Showing 27001 words to 30000 words out of 56965 words

Chapter 10 - RETURN OF THE KING COMPLETE BY APHSERT KHAIREE .txt

28 Dec 2024

3341

cin amana, dadai sauran muggun halaye saide anan nakasa gane shin wake cin dunduniyar daya a cikinku?"


Jijiyoyin goshin AA ne suka miqe sukayi rad'u rud'u idanunsa suka d'ad'a rinewa,a zuciyarta tace


"Anzo wajen"


Gyara zamanta tayi tace


"Kamar yanda kace last question, I have no choice dukda dubbin tamboyoyin dake bakina dole na tak'aita.Baka ganin zargi zai iya hawa kanka akan 6atansa sbd ka samu ka hau mulki?"


"Saide in kece zaki cusa musu wnn tunanin yanxu"


"Thank you so much for your time Excellency,anan muka kawo muku karshen wnn shiri sai ince sai mun mako na gaba inda zamu k'ara gayyato muku daya daga cikin gubernatorial candidates dinmu"


Tashi yayi gaba koh amsa godiyansu baiyi ba securities dinsa suka goyo masa baya suka bude masa bayan mota ya shige tare da P.A a gefensa


"Ina buk'atar kowanne movement dinta"


Yacewa P.A ba tareda ya kallesa ba


"Done"


Da fara'a a fuskarta Fahima ta doshi sauran ma'aikantan nasu dayan daga cikinsu ne yana fara'a yace


"Wow Fahima Aliyu you killed it,wallahi kin burgeni don nasan kua da tambayar nn a bakinsa kinga kin jawo attention din jama'a bari ma kigani"


Ya shiga Facebook a wayansa inda suka daura shirin live dubbin comments din jama'a


"Yes Nurraddeen haka mukeso dama"


Cewar Fahima sai murna take,Boss ne ya karaso inda take yace


"Weldone Fahima Aliyu am proud of you,samun jajirtacciyar da mara tsoro cikin ma'aikatan mu abu ne mai wuya.Allah ya taimaka ya kareki"


"Ameen Sir thank you so much"


Tattarawa tayi ta bar office sbd aikinta na gaba da takeson aiwatarwa,Health care hospital ta nufa direct dama ta samu contact din registrar asibitin..








_ZEE KAITA_


Tunda AA ya fadamata buk'atarsa ta shiga rud'u da tunani dukda abinda ta dade tana nema ne da mafarkin samu ama tayaya hakan zai faru,menene dalilin AA na sata wnn aikin kode cutar da King yakeson yi don har wani abu ya bata da zatasa a gabanta.Toh ko da hannun AA a 6atan King da matarsa ne? Ita kadai take yiwa kanta tambayar


"No,bazan taba yarda ka cutar dashi ba AA.Inason King son da bazan ta6a bari wani ya cutar dashi ba balle ni da hannuna, tabbas 6acewa Dija ni alheri ne a wajena snn sai kayi nadamar damar da ka bani akansa don zanyi amfani da ita wajen cimma nawa burin"


Shiryawa tayi cikin atamfarta lemon green dinkin gown tayi kyau sosai,mayafi,jaka da takalminta milk ratsin atamfar.Ita kadai ta fita don koh guards dinta da driver ce musu tayi bataso yau ta ita kadai zata fita


Cikin wani black tint car ta nufi anguwarsu King da sunan zataje mishi jajen abinda ya faru last two days.
Luckily kuwa ta sameshi a gida inda ta tarar da gurds dinsa guda biyu a parlor,Zaki bayanan ta tambayesu King daya guard din yace mata yana sama bari ya mishi magana kamar ta ce masa ya bari zataje saman da kanta sai kuma ta basar.


Yana kwance akan 3seater a parlornsa na sama idonsa a lumshe kamar mai bacci, guard din yayi knocking ya bashi izinin shigowa


"You've a visitor downstairs"


Ba tareda yabude idonsa ba yace


"Who's that?"


"First lady Zee KAITA "


"Kace ta karaso sama"


"OK"




"Meet him there"


Guard din ya fadamata haba kamar an mata bushara da gidan aljanna haka taji don dadi,ta wani kara sauke wuyan rigarta da yake off shoulder mayafin dama oneside ta yafashi sai er mini bag dinta a daya hannu ta haura sama cikin wani tako mai jan hankali,koh knocking batayi ba ta bude kofar kanta tsaye


Yana nn a kwance haryanxu idonsa a rufe tayi sallama karaso har inda yake,ciki² ya amsa mata still bai dago ba kuma bai bude idonsa ba.Tsaya tayi tana binsa da wani mayen kallo from head to toe,singlet ne jikinsa sai three quarter har wani hadiye yawo take don nn take jikinta ya bata wani irin sign


Sarai YANA kallonta ta wutsiyar ido ama yaki koda motsawa a wajen ita kuma hakan ya bata daman kare masa kallo tanaji kamar ta kwanta a kirjinsa a yanda yake kwancen,hannun kujerar ta zauna wajen kafarsa tace


"Hy king"


Sai lokacin ya bude idonsa yana dan lumshesu yana mata wani irin kallo daya kara narkar da ita,a hankali kamar wanda bayason yin maganar yace


"Zee how u?"


Mayfinta ta ajiye kan table da jakarta tana gyara zamanta akan hannun kujerar har kafarsa na shafan bayanta ta kwantar da kanta jikin kujerar tana mishi wani jarabben kallo


"Am good my King,ya hakuri?"


Kafin ya bata amsa yaji hannunta kan yatsun kafarsa tana shafawa zuwa tafin kafarsa,bai hanata ba kuma bai tanka ba snn bai tashi daga kwanciyar ba ya kyaleta tanayi.Ita kuma ganin mai gwaleta ba yasata jin wani irin dadi har ranta suka kafe juna da ido ta cigaba da shafa kafar tasa har kan wajen sangalalin inda gashi yake luff a kwance


Lumshe idonsa kawai yayi,ya rabu da ita, hakan ya mata dadi sosai tana ganin yau ta taki babbar sa'a sai ta zame daga hannun kujerar ta daga kafafun nasa ta zauna akan kujerar dakyau tare da daura kafarsa akan cinyarta.


"What are you trying to do"


Ta tsinkayi muryar King daya bude ido yana kallonta,daga kai tayi ta kalleshi tayi dan murmushi ta wani langwabe kai akan kujerar tana lumshe ido


Knocking kofar parlor aka fara Wanda yasa Zee zubara ta mike ba shiri,murmushi king yayi yana kallonta sai lokacin ya tashi daga kwanciyar ita kuwa tuni ta dau mayafinta da jaka zatayi hanyar kofa


"Five star room 102 tomorrow at 9"


Ya fada,juyawa tayi kafin tayi magana yacewa mai knocking din


"Come in"


Dole ta tsuke bakinta,Zaki ya shigo da sallama a bakinsa wani banzan kallo yayi mata ya dauke kansa ita kuwa da fice kawai tanajin wani irin farinciki mara misaltuwa....








Sorry kunji ni shiru 🙏🏻🙏🏻


















More comments more typing😎
[1/6, 9:07 PM] +234 708 603 7570: *RETURN OF THE KING*






21
"Where av u been,na kira wayarka bakayi picking ba?"


"Sorry King,naje checking wnn guys din da muka samu ne.They're very hard to break don haryanxu sunk'i bada had'in kai kuma kace mubi dasu a hankali and that will not be possible"


Shiru King yayi na en seconds tukunna yace


"Ku musu duk abinda ya dace"


"Okay"


"P.A na downstairs, yanason ganinka"


"Lemme fresh up,ina zuwa"


"A fito lafiya"


Fita Zaki yayi sai da King ya debi kusan 10mins a zaune tukunna ya tashi ya shige bedroom dinsa.Bayan 30mins ya fito cikin shiri wani voile yasa cream color kansa bbu hula ya gyara gashin sai sheki yake,takalminsa da wrist watch kalan kayansa,guards dinsa da P.A suka gaishesa ya amsa ba yabo ba fallasa bayan ya zauna akan cushion P.A ya karaso kusada shi da takarda a hannu na schedules dinsu na yau ya fara masa bayani




"Kamar yanda muka tsara zamu kaiwa gidan marayu ziyara yau that's will bayan sallar la'asar,gobe kuma zamuyi visiting kasuwanni koda biyu.Ranar Wednesday kana da interview da Daily trust TV"


"Allah ya kaimu"


King yace tareda mikewa sbd kiran sallar la'asar da akeyi suka fice dukkansu don gabatar da ita.Suna idarwa Zaki yacewa daya daga cikin guards din


"Get the cars ready"


Koh kafin King ya gama gaisawa da jama'ar da sukayi sallah tare har an shirya motocin shi kawai ake jira,ya shiga gidan baya P.A a gefe sai Zaki da driver a gaba sauran guards din kuma suka shiga sauran suma. P.A na mishi bayani kan tsare²nsu,King kuwa kallon garin kawai yake da d'an chanje²n da aka samu sai yaga garin ya chanza mishi gabadaya.


"Kaduna has really changed"


King yace har lokacin yana kallon hanya,Zaki ne ya bashi amsa


"Yes it has my King but it's still also belongs to you"


Murmushin gefen baki King yayi bai sake magana ba hakama P.A sai driver dake aikinsa,suna cikin tafiya driver yayiwa Zaki wani magana wanda yasa Zaki juyawa ya kalli King yace


"It seems we have company, koh zamu juya?"


Kwantar da kansa King yayi ba tareda nuna damuwa ba yace


"No,Kyalesu suyi"


Waya Zaki ya ciro daga aljihunsa yasa a kunne


"Keep moving but shine ur eyes"


Ya mayarda wayar aljihunsa har suka iso orphanage din inda suka zazzaga snn King ya bada tallafin mak'ud'an kudade wanda yasa P.A bayan sun shiga mota zasu koma gida magana


"Sir,account dinmu yayi kasa sosai fah gashi gobe zamuje kasuwa"


"Ina kace zamuje?"


King ya tambayi P.A


"Kasuwa"


Bai sake magana ba har suka iso gida.






_FU'AD_


Dawowarsa knn daga office ya baje a parlor yana sassauta tie dinsa inda Salim ya taho da gudu yana masa oyoyo,kannensa emmata biyu Abidah da Siyama na zaune a parlor da waya kowacce a hannunta suka mishi sannu da zuwa


"Yawwa emmata Mummy, ina mummy take?"


"Tana upstairs bari na kawo maka ruwa bro"


Siyama ta amsa tareda mikewa ta nufi kitchen,Abidah da hankalinta ke kan waya ne ta d'ago ta sauri tana


"Bro bro kaga news din dake trending a social media kuwa,wow gsky mom Salim ta burgeni"


Tsaki Fu'ad yayi yace


"Ai daman ke shashasha ce,me abin burgewa a aikin sa kai a had'ari,aikinda zai rabaka da masoyanka"


Ya fada with deep pain in his heart,shiru Abidah tayi bata sake magana ba don ta harbu jirgin Yayan nata


"Ai sai taje cen ta karata tunda abinda ta zab'awa kanta knn,kai kuma daman koh kusa koh alama banasoji na sakeji ka taka inda take tunda Allah ya tseratar dakai da yaron nn toh ya kare mata ita kadai.Duk tsuntsun dayaja ruwa shi ruwa yake duka"


Suka tsinkayi muryar Mummy dake saukowa daga stairs, kasha shan ruwan da Siyama ta kawo mishi yayi kawai ya dauki jakarsa da rigar suit dinsa ya shige ciki hanyar dakinsa.Salim kuwa shiru yayi jikinsa yay sanyi don tunda yaji Aunty Abidah ta kama sunan Mom dinsa yasan akanta ake magana ga yaron da shegen wayo


Koda Fu'ad ya shiga dakinsa kwanciya kawai yayi kan gado cikeda damuwa da kewar matarsa,don har gobe bazai dena sonta da murad'in sake rayuwa da ita ba.


"Why Fahima why,meyasa kika zabi nisanta kanki dani,why do you always choose ova me,me kike nema a rayuwa da bazan iya miki ba,mesa bazaki tausayawa halinda zuqatanmu suke ciki ba? nasan kema kina cikin damuwa ama strong head dinki yayi yawa.Why....?"


Hawaye yake kamar karamin yaro yana jin wani irin rad'ad'i a ransa.






_FAHIMA_


"Assalama alaikum"


"Wa'alaikis Salam Fahima Aliyu sannu da zua, har kin k'araso knn"


Yace da fara'a a fuskarsa don ba karamin burgeshi daman take ba akan aikinta,hatta hiran da tayi da AA ya daya daga cikin wanda suka nuna jindadinsu akan tambayoyin da tayiwa AA din ta hanyar suburbud'o comments da jinjina a duk shafukan zumuntar da aka daura shirin live.Murmushi ta mishi tace


"Yawwa Magaji Ilyas right?"


"Sure sure,ka guri zauna mana"


Yana nuna mata kujera dake gaban desk dinsa sai fara'a yake zabgawa irin yau gashi ga cele dinnan don Fahima yanxu kam ta zama celebrity duk inda ta wuce sai ta gaisa da jama'a wasu ma har suyi requesting selfie da ita. (Wato yanxu de abu kalilan zakayi ka zama cele,kana daga kan gadonka ma in Allah ya daukaka akan wani abu sai kaga ka zama 🤭Allah ya kara soyayyarmu a zuk'atan masoyanmu ya bamu ikon nishad'antar da masoyanmu)


Zama tayi akan kujerar tana fuskantarshi ta ciro pen da wani dan karamin littafi mai kyau ajakarta


"How can help you"


Ya tambayeta,dan clear d'in throat tayi tace


"Thanks,shekararka nawa kana aiki a asibitin nn?"


"8 good years"


"Daga wani irin aiki ka fara?"


"Da farko na fara daga mai bada kati na kusan shekara 1 da rabi har Allah yayi daga baya na kuma registrar wato duk wani file na patients ni nake adana shi har kawo yanxu"


"Masha Allah,Allah ya taimaka ya k'ara daukaka"


Sosai yaji dadin addu'arta YANA murmushi yace


"Ameen ameen nagode kema ina miki fatan haka"


"Shekara 6 da suka wuce matar tsohon governor ALIYU MOHAMMED GIWA tayi ante natal dinta a nn asibita har takai matakin haihuwa kuma duk anan asibitin tayi koh zaka iya tuna lokacin"


"Tabbas haka yake,duk wani tsohon staff kai harma da sabon yana da wnn labarin don haihuwar wnn baiwar Allah ya kasance daya daga cikin kundun tarihi na wnn asibiti"


Cikin jindadin samun had'in kai da bayanai masu matuk'ar mahimmanci daga wajensa Fahima tace


"Koh meyasa haka?"


D'an furzar da numfashi yayi yace


"Sbd wani abu daya faru mai kamar almara koh tatsuniya,kamar a shirin film koh irin qirqirarrun labaran nn na litattafai.Abinda ya gigita asibitin nn da ma'aikatar cikinta gabadaya suka shiga cikin rudu da tashin hankali,yaso tarnishing image din asibitin.Tabbas wnn rana ta kasance unforgettable moments,abun was just unbelievable inde ba agaban idonka ya faru ba"


D'an katseshi Fahima tayi


"Koh zaka d'an takaita please ka fadamin ainihin abinda ya faru a wnn ranar"


"Tho nide kamar yanda kika sani nine in charge na kowanni irin file na patients a asibitin nn,Iyalin Gov,Mohammed GIWA wanda kowa yafi sani da King a nn take awonta har zuwa lokacin haihuwarta.Allah sarki mace mai fara'a,taimako da son jama'a kamar mijinta don koyaushe tazo asibitin nn sai tabi kowanne staff da mishi ihsani shiyasa duk cikin asibiti bbu wanda bai santa ba ga barkwanci sam bata da girman kai.Kasancewarta matar Governor a lokacin baisa ta raina asibitin nn da jama'ar cikinsa ba,Allah ya jikanta da Rahma"


Ya fada cikin jimami,Fahima ta duk ta tarkata nutsuwarta akanshi tace


"A nn ta rasu ne?"


"Asshha,ai da anan akaga gawarta ai da sauki"


"So maiyafaru?"


"A ranar da aka kawota labour ta nn gaba na aka wuce da ita,shiganta na karshe knn sai amsa amon mummunan labry da asibitin ya dauka na 6acewarta itada abinda ta haifa en biyu.A yanda nurses din suka fada tana haihuwa bayan doguwar nakuda wanda har takai karfinta ya kare sai CS aka mata toh kafin ta farfado an kaita dakin hutu suma jariran an gyarasu sai shigowa akayi aka nemesu dukka aka rasa abin al'ajabi"


"Ya Subhanallah,Innalillahi was inna ilaihi raji'un"


"Hmmm kede bari munga tashin hankali ranar don gabadaya asibitin nn hargitsewa yayi"


Wani irin ajiyar zuciya Fahima ta sauke,mmk ne ya cikata


"Su waye suka kawota asibiti ranar?"


"Ita da mijinta King suka zo, shiya kawota don bazan taba mantawa ba"


"Tho shi yana ina lokacin da abin ya faru"


"Nide bayan ta haihu naga wucewarsa har nake tambayarsa yace min ta haihu,cikin sauri ya fice daga asibitin tho tun daga nn ban sake ganinsa ba don koda abin ya faru bangansa ba haryau kuwa sai labarin dawowarsa da naji kwanakin baya"


"Su kadai suka zo asibitin knn,anya bbu wanda ya biyosu?"


"Gaskiya de bangani ba don kinga duk wani mai shiga da fita ina gani tunda desk dina na kan hanya inde mutum ya shigo maternity ward tho tabbas zan ganshi"


"Hmmmm Allah ya kyauta"


"Ameen yarabb"


Shiru sukayi na kusan 2mins


"Nasan bazaku rasa CCTV ba?"


"Ehh akoi"


"Zan iya samun bayanai na 2015 please"


"Chap,aiki jaa ama bari na hadaki da wani wanda zai taimaka miki akan wnn"


"Yawwa nagode sosai,Allah ya saka da alkhairi"


"Babu komai,anything for you"








_ABIA STATE_


Su 8 ne a zaune a parlor wasu na shaye²n su wasu daga cikinsu kuwa sai busa sigari suke,3 daga cikinsu hausawa kuma musulmai ne sai 5 kana ganinsu kaga iyamurai


"See yau ne rana ta karshe,kuwa da kake gani anan yayi nasa kai kadai ka rage gwanda karka batawa kanka lokacin kaje kayi kawai don gobe za'a mikawa ODUBARIBA ita"


Tsaki yayi cikin takaici yace


"I seriously hate dis bazaka gane bane Gboy"


Dariya suka kwashe dashi dukkansu banda wani iyamuri daya da kana ganinsa kasan baya cikin nutsuwarsa damuwa shimfide a fuskarsa


"Dude what's wrong,u look so worried"


"Ina cikin damuwa David"


"Kar kacemin akan sacrifice dinka,C'mon uchenna yarinyar da bakwa tare ma bbu wani shakuwa tsakaninku I think dat will be so much easy for you"


"Bazaku gane bane,she's all I have dukda bama tare ina kaunarta sosai"


"Karamin da iskane kai uchenna muda muka bayar da namu ance maka bama sonsu ne"


Daya daga cikin hausawan ya fada tareda jan tsaki ya mike yayi hanyar wani daki,tana kwance a kasa da jen zani a jikinta an mata daurin kirji dashi iyakar guiwarta


"Kee.."


Ya daka mata tsawa wanda ya sata razana da mike ta sauri take hawaye ya fara ambaliya a fuskarta,Wani irin shock da firgita yayi lokacin da ya kalli fuskarta


"Who are you"


Yana pointing dinta da yatsa,itde sai karkarwa take tana kuka daga tsaye


"How comes,I said who the hell are you?"








Comments and share fisabillah🙏🏻
[1/6, 9:07 PM] +234 708 603 7570: *RETURN OF THE KING*




ELEGANT ONLINE WRITERS


22


A kid'ime ya fito daga d'akin,yanda ya bugo kofar ne ya jawo hankalinsu David kansa duk suka tsura mishi ido yanda ya wani firgice yana wani irin numfashi kofofin hancinsa duk sun bude har jijiyoyin kansa sunyi rad'a²


"No,this is not possible. Tayaya hakan ya faru,garin yaya"


Gboy ne ya taso kusada shi ya rikeshi yana tambayarsa da Hausa


"Meyafaru ne AA,koh ta mutu ne?"


Girgiza kansa kawai AA yakeyi yana


"Ba ita bace,wallahi ba ita bace"


"Kamarya ba ita bace,ban gane ba?"


"Wnn ba Dija bace,wnn ba matar King bace she's really not the one"


Dukkansu saida suka shiga shock suka fara kallon junansu


"What do you mean she's not the one AA,wani irin magana kake ba kai ka kawota da hannunka ba?"


Cewar David duk sun k'ura masa ido suna neman karin bayani


"Yes nina kawota da hannuna,nina fito da ita da yaranta daga asibitin ama tun ranar ban sake shiga inda take ba sai yau.Kuna nufin wnn ce a gidan nn tun ranar dana kawosu?"


"Itace mana AA,itace ka kawo da hannunka ama tayaya zakace ba matar King bace?"


Gboy ya tambayesa


"Tabbas ba ita bace,kaina ya kulle ina buk'atar ganawa da ODUBARIBA ayau don komai zai iya faruwa"


Tsaki Uchenna da nasa damuwa ya isheshi shima yaja ya mike yana


"Stupidity, you destroyed evrtin AA and am sure u'll face the consequence for that"


Yayi ficewarsa daga parlor,kwalbar giya dake kan center table AA ya dauka ya soma kwankwada har saida Gboy ya rike kwalbar a hannunsa


"Calm down,it's not too late evrtin will be fine ka kwantar da hankalinka"


Hannu AA yasa yana bubbuga kansa idonsa yayi jajir


"Aahhhh,urghhh No...bazai taba yiwu ba after all this long ace aiki banza kawai mukeyi"


Daya daga cikin iyamuran mai suna Samuel ne ya matso kusada AA ya dafashi yace


"Easy Man evrtin will be fine,am sure ODUBARIBA will find a way out"


Hanyar underground suka nufa inda DAKIN DUHU yake don zuwa ga ODUBARIBA,cikin ladabi, gushewar imani,toshewar zuciya da kwakwalwa suka zube a gabansa suna mishi sujjada.Cikin wata kakkausar murya mai tsoratarwa ya fara magana


"You destroyed evrtin AA KAITA so you're the only one to fix it"


"Tuba nake ODUBARIBA,nima bansan garin yaya hakan ta faru ba"


"For all this while our cults is waiting for the KING to RETURNED, our success and progress relays on RETURN OF THE KING"


"Meyasa Kunqiya tafi buk'atar King kawai ODUBARIBA"


David ya tambaya kansa a qasa


"Sbd lokacin sauka na yayi kuma muna bakatar mutum mai tarin nasara,farin jinin jama'a yayi taking over.Kaf

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login