Showing 18001 words to 21000 words out of 56965 words
Chapter 7 - RETURN OF THE KING COMPLETE BY APHSERT KHAIREE .txt
shushemu keda Allahnki"
Ta fada sound so helpless irin bbu yanda ta iya d'in nan.Ajiyar zuciya King ya sauke at least de ta yarda zata kwantar da hankalinta ta zauna don amincewar Dada shine na Dija,sannu² zasu gane wani irin mutum ne shi da manufarsa akansu na son inganta rayuwa
"Nagode da amincewarki Dada insha Allah bazaku ta6a nadamar kasancewa dani ba"
"Munji tho,yanxu a kawo mana abinci bingel am tanajin yunwa don tun jiya rabonmu da abinci"
Tashi King yayi cikin hanzari yace tho ya fita a dakin inda ya samu Zee da AA na zaune zaman jiranshi,dinning ya wuce ya dauko warmers din abincin da aka jera wanda Babaji yaci nashi ya bari don plate dinma na wajen ya hada da plate da spoon ya kara wuce dakin nasu sude su Zee da kallon mamaki kawai suka bishi harya rufe kofar dakin.
Dija na ganin King da warmers din abinci ta hadiye kukanta dukda batasan meya dauko ba ama tana kyautata zaton kwanukan abinci ne na en gayu,ajiyewa yayi a gaban Dada yace
"Ga abincin nan Dada,idan kun gama ku fito parlor don Allah"
"Toh sannu mungode,ina fatan bakasa guba a abincin ba?"
Murmushi King yayi ya girgiza kansa kawai ya fice a dakin
"Sorry na barku jira"
Ya zauna kusada AA,kallonsa AA yayi yace
"What's going on man?"
"Karka damu aikin ba naka bane"
Ya fada yana maida dubansa kan Zee yace
"Ermmm Zee please taimako zakimin,inada baki en Fulani ne a nan gidana that I want to help.Family ne I mean Baban da mamar sai er su duk suna nn wajena"
Da mamaki AA da Zee suke kallonsa
"Man a ina ka samesu,na tabbata bakuda en uwa Fulani?"
"Abeg AA ka kyaleni nace maka aikin nan bai shafeka ba,just listen in kuma bazaka iya ba then set your way kawai"
Dariya AA yayi yace
"Kaide a kwashe² zaka kare wallahi"
"Ehh naji,mind ur business please"
Wayarsa ya ciro yana dariya shi kuma King ya kara maida dubansa kan Zee data kuresa da ido tun dazu
"Kinaji Zee,yarinyar nakeso ki taimakawa don inason kaita school gashi koh Hausa bataji Kinga ba karamin aiki bane"
"How old she is?" Zee ta tambayeshi
"Bazata wuce 16 ba"
Wani irin tuquqi Zee taji a ranta dukda bataga yarinyar ba
"Can I see her"
"Yeah,zasu fito yanxu suna cin abinci ne"
"Okay,so yanxu me kakeso na maka akai?"
"Yawwa,like I was saying zaki taimaka mata wajen koya mata wasu abubuwa na zamani da kuma karatun please kinde gane mai nake nufi.Irin fulanin dajin nan ne masu yawo kiwo,she needs to know a lot"
"Karka damu zanyi iya kokarina Insha Allah"
"Yawwa nagode sosai,yanxu wani school kike ganin zata fara?"
"Ehmmm,we'll think about it"
Bude kofar da sukaji ne ya mayda hankalinsu wajen inda Dada ta fita Dija na rukube a bayanta,tashi King yayi da fara'a a fuskarshi yana nuna musu kujera yace
"Bismillah Dada,ga dan uwana da matarshi sunzo gaisheku"
Wani kallo Dada ta bisu dashi ta tsaya kallon Zee din sama da kasa kamar taga kashi,AA ne ya fara gaisheta ta amsa a dakile snn Zee tace musu
"Morning"
Wani sheqeqe Dada ta kalleta tana wani sake baki tace
"Kaji kafura er gidan kafurfur jikar k'aruna"
Wani kallo Zee tabita dashi tana mamakin wannan village woman d'in da ko kallo Bata ishetaba take cemata kafura karde sune King yake magana akai?kallon AA tayi tana fadin
" Wonder shall never end, can you imagine see dis old rag"
gyaran murya king yayi Zee ta juyo tana kallonsa ranta a 6ace daman ita akoi saurin hasala yace
"Take it easy lady,Dan Allah don't take it personal help them for my sake"
Hadiye wani tuquqin bakin ciki tayi daya tokareta a wuya dakyar,Dada kuwa tashak'a takai har wuya jin suna zuba yaren kafirai.kallon king tayi tace
"k'ad'o shinikin kanmu kakeyine mude mundogara ga Allah"
AA yayi gyaran murya yamaida kallonsa ga Dada yace
"Mama ki kwantar da hankalinki indai agidan nan kuke wurin wannan bawan Allahn to bakuda fargaba dan mutumin kwarai ne in yanason cutar daku bazai kawo ku gidansa ba ya kawo kune kawai dan inganta rayuwar ku data erku
Kuyarda da Allah ku yarda dashi bazai cutar da kuba"
kallon zee yayi yana guntse dariya cikin murya kasa² yace
"Saikin dage dan kansu a tukunya yake"
Gyada kai tayi tana mai jinjina aekin da king ya bata murmushi tasakarwa Dija dan ita Dada tagama shaqar da ita duk da taga yanda jikinta yayi sanyi da maganganun AA tace
"Emmata ya sunanki?"
King ne ya bata amsa da DIJA,murmushi tayi tunawa da abinda King ya fadamata dazu akan batajin Hausa.Still tana kallon Dijan da kanta ke k'asa tana wasa da fingers dinta ta maqale a jikin Dada tace mata
"DIJA,masha Allah Khadijah kenan ko?"
Jin ta kira sunanta yasa Dija d'aga mata kai kawai badan taji mai ta fada ba saide yanda Zee keta mata murmushi ne ta burgeta har taji itama ta kwanta mata arai tana mayar mata murmushi ta mai kyau wanda yasa zuciyar zee bugawa dan zallar kyau da quruciyarta daya bayyana sharewa tayi ta mayda kallonta kan King tareda lumshe idonta da gyada masa kai alamun komai zai tafi dai²,itade Dada kallonta kawai takeyi a yatsine don sam yarinyar bata kwanta mata ba...........
🤥🤥🤥
Kar kuyi sanya,ku cigaba da biyoni don ba'a ma fara wasan ba tukun 🤙🏻
"
[1/6, 9:03 PM] +234 708 603 7570: *RETURN OF THE KING*
BY APHSERTEEN KHAIREE
ELEGANT ONLINE WRITERS
15
ZEE basu bar gidan ba saida ta tabbatar taja Dija a jikinta sosai ta sake da ita dukda Dada na tsawata mata dole ta hak'ura ta kyalesu ama idonta na kansu kar a cutar mata da 'ya.Ran Zee fes cikeda nishadi don wnn aiki da King ya sata tamkar wani tsani ne na cimma nasara wajen biyan buk'atarta,mutuk'ar gyara wnn er dajin ne farincikin King toh ta daura d'amarar biya masa buk'atarsa ta tabbata hakan ne kad'ai zaisa ta samu kusanci da shi.
Sun tafi akan kullum zata dinga zua tana yini dasu Dija harsu sake da ita kafin a sama mata makaranta,Babaji kua yana cen wajen sabon abokinsa Baba Audu mai gadi da yake cewa Bandarawo (abokina) ya sake sosai suna hirarsu Babaji ya dafa musu shayi a er butar shayin mai gadi sun karkace akan benci suna shan kidarsu a tashar radio.
Koda King ya rakusu AA suka gansu abin ya mishi dad'i sosai don har saida kwalla ya taru a idonsa tunawa da Babansa don shima yana yawan fitowa wajen mai gadi su sha hirarsu, yana fatan Dada ma zata sake ta kwantar da hankalinta su daukeshi tamkar d'a.
Su AA zasu shiga mota King ya tsaida su
"Ga baban Dija cen wajen Baba mai gadi muje ku gaisa"
"Ohh King toh ka bari mu shiga motar ai sai mu tsaya mu gaisheshi" inji AA
"NO,wallahi baka isa ba wani irin gaisuwa ne a mota"
"Hahaha,Man anya kua ba wata a k'asa kode²"
"Kai kasani,nide muje ku gaisa lokacin sallah yayi don iskanci ka tsaya kayi sallah tukun ama zakace wani sauri kake.Haryanxu bazaka dena missing sallah a jam'i ba koh?"
Basar da zancen AA yayi yace
"Kaide muje mu gaisa dashi kana 6atamin lokaci bansan yaushe ka koyi surutu ba yau,Zee taho da motar bakin gate kawai ki sameni anan"
Okay tace bayan sunyi sallama da King ya shiga tayi warming motar su AA kuma suka doshi wajensu Babaji dake kishingid'e Baba mai gadi kuma ganin Zee ta tada mota ya nufi gate
Bayan sun gama gaisawa AA ya shiga mota suka wuce gida cike da sake² a ransa,shima zuciyarsa fess don yana ganin lokacin cikar next burinsa akan King ya kusa dama Allah² yake a zo wajen
"You're smiling?"
Zee da tagama noticing dinshi don yana driving yana zabga murmushi kana ganinshi kasan yana cikin farinciki,cikin er basarwa AA yace
"Kuka kikeso nayi?"
"No,but what's the reason behind d smile? Tunda muka fito kamar kana cikin nishadi"
Dariya AA yayi ya d'an buga sitiyari yace
"Zee sa ido,kawai mutanen King ne suka bani nishadi.They're really funny,I like them"
Ya fada yana murmushi,6ata fuska Zee tayi taja tsaki kawai har suka iso makeken gidansu dayafi na King tsaruwa da kele²n duniya don ba karamin kudi AA yake kashewa kansa ba haka zasuyi ta fada da King akan ina yake samun irin kudi daya yake kashewa haka don yasan aikinsa de bai kai ya dinga samun wnn mak'udan kudin ba sai yace mishi yana k'ananan harkokine.Haka ma wajen suturu da motoci duk ya kere King ama dukda haka farin jinin jama'a da samun nasara akan komai King ya fishi don koh a wajen aiki ya fishi matsayi saide kawai AA ya nunamasa kudi wanda baisa jama'a kaunaceshi ba kamar yanda sukewa King.Sau tari ma mutane na mu'amala dashi ne sbd kusancinshi da King din
A kwana a tashi ba wuya,duk abinda aka sawa naci da addu'a tareda fatan nasara sai an cimma gaci saide wani ikon Allah don ba lalle ba komai kake so saika sameshi ba arayuwa duk nacinki wani abin saide ka hak'ura,haka ma idan kaga kanata addu'a da rokon Allah akan abu kaga bai baka ba toh karka sare shiyasa akeso ka barwa Allah zabi akan komai da zakasa gaba arayuwarka.Allah ya mana zabin alkhairi
Yau da gobe tafi karfin wasa don duk kulafici,taurin kai da kafiya irinna Dada saida ta hakurewa kanta don kusan wata kenan bata taba cin karo da abin 6atanci ba a gidan King ba,sunyi fresh fatarsu da kalar tayi kyau sosai sbd nutsuwar zama waje daya da samun ingatattun abinci masu lafiya da gina jiki ga ra6ar AC ga rashin shiga rana.A cikin wata daya ba Wanda zai gansu yace sune masu yawo kwararo² sako²
'Suna bara suna karuwa' ba,dukda Allah ya karesu ba'a taba karuwar dasu ba 😂
DIJA an fara d'an gane Hausa ana kwakkwab'awa don irin yaran nn ne masu karambani da son koyan abu ashe rashin sakewar Dada ne yasata ta zama wata sukuku lokacin, gashi ta fara zuwa makaranta gand'an² a primary 4 both boko da islamiyya King ya sata dukda wahalar da karatun na bata wahala yanda komai tayi a aji sai yara sun mata dariya a makarantar baya sata losing hope hakan nn take dagewa ta kwab'o abinta koda za'a dariya ita koh oho abinda tasa a gabanta kawai takeyi itama tanaso ta zama er gayu kamar yanda take ganin Zee yana bata sha'awa a koda yaushe.
Zee ma na iyakar kokari akanta don sun saba sosai tana qoqarin fahimtar daita yanda zata kula da tsaftar jikinta dan dija ba Arabia bbu boko ko jinin haila batasan yanda zata kula ta tareshiba balle akaiga zancen wanka ranar da jinin yazo zee tana nan ita takoya mata yanda zatasa pad aekuwa ranar haka ta dinga tafiya tana kwale² Jim kadan sai ta tafi toilet ta leka in taga jini koh d'an diss ne sai a chanza wani,a takaice de kan tayi wanka saida aka karar da pad yakai leda 6.Zee kuwa tana cin dariya
Bra kuwa da Zee ta siyo mata masu shegen kyau ta nuna mata yanda zatasa,suna zaune a parlor da Dada sai ganin Dija sukayi da fito ba riga
"Dija ya haka ina rigarki kuma ya zaki fito parlor haka?"
"Ai wollah wnn riga mai cheu din bani rufeta,Zee am kinga yanda tamin cheu kuwa"
Haba Zee mai zatayi banda dariya,Dada kuwa ta shak'a tace
"Kai Zoo karuwa zaka koyawa bingel am,koda ban bari tayi karuwa ba sai yanxu zakizo ki fara koyamata yawo tsirara shiyasa har yanxu ban gama sakewa dake ba don daga ganinki kema karuwa ce Aradun Allah"
Cikin fullanci ta cewa Dija ta wuce da kuma ta saka rigarta,turo bakin gaba tayi tana tattaka kafa irinna shagwaba.Ana cikin wnn drama saiga King ya shigo da sallama idonsa ya sauka kan kirjin Dija,a guje ta koma daki sbd tsananin kunya ita tama manta da zai iya shigowa.
Zee CE ta bashi lbry abinda ya faru ya ka'da kansa kawai ya fice don ba karamin harbuwa yayi ba har junior na bashi sign 🙈
Ranar wata Saturday,Driver ya d'auko Dija daga islamiyya around 12 ta wuce flat dinsu da gudu SBD yunwar da ta kwasu don batayi breakfast ba,a parlor ta yarda hijab din islamiyyar da dankwalinta tayi kitchen ama bata samu komai ba don Dada ta fitar da breakfast din Sanin za'a kawo lunch kuma tasan Dija kota dawo bazata ci ba.
Dakinsu ta shiga ta tarar da Dadan na bacci dama ta baro Babaji a wajen bandarawonsa,yasa mai zatayi tayi gashi har kamar ji takeyi manyan hanjin cikinta na had'iye kananan,fito tayi ta doshi flat din King for the first time.Bata samu kowa a parlor ba ta danyi dube² koh zataga wani ama shiru sai kawai tayi hanyar steps da tagani
Kofar farko da bude a hankali Wanda yake parlorn King inda bedroom dinsa yake,tayi sa'a kua YANA parlor a kwance yana kallo jin bude kofar yasa shi kallon bakin kofar
Yayi mamaki ganinta don basu ta6a shigowa flat dinsa ba,tashi yayi ya zauna yana kallonta cikin shigar uniform dinta sky blue riga har guiwa da wando Wanda ya fito da asalin kuruciyarta kanta ba d'ankwali ga gashinta a tsafe yasha gyara don Zee na kula mata da kan sosai.
Bai taba noticing changes dinta ba sai yau,ta mishi matuk'ar kyau sosai harya kasa dauke idonsa akanta.Ji yayi yawun bakinsa ya qame ya kasa furta komai kawai ya kafeta da ido sai saukar muryarta yaji tana
"Don Allah zakici buyoti?"
Kasa gane me take nufi yayi kuma ya kasa kara tambayarta,ita kuwa duk ta soma galabaita don batada jimirin yunwa sam yau ma don tayi latti ne ama bata fita bata karya ba.
Cikinta ta fara nuna masa snn ta mishi in kiya dasu hannuta a baki alamar abinci sai lokacin ya gane tana nufin
"Don Allah zanci bread" kenan
Hanyar kitchen ya nuna mata don shi kam har lokacin jikinsa a mace yake dama kwana biyu ya kasa gane kansa tun ranar daya ganta bbu riga. Da sauri ta wuce kitchen din saide tana shiga ta tsaya turus don bataga komai a sarari ba sai kawai ta durkushe a wajen tasa kuka
Jinta shiru² bata fito bane yasa King tashi ya bita kitchen din,tun kafin ya karasa ya hangota a durkushe a kasa tana kuka shame² koh ganinsa batayi ba
Cikin sand'a ya koma baya yana gintse dariyarsa ya dauko camera sa dake parlor don dazu ya game duba wasu pictures daya dauko,dawowa kitchen din yayi ya tsaya inda bazata gansa ba har lokacin kuka take iya karfinta ga majina da hawaye har bakinta yayi snapping dinta..............
_CIGABAN LABARI_
Knocking kofarsa ne ya dawo dashi daga cen shudadden duniyar daya tafi na tsawon lokacin da bai sanma ya bata ba wajen
"Come in"
Yace dakyar don murya koh fita dakyau batayi kuma yasan Zaki ne,budewa yayi ya shigo da sallama King ya amsa ciki²
"AA KAITA da matarshi suna jiranka a kasa"
"OK ina zuwa"
Share and share fisabillah 🙏🏻
[1/6, 9:03 PM] +234 708 603 7570: *RETURN OF THE KING*
16
K'arar spoons ne kawai ke tashi akan dinning table din,kowa ya maida hankalinsa kan abinci yayinda suke having dinner a nutsuwa da burgewa.Cikin zukatansu kuwa tunani ne da sake² kala² kowannensu keyi
AA ne ya fara ajiye spoon din ya d'au tissue ya goge bakinsa,d'an gyaran murya yayi dukda King ya jisa baisa ya d'ago ya kallesa ba ya cigaba da aikin cin abincinsa.Zee kuwa juya spoon din kawai take ama hankalinta sam baya jikinta ta rasa dukkan nutsuwarta ganin wani irin kyau mai daukar hankali da King yayi,gashi k'ananan kaya ne a jikinsa don kafin ya sauko saida yayi wanka yasa wata iri armless da three quarter trouser wanda ya k'ara fitowa da ainihin mazantakarsa ga kamshin turarensa daya gama tafiya da nutsuwarta.
"I must say it's good to have you back again after a while"
Ba tareda ya d'ago daga cin abincinsa ba yacewa AA
"Thanks"
Murmushi AA yayi cikin son basar da abinda King din yayi na nuna halin koh in kula akansu daga shi har Zee din yace
"So,wani irin taimako zan maka yanxu"
"Akan me kenan?"
"Your upcoming gubernatorial election, naga yanxu baka da komai baka da abinda zaka tsaya campaign dashi and I know baka da wani dan uwa da zai tsaya maka bayan ni"
Ajiye spoon din shi king yayi ya kalli AA yana masa murmushi yace
"When a King's palace is burnt,a more beautiful one is rebuilt. Kar ka damu I need no one help,kaji da naka campaign din.I can do and undo as I wish"
Tashi tsaye AA yayi shima King ya tashi suna fuskartar juna kowannensu da murmurshi a fuskarsa ita kuwa Zee kawai binsu take da ido kamar an kafeta a wajen haka Zaki ma na tsaye daga gefensu,AA ya mikawa King hannu yace
"Allah ya Bawa mai rabo sa'a,best of luck Man"
Rike hannun AA yayi still smiling yace
"Ameen ya hayyu ya qayyum,thanks so much Old friend"
Sallama sukayi AA yayiwa Zee da ta kasa furta koda kalma daya magana akan ta tashi su wuce,har wajen motocinsu King ya rakosu ya daga musu hannu yayinda suke fita a gidan.
Dakin da Fahima take ya wuce direct inda ya sameta a bakin gado tana kwance kan praying mat tana kallon ceiling, she's deep in her thought har bataji shigowarsu King da sallamarsu ba.Sautin gyaran muryar King ne ya dawo da ita hayyacinta,ganin King a zaune ya sata mikewa da sauri ta zauna tana kokarin hada kalmomin bakinta ama ta kasa sbd firgici don bataji shigowarsa ba sam
"I inaaa kwa..kwana..
Ta fada kamar mai koyon magana,sarai ya gane yanda ta firgita sai kawai ya basar ya kara hade fuskarsa tamau yace
" Dukda abinda ya faru dake nasan you'll still eager to know much about me koh?"
Cikin dan tsoro Fahima tace
"No no Sir"
Daga mata hannu king yayi alamar tayi shiru ya cigaba
"Nasanki Fahima Aliyu,nasan nacinki da son bin kwakwafinki akan aiki kuma nasan kowanni irin hali zaki shiga bazai saki qara jajircewa akan aikinki ba and I like that,keep it up.Inaso ki cigaba da aikinda kika fara a kaina but this time around ya zama kanki da kasarki kike yiwa aiki ba don buqatar wasu ba"
Idonta ne ya tara kwalla jin abinda king yace,tho koh Zaki ya fadamishi tambayar da tayi masa ne dazu.Ama kuma menene bazata zubda mukamanta ba,tabbas yanxu ne ma take qara jin wani irin karsasshi akan aikin nata
"Ama yarona fah?"
Ta fada idonta na kawo kwalla,dauke idonsa yayi daga kallonta yace
"He'll be safe,kema zaki koma gidanki ki cigaba daga inda kika tsaya"
"Kana ganin zasu kyaleni?"
Tashi king yayi ya juya ba tareda ya kalleta ba yace
"You're