Showing 24001 words to 27000 words out of 43872 words
na ji mugun tsoro ya shige ni fiye da na farko,haka na soma bulaye a ƙatuwar duniyar ina kallon abubuwan ban mamaki har na isa wani wuri inda ake yi wa wani aski.Duk suka ɗago suna dubana kafin su fara ƴar kallon-kallon,ɗaya daga cikinsu ya ce “ wane ne kai?”
Ba tare da wani tunani ba na basa amsa da “ Ni bil'adama ne!” ko ida rufe baki ban yi ba suka yi min caaaa kowa na faɗar ra'ayinsa“ a'a ni zan ɗauka! ” “A'a wannan fa gangar jikin tawa ce! ” “ kai kana da wajen biyu fa ka bar min kawai”
Ido kawai na rumtse ina rawar jiki,jin ana rigima akan gangar jikina wacce Allah ne ya halitta min ita amma saboda wata buƙatata na butulce wa rahamarsa na sayar.Ina cikin haka ne sai na soma jin canjin yanayi,ina ware idona sai na koma fanko wato ruhi babu gangar jiki.Da ido nake kallon yadda ake faɗan shiga gangar jikina wacce ta zama tamkar riga mai haɗe da wando............
Talla! Talla! Talla!!!!
Set d'in gyaran gashinmu na dauke da
* Shampoing don wanke gashi
* Man ganshi da zai taimakawa gashin wajen k'ara tsayi
* Man gashi wanda zai cire miki kwarkwashi/dandruff/Pellicules
* Garin ambunu da zai hana karyewar gashi
* Man karkar da zai taimakawa gashi wajen k'ara bak'i
* Garim amrfit don sakawa a hamata ta kasance cikin kamshi
* Man coco na asali don gyaran fata
+22780416252
[26/12 à 09:33] MRS SADAUKI: *MAFIYA*☠️
LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
_____________________
05
Ni da gangar jikina amma banda iko da ita wannan lokaci,ban ma san taƙamaimai ya zan yi na mayar da ruhina a cikinta ba ko kuwa sun maido min ita.A yanzu da nake gantali cikin iskan ɓoyayyar duniya sai na fahimci a cikin MAFIYA ni ba kowa ne ba fa ce ɗan ƙaramin jinjiri ashe ban san komai a kanta ba.
Dōr̃ānī kamar yadda aka sanar da ni sunansu tun shigowa ta nan,irinsu ne su biyu suka zo suka ƙwace gangar jikina daga hannun aljanan kafin su miƙo min .
“Ka shiga gangar jikinka sannan ka koma duniyarku tun da wa'adin da aka ɗebar ma ya cika,ka yi kwana uku cicif ”
Tsakanin furucinsa na cewa na yi kwana uku alhalin ni dai a lissafina ba zai wuce na yi minti talatin ba,da kuma tunanin yadda zan mayar da gangar jikin nawa a ciki sai na rasa wane zan yi.
“Ka mayar mana za mu mayar da kai” ya ƙara faɗa .
“Ban san ya zan yi na mayar da ruhina a ciki ba” na basa amsa.
Suka kalli juna kafin kuma su haɗin baki wurin cewa “ kai ɗin ba ahalin MAFIYA ba ne?”
Na jinjina kai na ce “sosai ni ɗin ɗana ga Mafiya amma ban san ya ake yin duk abubuwan nan ba” ban rufe bakina ba na ji sun soma karanta wasu ɗalasima wanda na yi imani na tsafi ne.Wani girrrr na soma ji,gangar jikina na haɗe wa da ruhina ban san ta yaya hakan ta faru ba amma tabbas yanzu na dawo HAROON ɗina.
Na ja ajiyar zuciya lokacin da suka ja ni izuwa can wajen ƙofar fita,na kasa haƙuri na ce “ amma ɗazu kamar na ji ka ce wai har na yi kwana uku a nan,sai nake ganin kamar minti talatin ne ko zuwa da biyar haka”
“Lokacin nan ba iri ɗaya ba ne da na duniyarku,duk minti goma ɗin ku matsayin kwana ɗaya yake a nan” ban kai ga ƙara yi masa wata tambayar ba suka cillo ni waje.
Ta hanyar da na bi na shigo nan ta haka na koma,a gaban idona yanzu ma can saman ya tsage kamar wata leda marar nauyi haka na tashi cikin iska na fito har tsakar fadar Oga ,tile ɗin ya koma ya ɗinke kansa.
Ɗaya bayan ɗaya nake kallon members ɗin ƙungiyar tamu,da dukkan alamu sun shirya wa fitowar tawa kamar yadda nake tsammanin Oga ya sanar da su komai.
A cikin abin da bai fi minti biyu ba na ga wani sabon abu wanda can farko ban taɓa ganinsa ba,ba komai ne bai sai shatin Cross a goshin kowa na member ƙungiyar sannan a ƙasan Cross ɗin kowanne daga cikinsu yana da alamun lamba,wasu 9,wasu 18 da dai sauransu.Ban yi nauyin baki ba wurin cewa “ Oga lambobin mene ne nake gani a goshi mutane?”
Bai bani amsa ba sai jin shuuu na yi,wani ɗan madaidaicin madubi ne ya zo yayi tsaye a gabana,ba wai wani ya riƙe shi ba a'a shi ke riƙe da kansa.A ta cikin madubin na hango hoton fuskata,wannan karon da tsokarta irin ta ƴan adam ba ƙwarangwal ce ba.Lamba ɗaya(01) na gani a tsakiyar goshina kuma ni ma ina da zanen Cross ɗin,ina gama gani madubin ya ɓace daga gabana.
Sai a lokacin Oga ya soma magana,“ Barka da shigowa wani level daga cikin MAFIYA! A can farko ba kowa ne kai ba face costumer mu,amma a yanzu kana level 1 sannan kamar yadda ka nemi alfarmar janye yarjejeniyar mu ta farko domin kawo wata sabuwa,mun karɓi kokenka.Sai dai kamar tun can farko yanzu ma zan sake jaddada maka cewa kowanne tasiri yana da farashi,ina nufin yanzu shekaru biyar ɗin da suka rage maka a duniya za ka iya ƙara su domin yin doguwar rayuwa” yana kawo wa nan sai yayi shiru tare da nuna mini kujera na je na zauna kamar sauran.
Zamana kan kujerar sai na ji tamkar ba normal kujera ba ce amma na dai yi shiru kawai ina jiran ƙarin bayani.
“ HAROON ?” Oga ya kira sunana,na ɗaga kai na kalle shi sai kuma na je zan mayar da shi ƙasa amma ya hana ni ta hanyar ce mini “ tsakiyar ido za ka kalle ni sannan ka sanar da ni ka gani a ciki”
Har sai da na ɗan ƙanƙance idona don ƙara samun tabbacin abin da nake gani shin gaskiya ne ko kuwa?
“Mi kake gani?” ya jefo mini tambayar.
“ Maƙabarta!” na basa amsa.
“Ka san me ake yi a can?”
“Eh na sani Oga!”
“Yawwa madallah da kai HAROON tabbas alamu sun nuna kana yunwar ƙara tsawon rai” cewar Oga kafin ya nufi allon da yake yi mana rubutu ko nace darasi.Wani suna ne ya rubuta mai harafi bakwai wanda tuni na soma tambayar kaina ‘ mene ne kuma alaƙarmu da sunan?’ ashe kuwa amsar na kusa.
“ HAROON ko tashi ka karanta mana abin da ke rubuce a nan” Oga ya umarce ni.
Na tashi tsaye kamar yadda ya buƙata kafin na karanta “ likafani ”
“Ƙwarai kuwa likafani ne kamar yadda ka karanta ɗin,ka yi daidai ina fatan kuma aikin da za ka yi da shi shi ma ɗin ya zama daidai”
“Aiki kuma Oga?” na tambaya cike da tsoro,duk kowa ya kwashe da dariya sai da suka yi son ransu kafin Oga ya umarci kowa yayi shiru.Fuskarsa babu alamun wasa ya dube ni yana cewa “daga lokacin da wa'adin shekaru biyar ɗinka ya cika to za ka dinga farautar likafanin sabuwar gawa domin luluɓa shi a jikinka ka kwana da shi,ta wannan hanyar ce kawai za ka ci gaba da rayuwa a wannan duniyar akasin haka kuma za ka koma inda ka fito yanzu.Na sanar da kai ne tun yanzu don ka zamana cikin shiri,abu na biyu kuma da ƙungiya ke buƙata a wurinka shine tsofin takalmi na yara ƙanana.Kowa zai iya tafiya meeting ya ida” yana gama faɗa ya bi wata hanya ya shige yayin da kowa ya watse ya bar ni cikin zullumi.
Dole dangin na ƙi ce ta saka ni fitowa ni ma,sai yanzu na tuna inda na bar motata wato can tsohon gidana.Taxi na shiga aka kai ni can amma abun mamaki babu motar a nan,a dole na ƙara shiga wata taxi ɗin na nufi gida.
Tun a bakin ƙofa na ga kallon da direbana ke yi mini,kamar zai yi shiru sai kuma ya kasa ya ce “yalaɓai yanzu ko minti ɗaya ba a yi ba na ganka da baƙaƙen suite fa kuma ga shi har ka canza kaya”
Na haɗe rai na ce “wato sa ido kake yi min?”
“Yi haƙuri yalaɓai” ya faɗa yana rusunawa.
Ina shiga cikin falo na ci karo da Ammy ita ma idon ta waro tana cewa “ HAROON canje-canjen kayan na mene ne? Ko don ka burge Malama Zainab ne? Hahaha! Wannan kayan fa kamar ma sun yi datti,waɗancan ɗin dai sun fi yi maka kyau”
Murmushi kawai na sakar mata ina cewa “ina zuwa” sai kuma na haye can sama,ina buɗe ɗakina na hangi irina sak yana ƙoƙarin shiga madubina.
“Dakata!” na faɗa da sauri,ya juyo muka haɗa ido amma bai saurare ni ba yayi wata suka cikin madubin tamkar wanda ya shiga ruwa haka ya nitse ciki tun ina ganin inuwarsa har madubin ya dawo normal........
Assalamu alaikum,mata da ƴan matan garin Agadas.CHAFA'ATU MAKE-UP fitacciyar kuma jajirtaciya mai koyar da kwalliya iri-iri.Ta yi tattaki tun daga Nigeria ta zo nan Nijar a garin Agadas domin horar da masu buƙatar koyon kwalliya,ɗaurin kallabi.Wannan horar wa da za a yi za ta kwashi kimanin sati biyu ,kuɗin koyo jika ashirin ne (20.000f).Ga masu buƙatar ƙarin bayanin za su iya kiranmu kai tsaye ta wannan lambar 88584336 ,ko kuma ku tuntuɓe mu lambarmu ta WhatsApp 09041604348 .
[26/12 à 09:33] MRS SADAUKI: *MAFIYA*☠️
LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
_____________________
06
Gaban madubin na je na soma shafa shi tamkar wasu ruwan Teku haka na ji hannuna ya nitse a ciki.A kullum cikin ganin sabbin abubuwa nake tare da madubin da ni ne da kaina na saye shi,maimakon da na saka hannuna na ga ya nitse na fiddo shi a'a sai na gwada shigar da dukkan gangar jikina.
Hazo-hazo na soma gani a cikin sabuwar duniyar da na tsunduma kaina,ban ganin komai sai wani abu da ke zuba kamar dusar ƙanƙara .Idona na soma ƙanƙancewa nan na hango gobena,ga ni tare da Malama Zainab har da yarinyarmu.Wani daɗi ya wanzu a zuciyata,ina son ƙara samun wani bayanin amma daga can waccan duniyar nake jin muryar Ammyna a kunnena raɗau.Da sauri na fito ina mamakin ‘ dama ana iya shiga cikin madubi ? ’ Sai kuma na watsar da tambayar na nufi ƙofa na buɗe murmushi kan fuskata.
“ HAROON ka fito mana ko ka manta yau rana ce ta musamman a gare mu?” Ammy ta faɗa tana murmushi tare da gyara min zaman rigata ta sama.
Sai yanzu na lura,kayan jikina sun sauya daga waɗanda na shigo da su zuwa irin mai kama da ni da ya ɓuya cikin madubi.
‘ Wane abu ne zai faru mai muhimmanci haka?’ na yi wa kaina tambayar a zuci,yayin da kuma na samu amsar tambayar kuma a cikin kwanyata “ yau za ka sanar da Malama Zainab kana son ta,shine alƙawarin da ka yi wa Ammy ”
Shiru na yi ina tunanin ‘ ta ya aka yi nake jin muryar mutum na yi min magana cikin ƙwaƙwalwa? ’
Nan ɗin ma wata amsar aka bani “ saboda yanzu ka fita daga matsayin 0 ka koma level 01 ,kana da buƙatar ɗan kariya mai baka rahoto akan abubuwa da dama, waɗanda suka faru da kuma shawara wurin yanke hukunci”
Ajiyar zuciya kawai na sauke ina kallon Ammy tsakiyar ido,“ ya dai? Kar ka ce min dai tsoro kake ji?” Ammy ta faɗa ,na girgiza kai na ce “ mu tafi ga ta can har ta iso”
Da mamaki Ammy ta ce “ ta ya aka yi ka san ta iso?” sai ta ja kumatuna.
Abin da na fahimta wannan ɗin sam ba furcin tunanina da niyyata ba ne, mataimakina ne ya furta ba ni ba.Amma sai na yi saurin cewa Ammy “ saboda ina mugun ƙaunarta shi yasa a duk in tana kusa da ni ina jin sautin zuciyata na canza wa”
Ammy ta shiga yi min dariya kafin ta kama hannuna kamar wani ƙaramin yaro muka fito.
Ina taka step ina kallon Malama Zainab wacce ke zaune tana duba wani littafi,yanayin nutsuwarta da cikar kamalarta sun fi komai burge ni a tattare da ita.
Ammy ce ta yi sallama,da sauri ta ɗago tana amsawa tare da gaishe ta.
“Lafiya lau Malama ya gida ina kuma iyayenki fatan duk kuna lafiya?”
“Alhamdullah suna gaishe ki ma” ta faɗa cikin rawar murya tana sunne kai,cikin ƙwaƙwalwata na ji muryar nan na ce mini “ kar ka cika kallonta hakan fa zai sa ta fasa son ka”
Ammy ta ɗan zungure ni,na dube ta sai ta yi min alamu kan na yi wa malamar magana.Na yi gyaran murya na ce “ uhum! Hajiya ko na ce Malama na gode sosai da kika karɓi wannan aiki na koyar da Mamana karatu muna godiya...” sai kuma na yi shiru, Ammy ta gusa ta bar falon tana harare na tare da yi min alama kan na zauna kan kujera .Abin da Ammy ba ta sani ba iya wannan tsayuwar ji na nake a takure,tamkar wanda ya shiga wurin da babu iskan shaƙa na san kuma hakan bai rasa nasaba da ƙarfin imaninta.
Ɗan nesa da ita na yi,sai na ji abin yayi dama .Na sauke ajiyar zuciya kafin na ce “ Malama Zainaaab?” a hankali ta ɗago ta dube ni muka haɗa ido,sai na ji wani ƙuna tamkar ta watso min barkono wannan karon ni ne na sauke idona ina rayawa a zuci ‘ tabbas da matsala! Yarinyar da na kasa haɗa ido da ita ta yaya kenan za mu yi aure har mu haihu? Ko dai duk abubuwan da na gani cikin madubi ƙarya ne? ’
Ɗayar muryar mai min magana cikin kwanya ta ce “ sam wannan ba ƙarya ba ce,tabbas za ka aure ta sannan ku samu yara sai dai saurin yiyuwar haka na tattare da kai akwai abubuwan da ake buƙata ka yi kafin har ka cimma ƙudirinka in ka ji kana iya wa tun yau za ka soma”
Tun da na soma jin maganar na yi shiru har aka ida kafin na sake tambayar muryar ‘ ta yaya kenan? ’
“Ta hanyar sato farin tauraro daga jikin wani bil'adama mai sakaci,tabbas da tauraronsa za ka yi amfani domin biyan buƙatarka” ina gama jin amsa na saki murmushi ,ina ɗago kai sai na kama Malama Zainab na satar kallona.
Na sakar mata murmushi yayin da ta yi saurin miƙe wa tana cewa “ zan koma ina da ɗalibai da zan yi wa karatu”
“Ok jira na kira Ammy ” na faɗa tare da zuwa ɗakin Ammy,tana gani na ta miƙe tana cewa “ komai ya tafi daidai? Ka furta mata ɗin kana son ta?”
Na yi murmushi mai sauti na ce “ A'a Ammy amma mun samu kusanci sosai ina ga ita ma tana sona ”
“Wato ba ka furta mata ba? Mtsww !” ta ja tsuki tana harare na tare da ficewa,duk sai na ji babu daɗi na take mata baya.
Da murmushinta mai tsadar nan take sanar da Ammy uzurinta,“ HAROON ka sauke Malama a makaranta”
“To Ammy ” na furta ba tare da na san yin haka babban kuskure ne a rayuwata ba.Har kusa motata Ammy ta yi mana rakiya,ita ce da kanta ta buɗe wa Malama Zainab gidan gaba.Dakyar na shiga na zauna na yi wa motar key,numfashina sai barazanar tsaya wa yake ba don komai ba sai don na yi kusa da farin ruhinta.
Ina tuƙi ina haƙi kamar wanda yayi tseren doki,zuciyata ji nake tana matse wa tana takurewa wuri guda .Hancina kuwa tamkar wanda aka matse sam babu daɗi ,iya ta baki kawai nake samu ina sheɗawa.Tun ina daurewa har na kasa,ina ƙoƙarin tsayar da motar kuma wayar Malama Zainab ta hau ruri ƙira'ar Sheikh Aliyu Jabeer ce inda yake karanta suratul yaseen.
“Yiiii!” na soma kyarma yayin da na kusa sakin sitiyarin motar ina,idona kuwa wani baƙin abu kawai nake gani da alamun lantarkin nasu ne yake dab da tsayawa.Hannunta na ji kan nawa on daidaita tsayuwar motar sai dai kafin wannan zuciyata ce ta tsaya cak da bugawa ........
Ga masu son fara yin payment ga detail nan ,500 via 2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank DM +22795045822 .Ki tura kawo sai ki turo min evidence sai na saka ki group.
Talla! Talla! Talla!!!
Set d'in gyaran gashinmu na dauke da
* Shampoing don wanke gashi
* Man ganshi da zai taimakawa gashin wajen k'ara tsayi
* Man gashi wanda zai cire miki kwarkwashi/dandruff/Pellicules
* Garin ambunu da zai hana karyewar gashi
* Man karkar da zai taimakawa gashi wajen k'ara bak'i
* Garim amrfit don sakawa a hamata ta kasance cikin kamshi
* Man coco na asali don gyaran fata
+22780416252
[26/12 à 09:33] MRS SADAUKI: *MAFIYA*☠️
LoVe aNd HoRrOr StOrY☠️
*Mallakar:* Chamsiya Laouali Rabo
(MRS SADAUKI💫✍️)
*Lambar waya:* +22795045822
*FIRST CLASS WRITER ASSOCIATIONS☀️*
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation.
_____________________
07
Cikin ikon Allah Malama Zainab ta yi nasarar tsayar da motar wuri guda,sama-sama nake jin sautin muryarta tana kiran sunana haɗi da girgiza ni “ HAROON ! HAROON ! Please ka tashi ! Innalillahi wa'inna ileyhi raji'un! ” ta furta kafin ta fita ƙila don neman taimako.
Fitarta yayi daidai da dawowar bugun zuciyata,na buɗe murfin motar na soma kelaya amai kamar raina zai fita.Ta zagayo tare da yin tsaye tana kallona,sai kuma ta je za ta tsallaka titi tana mai tsayar da mai sayar da ruwa .Manta wa na yi da halin da nake ciki na yi wani uban tsalle na jawo ta baya don kauce ta daga motar da saura ƙiris ta kaɗe ta.
Tamkar yadda in boom ta fashe take ɗaga mutum sama ta cilla shi gefe haka ce ta faru da na jawo Malama Zainab,sai da muka yi sama ni da ita kafin mu faɗa can gefe kaina ya bugu da dutse yayin da ita kuma ta faɗo kan ƙirjina gaba ɗayanta.A wannan karon babu wani jinkiri ruhina yayi nisan zango daga wannan duniyar na fita daga hayyacina ban ƙara sanin abin da ya faru ba.
A ruɗe Malama Zainab ta tashi daga jikin HAROON idonta na kawo ruwa,mutanen da ke bakin hanya ne suka matso.Ita ɗin ba wata ɓoyayya ba ce a garin Yamai wannan yasa cike da girmamawa suka fara tambayarta ba'asi.
“Yayana ne ya faɗi ne