amma bari kaga zuwa gobe zaka Abdurrahaman ,wato d'an juma kenan,Wallahi Alhaji kaikanka zaka fad'a ko acan birni yaci afara mai surutun rashin aure bare kuma munan kyauye ,da sa'annin shi sun manta da sunyi aure dan da akwai wanda ya aurar da 'Ya ma,amma shifa har yanzu babu maganar auran akan shi,nayi addu'ar nayi na kuma,tom har yanzu dai Allah bai kawo lokacin ba,Yanzu haka maganar da nakema mahaifin shi sama_sama yake mai magana saboda rashin aure".Shiru sarki yayi sannan ya ce"Yau she zaku kuma ne?,sai mu fara addu'ar zuwa gobe".Eh tom gobe gaskiya mukasa zamu koma,amma idan ba zai yuwuba sai mu k'ara kwana ai".Shiru sarki yayi sannan ya ce"Gaskiya idan sansamu ne ita Aminar abarta anan koda kwana goma ne mugani ".Tom shikenan ai ba damuwa,nima ina nan inda hakane shi Sanin sai su tafi shida Mariya,mu kuma mu zauna nida Aminar"
Haka dai su kaita firar su ta yaushe gamo har bacci ya kwashe su".






Washe gari,Alhaji Abba bayan sun gaisa da Alhaji ne yake sanar da shi sai dai shida hajiya Mariya su tafi,shida Meenal kuma sunanan har agama ma Meenal addu'ar nan da kwana goma".Alhaji Abba rasa abinda zai ce yayi dan yasan da akwai daru wajan Meenal sosai,amma babu damar yayi ma mahaifin shi gaddama hakan yasa ya ce"Tom shikenan,Alhaji idan hakane ni yanzu zan wuce dama ina da meeting yau".Alhaji Abba na fad'in haka ya tashi yayi musu sallama ya ce"Tom ni zan wuce idan munyi waya naji ranar da zaku dawo".Alhaji Abba na kaiwa haka yayi musu sallama ya tafi,dan Sarki na cewa ya tsaya ko karyawa mana yayi ,ya ce"Wallahi yanzu haka ana jirana ne".
Alhaji Abba haka ya tafi baima Meenal da Mommynta Sallama ba ,dan yasan indai Meenal taji zata zauna za'asha daru ,bazata yadda ya tafi yabarta ba,hakan yasa ya tafi bai musu sallama ba......✍️






Meenalyn daddy yanzu zamu shiga cikin labarin Sister,bini ahankali🚶‍♀️🚶‍♀️🚶‍♀️.




Share & Comment plz






📚 MEENALYN DADDY📚
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa}_
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo

*⚜️©J.A.W📚🖌️*




Na
Fadila Sani Bakori.






Page 9 & 10








Alhaji Abba sai da ya shiga cikin garin Kaduna sannan ya Kira Airtel d'in Mommyn Meenal dan yaji ance basu da network d'in M.T.N,Hajiya Mariya zaune take tana karyawa da kunu da k'osan da Maryama ta kawo musu .Meenal ko da ma ko agida ba shan kunu take ba.Hajiya Mariya na cikin shan kununta Kiran Alhaji Abba ya shigo wayarta,d'auka tayi tana mai kangawa a kunnanta .Bayan hajiya Mariya sun gaisa da daddyn Meenal ne yake sanar da ita ya tafi.Hajiya Mariya cikin mamaki ta ce"Daddyn Meenal ka tafi kuma kamar ya,mu fa?".Meenal da mamaki take kallan mommynta.Amsar wayar tayi daga hannun mommynta ta kanga akunnanta ta ce"Daddy kana ina?".Alhaji Abba cikin lallami ya fara magana,kamar haka"Meenalyn daddy meeting gareni 8:00 AM ,shi yasa banzo mu kayi sallama ba ina saur..."Meenal katse daddynta ta yi da cewa"Daddy wai kamar ya bangane ba,mu fa sai yaushe zamu tafi?".Alhaji Abba cikin lallami ya ce "Meenalyna ki yi hak'uri kinji ,Alhaji ya ce dole keda mommynki zaku zauna ku dawo tare,nan da sati mai zuw....".Ai Meenal bata gamajiba,ta yi wurgi da wayar ta fasa kuka.Maryama dake waje da saurinta har tana tuntub'e ta shigo d'akin tana tambayar lafiya.






Meenal kuka take tsakaninta da Allah ita tafiya za tai.Maryama cikin damuwa ta kalli hajiya Mariya da bata tankama Meenal ba tsabar haushi ta ce"Hajiya lafiya bata da lafiya ne?"."Wai daddynta ya tafi bai mata sallama ba,sai kace wata k'aramar yarinya".
Mariyama dai mamaki ya kamata ,amma sai ta aje mamakinta ta kalli meenal ta ce"Ki yi hak'uri kinji kar kanki yayi ciwo ".Haka dai Maryama tai ta ba Meenal baki har sai da taga tayi shiru sannan ta rabu da ita.




Hajiya Mariya kallan Maryama tayi ta ce"Dan Allah ko akwai yaro kusa in bashi ya amso ma ta kayan tea,da yake ita bata shan kunu ko agida".
Sallamar d'an juma da Maryama wato mahaifiyar shi taji ne yasa ta ce"Yauwa bari ga yayansu nan ya amso mata".






D'an juma cikin na tsuwar shi yayi sallama ya shiga,wani irin yarrrr yaji lokacin da idanun shi su kai mai tozali da Meenal da ke zaune ana bata hak'uri har yanzu dai tana shasshek'ar kukan.D'an juma cikin zuciyar shi ya ce"Ko sune bak'in da jiya sarki yace min anyi,amma kuwa wa In can kamar maza ne inda shi ya kirani yace min in samu d'akin kwana bak'i zasu kwana a d'akina".
Maryama wato Mahaifiyar d'an juma kallan d'an juma tayi ta ce"Yauwa dan Allah kawomana kayan tea".D'an juma kai ya siddar cikin sanyin muryar shi ya gaida hajiya Mariya sannan ya fita.Dai-dai k'ofar da zata sadashi da wajene yasake wai gowa,aiko take idon shi ya fad'a ana Meenal.Meenal da dama ta tsani kallo ta gallamai harara,aiko sai a idon Momnynta.






Hajiya Mariya kallan Maryama tayi ta ce"Shine babban d'anki ko?".Kai Marayama ta duk'ar tana murmushi irin kunyar d'an farin nan.Meenal ko azuciyarta hattace kai wannan bai kama da d'an kyauyan nan ba,amma jin alamun d'an matar ne ma,sai ta ce"Koda yake ko yadda yake kallan muta ne ma yasa ka shaida d'an kyauye ne".






Mahaifiyar d'an juma kuma fita tayi ta ce"Bari a'a za ruwan shayin".Bayan mahaifiyar d'an juma ta fitane ,Mommyn Meenal ta kalli Meenal ta ce"Meenal ina miki magana amma bakyaji ko,ke ala dole sai kinyi abinda za'asan baki da tarbiya ko,yanzu wannan da kika harara tsaranki ne?".Meenal turo baki tayi ta ce"Mommy bikiga yadda yake kallona ba,nifa na tsani kallo Wallahi".mommyn meenal dai na siha irin wadda ta sabayi ma meenal ce tayi mata.






Abin mamaki d'an juma sai fara jin shi wani iri ga wata irin fad'uwar gaba da kasalar zuciya ta samai , tunda yayi tozali da bak'uwar nan tasu.Abu kamar wasa koda yaje shagon manta abinda zai d'auka yayi sai da ya Kira Mahaifiyar shi awaya sannan ta tuna mai,ya aiki yaro ya kai.Shi kuma ya zauna yayi shiru,daga ya rufe ido sai yaga fuskar yarinyar yake gani,bai kawo komai aran shi ba sai cewa yayi tsabar kyan yarinyar ne yasa take min gizo a Ido.






Can cikin gidan kuma lokacin da Yaron ya kai kayan tea d'in lokacin ruwan zafin da Mahaifiyar d'an juma tasa har yayi zafi.D'iba tayi a kofi mai kyau ta kaima Meenal.Hajiya Mariya amsa tayi ta had'ama Meenal tea d'in ta bata.Meenal tana turo baki kamar yadda ta saba in ranta na ab'ace ta ce"Mommy na k'oshi".Hajiya Mariya babu yadda batayi da itaba tak'i.Hajiya Mariya d'aukar tea d'in tayi ta kaima mahaifiyar d'an juma da ke waje tana wanke kwanonin da ta b'ata.






Hajiya Mariya zama tayi gefan Maryama ,ta ce"Kin ga 'yar gidan na ki tak'i sha".Mahaifiyar d'an juma amsa tayi ta ce"Tom ko wani abun take so ta fad'a kafin yayansu ya tafi insa shi ya kawo mata"."Ki rabu da Meenal in taji yunwa da kanta zata naima bata da juriyar yunw..."Sallamar d'an juma ce tasa Mommyn meenal yin shiru.
D'an juma kallan Mahaifiyar shi yayi ya ce"Inna zan tafi ko akwai abinda kike buk'ata".Mahaifiyar d'an juma banza tayi da shi kamar bata ji abinda ya ce ba,ta ci gaba da wanke-wankenta.Shiru d'an juma yayi sannaya juya ya ce"Inna na tafi".yana fad'in haka ya tafi dan yasan ba amsa mai za tai ba.






Bayan d'an juma ya fita ne,Hajiya Mariya ta kalli Mahaifiyar d'an juma,ta ce"Auntyna idan laifi yayi ayi hak'uri dan Allah d'a zuma ina gani yana gaidaki baki amsa mai ba".Maihaifiyar d'an juma aje wanke-wanken da takeyi ta yi ,ta ce"Hajiya dole in fushi da shi ink'i amsa gaisuwar shi,na san ke kanki kallan mai mata kike mai,amma kin gan shi nan bashi da ranar auran ma,ke budurwar ma baida ita,an bashi yara da dama agarin nan yace baiso,tom ya yake so muyi,nan fa kyauye ne ba binni ba bare yace ,na tabbata ko a binni Namiji d'an shekara talatin da bakwai ya isa afara mai surutu bare kuma anan.Mahaifin shi yanzu haka fushi yake dani yace nina d'aure mai gindi,tom kwanannan k'anwar baban shi ta bashi 'ya itama yace bai so,tom taya bazanyi fushi da shi ba".Mahaifiyar d'an juma ta idasa maganar cikin alamun damuwa"






Hajiya Mariya kallan mahaifiyar d'an juma tayi ta ce"Eh gaskiya kam kallan mai mata nayi mai,duk da da darkoma banyi tunanin anan ya ke ba,amma abinda zaku duba aure lokaci ne,idan lokacin yazo zaiyi,duk kalar fushin da za ku yi da shi dole sai ranar da Allah ya nufa zaiyi auran zaiyi.Dan haka shawarar da zan baki nisiha zaki tayi mai ".Haka dai Mommyn meenal tai ta yima mahaifiyar d'an juma nasiha,da ankarar da ita komai lokaci ne"






D'an juma ko na fita gidan Sarki ya biya wato kakan shi kenan,zaune ya iske tsofaffin biyu sai hirar su suke.D'an juma zama yayi sannan ya gaida sarki da kuma kakan Meenal.Alhaji cikin fara'ar shi ya ce"Tun da na iso nakejin ana cewa d'an juma-d'an juma amma kuma d'an juma yayi wahalar gani".D'an juma dai murmushi yayi ,kuma dama shi mutum ne ba mai yawan magana ba .Sarki amshe zan can yayi da cewa"Ka gan shi nan girman banza ne babu mata,tom ko dai Kadunar zaka tafi da shi ka zab'ar mai matar aure acan inda yak'i na mahaifar shi".Dariya Alhaji yayi ya ce"Abdurrahaman zaka Kaduna ko in baka mata".Shi dai d'an juma murmushi kawai yayi.Sannan ya yi musu sallama ya tashi ya tafi,yana mai son sanin su waye su,dan shi dai bai tab'a jin ance suna da 'yan'uwa a Kaduna ba,amma kuma abisa ga dukkan alamu wannan sun saba da Sarki .






Sarki Kiran d'an juma yayi ya ce"Yauwa d'an juma zoka kaima Yarinyar nan addu'ar nan ta fara sha tun yau".Alhji wato kakan meenal ya ce"A'a indai Amina ce bazata shaba,yaje dai su taho tare in tsareta ta sha agabana" .






D'an juma fita yayi ya d'auki mashin d'in shi roba-roba ya nufi gidan su,yana zuwa ko ya iske Mahaifi yar shi ce kad'ai atsakar gidan .kusa da ita ya k'arasa ya ce"Inna Sarki ya aikoni inzo in tafi da yarinyar nan bak'in da akayi". Mahaifiyar d'an juma ba tare da ta amsa mai ba ta shiga d'akinta inda Meenal take da Mommynta, Meenal na kwance dan yunwa ta fara matsa mata.Mahaifiyar d'an juma kallan Mommyn Meenal tayi ta ce"Hajiya wai sarki ne ya aiko kiran Amina"."Tom shikenan d'an ai kyan na nan ai sai su tafi tare".Mommyn Meenal na fad'in haka ta fara bubbuga Meenal dake jin su ,ta ce"Meenalyn daddy ki tashi kije ana kiranki".Bud'ar bakin Meenal sai cewa tayi "Mommy ni bazani ba".Hajiya Mariya d'aure fuska tayi tana mai jin kunyar maganar da Meenal tayi,ta ce"Meenal ki tashi nace ko?".Meenal turo baki ta yi ta ce"Tom mommy ni mai zanyi dan Allah ni bazani ba" .Hajiya Mariya sosai taji kunya,haka yasa k'asa-k'asa yadda Mahaifiyar d'an juma bazataji ba ta ce"Wallahi kinji na rantse idan har biki tashi ba zan kira daddynki in ce mai ba yanzu zamu koma ba,idan kina ganin wasa ne kar ki tashi ki tafi" .
Meenal tashi tayi tana zun b'uro baki tayi hanyar waje,dan ita bama ganin Wanda zai kaita tayi ba .Hajiya Mariya gyalan Meenal d'in ta wurga mata ta ce"Ga gyalanki nan".Meenal amsa tayi ta fita ba tare da ta yafa ba ,bak'ar abaya ce jikinta taji adon stone tayi mata kyau sosai dama kuma ita Meenal tafi ra'ayin dogayan riguna.






Tsaye yake da key d'in mashin d'in shi a hannu ,yayi adon shi ciki wani yadi mai kyau Masha Allah,Wanda ya dai wuce araina,dan d'an juma mutum ne mai son gayu gashi kuma shi dama hurd'ar shi tafi yawa a funtua.
Sosai ya k'osa tafito ya k'ara kallan kyakkyawar fuskarta.Meenal tsaye tayi tana kallan shi bisa ga alama shine zai kaita.D'an juma ko dama tun kafin ta k'araso ya k'ureta da ido dan ko kyaftawa ba yayi,tana zuwa kusa da shi yayi saurin kauda idon shi,Meenal tsaki tayi dan ta tsani kallo,ja tai ta tsaya ,batare da ta tanka mishi ba,shima kuma sai ya kasa mata magana.Mahaifiyar d'an juma ce ta ce"Yayan su kuje mana gata nan ta fito" .Meenal tsaki tayi tai gaba yana binta abaya.Aiko suna fitowa 'yan gidan kowa idan shi akan Meenal

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login