Showing 3001 words to 6000 words out of 47397 words

Chapter 2 - MEENALYN DADDY Complete Book By Fadila Sani Bakori.txt

06 Jan 2025

2932

daga yau karki kuma yadda ki zama sanadin kukan Meenal,idan bahaka ba zamu samu sab'ani tsakanina da ke!".
Hajiya Mariya tashi tayi ta zauna tana kallan Alhaji Abba,sannan cikin nuna fushinta ta ce.
"Daddyn Meenal naji insha Allah daga yau bazan sake yi ma Meeenal maganar da ta danganci aure ba kamar yadda kace insha Allah,amma maganar Meenal ta tayani aiki agidan nan bazan tab'a janyewa ba,dole Meenal tayi aiki agidan nan".Hajiya Mariya ta'idasa maganar cikin b'acin rai.
Alhaji Abba tashi yayi zai fita,har ya kai bakin k'ofar da zata sata shi da falo ya juyo yana kallan hajiya Mariya ya ce.
"Wallahi kinji na rantse indai tai makon aiki kike so sai dai ki samu 'yar aiki,amma ba dai Meenal ba".Alhaji Abba na kai haka ya ja k'ofar hajiya Mariya da k'arfi ya fita"






Hajiya Mariya ta dad'e konce tana juyi tana tunanin ta yadda zata b'ulloma lamarin nasu,dan awannan karan ta d'auki aniyar yak'i da Meenal da daddynta.Washe gari mahaifiyar meenal haka ta tashi da wuri kamar yadda ta saba tashi ta shirya musu abin breakfast,tana nan zaune Alhaji Abba ya fito dan yau k'in shiga part d'in shi tayi dan ya san fushin da gaske take yi da shi.Alhaji Abba ko da fara'ar shi ya k'araso inda hajiya Mariya take,yana cewa"Wato yau dan ana fushi dani shine aka k'i tadani ko?".Murmushi Mommy Meenal tayi tana mai cewa"A'a daddyn meenal nikam bana fushi dake makara nayi nima".




Alhaji Abba zama yayi yana mai cewa"Ina meenalyn daddy fa?".
"Kasan indai ba Exam gareta ba sai an tadata ".
Alhaji Abba tashi yayi ya nufi bedroom d'in Meenal,lokacin da Alhaji Abba ya shiga kwance ya sameta sai sharar baccinta take.Ahankali Alhaji Abba ya fara bubbuga Meenal yana kiran sunanta.
meenal bud'e idonta tayi tana mai sakin murmushi wa daddyn nata.
Alhaji Abba kallan Meenal yayi ya ce"Meenalyn daddy tashi ki yi wanka ki yi breakfast ".meenal tashi tayi batare da ta tanka ba tana mai shigewa toilet .
Alhaji Abba ganin meenal ta tashi ,shima fita yayi"






Meenal cikin sauri ta shirya ta fita dan ta kusa late.Zaune ta iske daddynta na jiranta,tana zuwa sauri-sauri suka yi breakfast d'in ,dan dukkan su sunyi late"




Alhaji Abba kamar yadda ya saba sai da ya kai meenal cikin makarantar su sannan ya tafi private hospital d'in da yake aiki .
Hajiya Mariya ko ita ma kusan tare suka fita,dan tana son ta fara biyawa gidan kakannin meenal kafin ta shiga school d'in da take teaching"






Hajiya Mariya zaune gaban Alhaji Abdullahi ,wato kakan meenal kenan,mahaifin Alhaji Abba .
kakan Meenal da kallo d'aya za kai mai kasan datijon ya kwana biyu dan kanshi gaba d'aya farin gashi ne,sai dai da k'arfin shi sosai.
Alhaji Abdullahi ,wansa yawancin mutane da kuma sukansu suke Kira da Alhaji,da fara'arshi ya tari hajiya Mariya wato mahaifiyar meenal ,yana cewa" Mariya tunda naganki da wuri haka nasan ba gaidani akazo yi ba "Hajiya Mariya dariya tayi,ta ce"Ina kwana Alhaji,ya k'arfin jikin" "Jiki alhamdulillah"cewar kakan meenal.
Hajiya Mariya k'ara gyara zama tayi sannan ta ce"Alhaji dama wallahi akan meenal ne,kamar yadda dai kasani bani da iko akan meenal,ban'isa insata ba ban'isa in hanata ba,tom har yanzu ahaka muke.Wato abinda kedamuna meenal banda cin abinci da wankanta babu abinda ta'iya,akoda yau she ina nuna ma mahaifinta ita macece gidan wani zata,amma wallahi ita da daddynta duk ranar da na furta haka ma sai munyi ba dad'i,shine nazo nasan kai in kayi mai magana zaiji kace mai dole meenal ta rik'a tayani aikin gida ko asamu ta iya wani abun daga cikin aikin gida"Shiru hajiya Mariya ta yi ta d'an numfasa sannan ta ce"Tom Alhaji wannan ita ce buk'atata dan Allah".






Kakan meenal tashi ya yi daga shingid'an da yake ya ce"Wai Mariya kina nufin Amina bata iya komai ba na aikin ku mata?"."Wallahi Alhaji bata iya komai ba,shara wanan, Allah tunda meenal ta isa hankakinta banta b'a ganin tayita ba da idona ba,tun abin baya damuna nikam yanzu har yafara damuna".
"To shi Sani in banda abin shi haka zai d'auki "'yar ya kaita gidan aure bata iya komai ba,tom ki barshi dani ,bari Sule yazo zansa ya kiramin shi".
Hajiya Mariya godiya ta yi ma sirikinnata sosai sannan ta tashi ta tafi"








Sule mai kula da Alhaji wato kakan Meenal yana zuwa Alhaji ya sashi ya kira mai Alhaji Abba awaya ya ce daga ya tashi aiki ya biyo Alhaji nason ganin shi".






Aiko haka akayi Alhaji Abba na tashi aiki ya je Kiran Mahaifinnasa, dama kuma dai kullum sai ya laik'a Mahaifinasa.Bayan sungaisa ne Mahaifin Meenal ya ce"Alhaji gani ance kana son ganina"
"Eh Sani ina son ganinka,d'azu Mariya tazo nan ta kawomin k'ararka kai da Meenal,taya zaka ce Meenal bazata rik'ataya Mahaifiyarta aiki ba,bakasan tana da hak'i akanta ba ne?,dan haka karka kuskura kajama yarinyarka fushin Allah,karik'a barinta tanayin aiki,kamar yadda mahaifiyarta tace ita macece nan gaba gidan wani zata,dan haka daga yau duk wani aiki su rik'ayi tare,idan ma ta kama ta hak'ura da makaratun ne tom ta hakura ta zauna ta taya Mahaifiyarta aiki, itama ta iya".
Mahaifin Meenal wato Alhaji Abba kallan Mahaifin nasa yayi ya ce"Alhaji meenal fa yarinya ce ,taya za'ace ta had'a karatu da aiki,bazata juri aiki irin wannan ba,inda ba sabawa tayiba.Sannan tunda Mariya tayi min maganar zata takatar da masuyi mata aiki nahanata,gudin haka,amma saboda wata hujja tata ta banza da ta tsiro da ita tak'iji ,shine yanzu aiki yayi mata yawa zata d'orama Meenal".
kakan Meenal da tunda Abban meenal ya fara magana yake kallan shi,har ya kai k'arshe,cikin sanyin shi,dan shi ko fad'a zaiyi cikin sanyi yake abinsa,ya ce"Sani dole meenal ta yi aikin gida kamar yadda mahaifiyarta ta buk'ata ,zaka iya tafiya".
Alhaji Abba ya dad'e bai iya k'ara cewa komai ba sannan yayi k'arfin halin cewa"Shikenan Alhaji zatayi,zan tafi babu abinda kake buk'ata?"."Babu Allah yayi maka albarka "cewar Alhaji wato kakan Meenal"




"Ameen"Mahaifin Meenal ya ce ya tafi.




Sosai ran alhaji Abba ya b'ace da abinda hajiya Mariya ta yi mai,yana shiga gida hajiya Mariya ta lura da yanayin shi tasan Alhaji ya fad'a mishi,dama kuma tunda taji shi shiru ta yi tunanin hakan.
Meenal ko da ke zaune tana aikin buga game awayarta ,aje wayar tayi tana mai yin welcoming din daddynta.Alhaji Abba hannun meenal ya kama suka zauna.
Hajiya Mariya cikin sanyi ta ce"Barka da dawowa daddyn meenal""Uhm"Alhaji Abba ya iya ce mata kawai.
Meenal ma ganin haka tasan yau an tab'a daddynta hakan yasa cikin sanyi ta ce." Daddyna waya b'atama rai?".Meenal tayi maganar tana kamo fuskar shi abin gunnin mamaki.
Alhaji Abba Mahaifiyar meenal ya nuna ma meenal ya ce"Kin ganta meenalyn daddy bata son farincikina".Meenal cikin sanyi ta ce"Daddy mai tayi ma?".Alhaji Abba murmushin takaici yayi sannan ya ce"Meenal ta had'ani da Alhaji wai sai dai ki rik'a tayata aiki"."Wallahi daddy bazanyi b...".Alhaji Abba saurin rufe bakin meenal yayi dan karta idasa fad'in abinda take cewa,ya ce" Yi hak'uri Meenalyn daddy karki rantse kinji,ki yi hakuri kina kallon yadda take aikin,ahakama zaki iya,basai kin amsa kinyi ba ".Meenal kuka tasa tana cewa"Daddy inje school in dawo inyi aiki Allah bazan iya ba ni kam bazanyi ba". Alhaji Abba hannun meenal ya kamo ya shigar da ita side d'in sa ,cikin falonsa suka zauna ,cikin lalla shi ya ce"Meenalyn daddy tausayin daddynki zakiji ki yi badan Mommynki ba,kinga Alhaji zai iya fushi dani".Bud'ar bakin meenal sai cewa ta yi"Yo daddy ya dad'e bai yi ba,ba shi ya sani b..." .Alhaji Abba rufe bakin meenal ya yi ya ce"Meenalyn daddy Mahaifina ne fa,ni dai dan Allah ki tai maka kirik'a ganin yadda ake girkin zanma rik'a biyanki ba kyauta ba zaki yi".meenal dai turo baki ta yi bata ce komai ba,haka Alhaji Abba ya yi ta rok'on meenal daga k'arshe dai sai da ya yi kamar zaiyi kuka ta yadda,amma fa ta d'auki matakan yak'i da Mommynta dan acewarta bata sonta .Niko abin ta kaicima ya ke ban dan tab'arar tayi yawa"


.


Ranar dai abincin da Hajiya Mariya ta yi daga Alhaji Abba har meenal babu wanda ya kallai dan dukkan su fushi suke da ita.Tsaddan restaurant Daddyn Meenal ya kaisu sukaci abinci"




Washe gari takama Weekend ,hajiya Mariya da wuri taje ta tada Meenal,Meenal da ke kan duniyar bacci kallan Hajiya Mariya ta yi tana turo baki ta ce"Lafiya".",Tashi zakiyi muje kifara gani inda kice bazaki ba,naji ki kallama ya wadatar "cewar Mahaifiyar meenal. Meenal turo baki tayi tana k'unk'u nai ta ce" Tom kije ganinan zuwa"."Tashi zakiyi muje ".




Meenal sakkowa tayi tana mai bin bayan hajiya Mariya tana mai goge hawayan da ya fara zubar mata.




Hajiya Mariya cigaba tayi da gyaran falon da tafara ta tuna bata tada Meenal ba.Hajiya Mariya tanayi tana surutu ,kinga idan kika fara share duster d'in sanna sai ki share ki goge,duk abinda hajiya Mariya za ta yi tanayi tana magana,irin dai na masu koyama mutum abu.Meenal ko kallanta kawai take da na goge hawayan da ke zubar mata akai-akai. suna gamawa hajiya Mariya ta kalli meenal da yanzu tabar kukan sai dai baki da ta turo ta ce"Yauwa Meenalyn daddy ba gashi har mun gamaba,yanzu saura mana mu had'a breakfast".




Nan ma dai haka meenal ta bi Mommynta tana turo baki,ahaka dai suka dama kunun gyad'ar da suka dama ,ana cikin dama kunun ne Alhaji Abba ya shigo kitchen d'in,cikin fad'ad'a murmushin shi ya ce"Sannu da k'ok'ari meenalyn daddy".meenal turo baki tayi bata tanka ba.
Hajiya Mariya kallan Alhaji Abba tayi ta ce"Barka da safiya daddyn meenal".
maimakon alhaji Abba ya amsa hannun meenal ya kamo ya ce"Tom aikin ya isa haka muje ki huta".




Meenal hannun daddynta ta rik'e suka tafi suka bar Hajiya Mariya nan ,hajiya Mariya da kallo kawai da bisu taci gaba da aikinta.Alhaji Abba kallan Meenal yayi ya ce"Jeki shirya meenalyna mu je muyi breakfast bama k'aracin abincinta sai dai taci ita kad'ai ki rabu da ita karma ki k'ara b'ata ranki ko kiyi kuka ".Meenal kallan daddynta ta yi tana goge hawayan jin dad'in son da daddynnata ke mata ta ce"Daddy me yasa mommy da tafi sona yanzu ta ke min haka ne?".Alhaji Abba goge ma meenal hawayan da ke zubar mata ya yi ya ce"Ki yi hak'uri kinji meenalyna ni bagani ba kuma ina sonki,kibarni da ita zanyi maganinta kwanannan,maza kije ki shirya muje muyi breakfast".






Meenal cikin jin dad'in daddynta yace zaiyi maganin takurawar da Mommynta ke mata ta shirya da wuri.Haka suka zo suka wuce hajiya Mariya da ke zaune daga gani jiran fitowar su take suyi break tare,amma sai ta ga sun fita.






Alhaji Abba restaurant d'in jiya da ya kai Meenal su kai breakfast,can ya kaita yau ma,sai da suka yi breakfast d'insu sannan suka koma gida "






BAYAN SATI D'AYA.
Gaba d'aya satin nan haka hajiya Mariya ta yi shi duk ba dad'i dan tagaji da fushin da Meenal da daddynta su ke yi da ita,gashi aikin ma Meenal ba wai yi take ba sai dai tai mata tsaye akai dan ita bata ce tanama fahimtar abinda take koya mata ba.
Fushin da Daddyn meenal ya ke yi da hajiya Mariya sosai abin ya fara damunta hakan yasa yau da daddare bayan meenal sun rabu da daddynta ta kwanta ,hajiya Mariya ta turo d'akin Meenal d'in ta shiga,kamar ko yadda ta zata zaune ta iske Meenal d'in tana game awayarta.
Meenal najin sallamar hajiya Mariya ,kamar bazata amsa ba ,sai kuma ta amsa ciki-ciki,amma ko tad'aga kai ta kalleta.
Hajiya Mariya amshe wayar hannun Meenal ta yi.meenal turo baki tayi sannan ta juya zata kwanta,hajiya Mariya da sauri ta rik'o Meenal tana cewa"Haba meenaly daddy da mommynki kike fushi?,dan nace ki koyi aikin gida ne kike fushi dani keda Abbanki ko,tom indai hakane kisha zamanki daga yau ni kad'ai zan rik'a aikina shikenan ko ?".
Meenal turo baki tayi ta ce"Tom ba ke bace yanzu kin canza".Murmushi hajiya Mariya tayi ta ce"Meenal ba canzawa nayi ba bakudai fahimtan bane keda daddynki shi yasa"."Ni kam Mommy indai kina son mushirya sai dai ki dawo kamar da ".Shiru hajiya Mariya ta yi sannan ta ce"Tom meenalyna na daina ,mun shirya ko?".Meenal rungume hajiya Mariya ta yi ta ce"Yauwa mommyna har naji dad'i".
Murmushi hajiya Mariya ta yi ,ta ce"Meenal kenan,ke kikasa daddynki ya yi fushi dani ko?"."A'a mommy Allah babu ruwana ".




Murmushi hajiya Mariya ta yi ta ce" Tom ki aje game d'in ki kwanta ki yi bacci".Hajiya Mariya nakaiwa haka ta tashi tajama ma Meenal k'ofa,ta nufi bedroom d'in Alhaji Abba,koda taje ya rufe k'ofar shi hakan yasa sai da ta bubbuga Alhaji Abba da har bacci ya fara d'aukar shi ya ce"Waye"yana sane yace haka dan yasan ba meenal ba ce.
Hajiya Mariya kamar karta tanka dan tasan yana sane da ita ce,amma sai ta daure ta ce"Daddyn Meenal ka bud'e ni ce" Alhaji Abba tashi yayi ya bud'e ,yana kallan hajiya Mariya kallan har yanzu fa ina fushi dake.Hajiya Mariya kutsawa tayi ta shiga .Alhaji Abba kallanta yayi ya ce"Zan kwanta ne lafiya?".Shiru Hajiya Mariya tayi sannan ta ce"Ka zauna mana,magana zamuyi"Alhaji Abba zama yayi ya ce"Inajinki?".
Hajiya Mariya cikin siririyar muryarta ta fara magana kamar haka"Yanzu daddyn meenal fushi kake dani dan nasa meenal aiki?,Shikenan insha Allah daga yau bazan kuma sata ba".Alhaji Abba cikin d'aga murya alamun yaji zafin abinda mommyn meenal ta yi ya ce"Eh Mommyn meenal fushi nake da ke kamar yadda kika ce,akan me na d'aukar miki masu aiki ki koresu kice ke sai dai meenal ce zata ta ya ki,tom da me zataji da karatun da takeyi koko da aikin gida zataji!?".Numfasawa mommyn Meenal tayi sannan ta ce"Shikenan daddyn meenal ai ya wuce dan Allah kayi hak'uri insha Allah hakama ba zai sake faruwa ba duk yadda kace haka za'ai".Murmushi Alhaji Abba yayi ya ce"Yauwa,bawai bana son Meenal ta tayaki aiki bane,a'a nafi son sai ta gama karatunta kar abin yayi mata yawa".Dariya hajiya Mariya tayi ta ce"Tace tom ai shikena,ni kunsa duk na rame kai fushi meenal fushi.Memakon ko kaine kaji tausaina,amma kaziga 'yarka kuka had'emin kai kuka sani gaba,tom nadai janye".
Dariya sosai Alhaji Abba yayi ya ce "Yauwa mommyn meenalyna koke fa,amma nima fa naga kamar kinrane da gaske ,kamarma hadda k'ashin wuya mugani" Alhaji Abba ya idasa maganar yana jawo mommyn meenal.Hajiya Mariya buge mai hannu tayi ta ce"Ni rabu dani tashi zanyi in tafi "Hajiya Mariya ta fad'i maganar tana tashi zata tafi.Alhaji Abba jawota yayi ta fad'o kanshi ya ce"Ai inkinga kin fita nan tom kin ba Abban meenal gamsassan hak'uri dan Wanda kikaban yayi kad'an "Alhaji Abba na fad'in haka ya had'e bakin shi da na Hajiya Mariya..............โœ๏ธ








Yadda kike tunanin labarin ba haka yake ba sister bini ahankali๐Ÿ˜‡๐Ÿ˜‡๐Ÿ˜‡






kada ku manta da akwai banous da zan saki , masu Comment ne kad'ai zasu samai




Shere & Comment please






๐Ÿ“š MEENALYN DADDY ๐Ÿ“š
๐Ÿ””๐Ÿ“š
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION๐Ÿ“š*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa}_
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo

*โšœ๏ธยฉJ.A.W๐Ÿ“š๐Ÿ–Œ๏ธ*
NA
Fadila Sani Bakori.






Page 5&6.








Washe gari ,hajiya Mariya da wuri ta tashi kamar yadda ta saba tashi ta shirya komai ta d'ora musu abin breakfast.Lokacin da Meenal da daddynta suka tashi hajiya Mariya ta kammala komai kamar yadda ta saba.
Yau cikin fira da tsokana Meenal suka yi breakfast da daddynta da mommynta.Sosai hajiya Mariya taji dad'in hakan,amma satin nan gaba d'aya da suka daina cin abincinta firama suka bar zama suy da ita'dan hatta kallo Meenal a Falon daddynta take zuwa tayi.Bayan sun gama karyawa Alhaji Abba ya d'auki Meenal ya direta a school d'in da take karatu sannan shima ya tafi wajan aiki"






ASALIN LABARIN.
Alhaji Abba shine d'aya d'aya tilo wajan mahaifin shi,hakan yasa mahaifin alhaji Baba wato kakan meenal,ya ba Alhaji Abba gata sosai,alhaji Abba na matakin k'arshe na karatu Allah yayi ma mahaifiyar shi rasuwa.
Tunda Mahaifiyar Alhaji Abba ta rasu hankalin Alhaji wato kakan Meenal ya koma akan Alhaji Abba yayi aure, dan dama tun da ran mahaifiyar shi taso haka Allah bai yi ba. Babu maganar da Alhaji wato kakan meenal bayi ma Alhaji Abba ba akan aure amma yak'i,hakan yasa sai ya fara bincikin abokan shi ko sun sa budurwar shi amma abin mamaki sai suka sanar da shi bashi da budurwa,dan shi alakacin babu abinda yakeso kamar karatun shi,gani yake yin budurwa kamar b'ata lokaci ne,hakan yasa ya maida hankalin shi sosai akaratu,har ya kammala ya samu aiki,amma babu maganar aure aran shi.
Atak'aice dai Alhaji wato kakan meenal ya sha fama sosai kafin mahaifin meenal yazo mai da maganar auran mahaifiyar meenal itama lokacin ansha karatu.Cikin k'ank'anin lokaci aka tsaidar auran su akayi,za'a'iya Kiran auran da auran tazurai.Mahaifin meenal ana d'aura auran shi da hajiya Mariya bai yadda ya kusanceta ba sai da ya kaita asibitin da ya ke aiki akai mata tsarin family planing,acewar shi sai sun mori k'uruciyarsu sannan ko zasu haihu.
Atak'aice dai ,sai da sukai shekara tara babu haihu,daga nan suka fara bin asibitoci ,amma za'a'iya cewa ba adace ba.Nan fa abin ya fara damun su. Suna shekara ta goma da aure Allah ya ba hajiya Mariya ciki.kalar munar da sukai da cikin nan ba'acewa komai.Nan da suka fara tarairayar cikin .
Wayyo Allah ranar da hajiya Mariya ta haihu sai da alhaji Abba yayi kukan dad'i ,tun daga nan fa ya d'auki son duniya ya d'orama babyn ,ranar suna taci sunan mahaifiyar shi wato Amina,sukarik'a mata lak'abi da Meenal ,alhaji Abba kuma yana kiranta da meenalyn daddy kamar wasa sunan ya bita.
Tsabar son da alhaji Abba da hajiya Mariya suke nuna ma meenal yasa duk abinda tayi basa ganin laifinta,gashi tun daga kanta hajiya mariya bata kara koda b'atan wata ba.Hakan yasa meenal ta taso a sangarce, babu mai kwab'amata,tom garama hajiya Mariya dake shiga cikin mutane tana ganin yadda iyaye ke iko da yaransu takanji dama ita,dan ita kome zatai ma Meenal bata isaba tasa ta daina abinda takeyi,hakan sai ya fara damunta,tom shine fa yanzu ta fara k'ok'arin gyarawa amma ina abin ya ci tura.
Wannan shine dalikin da Mahaifin Meenal ya d'auki son duniya ya d'aura ma Meenal ganin ita kad'ai gareshi,gashi yasha wuya sosai kafin susameta .Wannan kenan"






Tunda hajiya Mariya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login