Showing 18001 words to 21000 words out of 43872 words

Chapter 7 - SURUKATA HORROR BOOK COMPLETE DOCUMENT 2025.txt

27 Dec 2024

3500

auren ba mai moruwa ba ne amma da ɗan sassauci kan rayuwata ta gida.


Kalamansa ne suka katse min tunani inda yake cewa,“ Zahra na san ba ki sona an aura miki ni ne bisa dole,sannan kuma yanzu da aka kawo ki sai kika ƙara tsanata saboda larurar da kike tarar ina da ita.Ki yi haƙuri da sannu za ki saba za ki ga kamar ma yana ɗaya daga cikin aikin da kika fi so na wankin kayan fitsarina,abu guda na sani kina da lada don ni mijinki ne sannan aure dukkansa bauta ce.Allah ne ya ɗora min babu yadda na iya,ba wai zaɓina ba ne duk da farko abin ya addabi ruhina har ya taɓa aikin da nake saboda ina tsoron yin bacci a cikin abokai na yi fitsarin kwance.Shawarar Mama ce da nake bi nake ganin canji,ita ce ta ce min kar na damu da duk halin da zan samu kaina Allah bai ɗorawa bawa abin da ba zai iya ɗauka ba,sannan in na je can mission inda zan yi bacci cikin mutane na saka a raina ba zan yi fitsarin ba,kuma kin san abun mamaki hakan take faruwa fa sosai nake jin daɗi” ya ƙarashe maganar yana sakin murmushi mai sauti yayin da kuma yake shafa gadon bayana.




“Amma kuma sai in ka zo nan gida ne kawai fitsarin yake dawowa?” na samu kaina da tambayar shi.


Ya bani amsa da “ eh! Amma ko a gidan ba kullum ba ne nake yi”


“Ita kuma ɗayar matsalar fa?” na tambaya a kunyace,shiru yayi bai bani amsa ba sai da aka ɗauki lokaci kafin ya ce “ wace matsala kenan?”


“A'a ko ɗaya ,zan yi bacci” na faɗa jin yana son raina min hankali wato fitsarin kwance kawai ya ɗauka a matsayin matsala shi rashin kusantata da ya kasa yi ba matsala ba.




“Zahra don Allah kar ki guje ni kin ji?” ya faɗa yana wani ranƙwafowa kamar mai leƙen fuskata.Na turo baki gaba kafin na ce “ kar ka damu Janiki ba ta taɓa yin farin ciki ba dama,ina tabbacin cewa sanin zan iya zama da kai suka haɗa aurenmu” na yi furicin hawaye na surnano min.




Hasken ɗaki ya kunna tare da yin zauna ,sosai nake jin idonsa a kaina duk da na juya masa baya.
“Ki bani labarinki” ya faɗa .
“Aliyu ba ka jin bacci ne halan?” na faɗa cike da takaici.
Ya ce “ me yasa ba ki jin kunyar faɗar sunana gatsal? In banda Hajiya babu wanda ke kirana da shi kai tsaye”


“To ai sunanka ne” na basa amsa a takaice.
“Kenan ba zan samu alfarmar da za a kira ni da wani sunan ba?” ya faɗa ,ni kuma na yi banza da shi.Tun ina tunani har bacci ya ɗauke ni, washegari ko da na farka ban gansa ba.Wanka na je na yi na canza kaya sannan na share ɗakina da kuma kewayena na kunna turaren tsinke.


Ina tsaka da goge ledar ɗaki sai ga sallamar Binta,bayan mun gaisa ne take tambaya ta “ me za a dafa?”


Tsuru-tsuru na yi mata don ban san me zan ce ba,a yadda ma na ga duk ranta a haɗe babu fara'a sai na ji kuma duk babu daɗi.


“Ban san dalilin da yasa Hajiya ta baki muƙamin nan ba,alhalin kaf gidan nan ni ce mace ta farko da aka fara aurowa.Amma an bai wa ƙanƙanuwar yarinya damar juya mu hum!” Binta ta faɗa tana wani kallona.




“Ki yi haƙuri Binta ki dafa duk abin da kike so” na faɗa murya na ɗan rawa.Ta ja tsuki kafin ta fice na bi bayanta da kallo,ina nan tsaye sai ga Aliyu ya shigo sanye da kayan gudu da dukkan alamu daga motsa jiki yake.




“Barka da warhaka!” na faɗa ,ba tare da ya amsa ba ya wuce har can bedroom da takalminsa na gudu waɗanda suka ɗauko ƙasa.Haka na ƙara bin wurin na goge,ko da na shiga ciki na tarar tuni ya soma wanka.


Bakin gado na zauna ina kallon ƙofar toilet ɗin,babu jimawa ya fito ɗaure da towel a ƙugu muna haɗa ido na sunne kai.


“ Ki zo ki fitar min da kayan da zan saka,sannan ki fara shirin zuwa Coci don da wuri zan ajiye ki na wuce wurin aiki” ya faɗa cikin dakakiyar murya,da na ɗaga kai na dube shi kamar ma ba shi yayi maganar ba.




Na miƙe na tsaya gaban drower kayansa,yadda na gansu jere ras sai na rasa wane zan ɗauko masa.
“Wane kake so?” na tambaye shi tare da juyowa ina kallonsa.


“In har na faɗa miki to mene ne amfanin zaɓar min ɗin da kika yi?” ya faɗa wannan karon cikin taushin murya har da wani zuwa a bayana yayi tsaye kamar mai shirin rungumo ni.


Hannuna har rawa yake wurin ciro masa wasu kwat baƙaƙe da kuma rigar ciki blue.“ Ka sa waɗannan za su yi ma kyau” na faɗa ina dubansa,ya langaɓar da kai kafin ya ce “ kin tabbata?” na gyaɗa masa kai.
Ya ce “ ni fa baƙi ne”
“Duk da haka za su yi ma kyau” na faɗa sai ya karɓa ya je ya ajiye su bisa gado sannan ya soma shiryawa,ni dai ina gefe ina kallonsa har ya gama.




Na ce “ saura turare ko?” ya ɗan yamutsa fuska ya ce “ yau ban son jin ƙamshinsa”sake da baki na yi ina kallonsa.
Sai na yi saurin fita falo jin muryar Hajiya Luba ,“ ina kwana Mama?” shine abin da na fara faɗa da na je,ta amsa cikin sakin fuska kafin ta ce “ ina Aliyu?”


“Yana ciki shiryawa yake”
“Yau ba ki yi wanki ba ne?” ta jefo min tambayar da ta bani mamaki,na ɗan dube ta kafin na ce “ yanzu zan yi”


“Na zata ko tun jiya kika yi cikin dare” ta ƙara faɗa tana ƙanƙance ido.Na girgiza kai, sai ta wuce bedroom ɗin ta bar ni nan tsaye ,babu jimawa suka fito ita da Aliyu tana gaba yana biye da ita a baya har suka fice . Sosai nake mamakin wannan kusanci nasu don ba haka take da sauran ƴaƴanta ba,a haka na je na yi shirin tafiya Coci.Direct kuma sai na fita zuwa ɗakin cin abinci,a zaune na tarar da su tana basa wasu magunguna da ke jere cikin faranti zinare.
Na samu wuri na zauna,babu jimawa kuwa mutanen gidan su ma duk suka zo don tuni Binta ta kawo abincin breakfast.






Bayan kowa ya zauna na tsawon kamar minti biyar haka , Hajiya Luba ta ce “ ƴata Janiki ki bada izinin cin abinci mana ”
Sai na ɗaga kai na dubi kowa,Binta ta yi kicin-kicin da rai alamun ba ta so ba .Amma haka na bi umarnin Hajiya na buɗe kwanon,yau ma wainar ce irin ta jiya da ɗan mamaki na dubi Binta sai na ga tana murmushi da ban san na mene ne ba,sai dai ko kafin na ɗora ayar tambaya Hajiya Luba ta rige ni “ yau ɗin ma wainar aka yi?”kana jin amon muryar za ka fahimci ranta ya ɓace .


“Janiki ce ta ce na yi,sai da na faɗa mata mu nan ba kasafai ake yinta ba amma ta ce babu ruwana ai ita ke da damar zaɓar abin da za a dafa ” Binta ce ta yi saurin faɗar haka,nan kuwa Hajiya ta wani maido dubanta gare ni.A tsorace na soma i'ina ,“ dama...dama” sai kuma na yi shiru tare da sunne kai ina hawaye,don a duniya babu abin da na tsana kamar a yi min ƙazafin abin da ban yi ba.


Ruwan hawayena na ɗiga kan capet sai kawai wani iska ya tashi labulaye suka soma tashi sama yayin da kuma hotunan Hajiya duk suka faɗo ƙasa,a can waje ma kana jiyo ƙarar faɗuwar abubuwa,duk sai hankali kowa ya tashi muryar Hajiya har rawa take wurin cewa “ ki yi haƙuri Janiki ki bar duk wannan abubuwan”




Ina ɗago fuskata Binta ta fasa uban ihu tare da dafe wuyanta muryar dakyar take cewa “ ki..kikiki yi haƙuri wallahi sharri na yi mata”


Tana faɗar haka na ja sanyyyar ajiyar zuciya,nauyin da na ji ƙirjina yayi ma duk ya ɗauke.Kamar kuma almara haka komai ya tsaya cak,ni sam ban fahimci cewa saboda raina ya ɓace ne hakan ta faru ba.




Hajiya Luba ta ja wata ajiyar zuciya kafin ta ce “ to kowa ya ci abinci” nan muka soma ci,bayan mun gama kowa ya fita yau ma yayi saura mu uku sai dai ba ta bani komai na sha ba sai ƴar nasiha da ta soma yi min.


“Ƴata Janiki ki dinga controling fushinki ,sannan ba komai ne yake sa mutum ya fitar da ɓoyayyar siffarsa ba”


Ba tare da na fahimci abin da take nufi ba na ce “ to Mama”
Ta saki murmushi ta ce “ Aliyu tashi ku tafi”
Haka muka miƙe muka fito,sai da muka koma ɗakinmu duk muka yi brush kafin mu fita can waje inda motarsa take,duk da ba irin waccan ba ce ta miliyoyin kuɗi amma tana da kyau sannan duk garin ba za su wuce su biyar ba masu motar hawa.
Gidan gaba na shiga ya ja ni zuwa Coci,har muka isa bai yi min magana ba.Har can ciki ya shiga da ni,ya samu wuri yayi parking kafin kuma ya juyo ya dube ni.Da sauri na sunne kai,ya kamo hannuna tare da cewa “ ki kula da kanki sosai kin dai ji abin da Hajiya Mama ta faɗa ko?” na gyaɗa kai tare da buɗe murfin na fita,cak kuma na tsaya ina kallon abubuwan da can farko ban ganinsu ban ma san lokacin da Aliyu ya bar wurin ba.
Idona ne na soma jin suna wani irin zafi tare da sauya kala suka koma baƙaƙe ƙirin,inuwar mutum na gani ina ɗago kai muka haɗa ido da father.


“Janakiii?” ya faɗa hankali tashe kafin ya riƙo ni,ido na rumtse gam jin tamkar ya jona min wutar lantarki.Amma a haka ya ja ni zuwa can ciki ya zaunar da ni,“ ina Cross ɗin da na baki?” ya jefo min tambayar ,sai yanzu na tuna tun bayan da aka sa na cire ta ranar da za a yi min lalle ban sake ganinta ba.


“Tana ga Mama” na basa amsa.Bai ce komai ba ya fita,babu jimawa kuma ya dawo tare da miƙa min wani kofi ya ce “ ungo ki sha” na karɓa kuwa ba tare da na tambaye shi ba na sha,ko minti ɗaya ba a ɗauka ba na soma jin ana yi min motsi cikin ciki ta ko ina kafin na ɗuka na soma kelaya amai.Sosai na yi mamakin yadda na yi aman baƙaƙen tsutsotsi kuma duk da ransu sai motsi suke.


Hankalin Father sai na ga ya ƙara tashi,ya tsure ni da ido na wani lokaci kafin ya je ya ɗauko wata kwalba mai kamar turare ya fesa cikin aman da na yi nan fa na ga abun almara yadda wurin ya kama da wuta har sai da komai ya ƙone ƙurmus wutar na tsayawa kuma aman ya ɓata.




“Ban san cikin me kika jefa kanki ba Janiki,amma tun ranar da kika rera waƙar nan na ga wata ɓakar inuwa mai tsaurin ido na biye da ke.Tabbas inuwar nan na da ƙarfin tsafi tun da har ta iya shigowa cikin coci a kuma ɗakin bauta” a cikin kalamansa babu abin da na fahimta,kuma kafin na kai ga tambayar shi sai ga motar Aliyu ta sake dawowa da sauri na je gare shi.


Gidan gaba ya buɗe min na shiga,ba tare da ya ce komai ba ya figi motar a tsiyace.Muna isa gida kamar wacce ta yi laifi haka ya wani fincike ni zuwa sashen Hajiya ,muna shiga a falon nata a yanayin da na ganta kawai na fahimci da tabbas na aikata mata wani babban zunubi wanda kuma take shirye da ɗaukar tsatsauran mataki a kaina.Daidai nan free page ya ida duk mai son ci gaba sai ya biya kuɗin karatunsa.






My book is only 500 via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank


DM +22795045822
[26/12 à 09:33] MRS SADAUKI: *MAFIYA*☠️


01


‘ Lokacin da muna yara,da zarar an ce MAFIYA kawai abu guda kwanyata ke bani ƙungiyar shan jini ce mai sa a yi kuɗi.Amma yanzu da na girma,na kuma tsinci kaina a ciki sai na fahimci cewa MAFIYA na nufin cikar muradi.
Sunana HAROON matashi ne ni ɗan kimanin shekara talatin da takwas a duniya,maraya na uba ,shalelen mahaifiyata.Na taso cikin matsin rayuwa ta talauci kafin kuma na tsinci kaina cikin daula...... '




“Haroon sakatariyarka ta ce yau ba za ka fita ba ko zan san dalili?” muryar Ammy ta katse mini ɗan taƙaitaccen tunanin zucina wanda kusan lokuta da dama nake zama haka kawai ina bai wa kaina labarin kaina.


Na saki murmushi ina kallon sanyin idaniyata abar alfaharina,“ ban jin daɗi ne Ammy shi yasa,amma kar ki damu ciwon kai ne kawai”


“Kamar ya kar na damu ? Ciwon kan ne kake faɗa ƙaramin abu? Jira ni ina zuwa” ta faɗa tare da yin gaba.


Na bi ta da kallon ƙauna,Ammyna kenan uwa ta gari wacce a idonta sam ba na girma kullum tamkar ƙaramin yaro haka take ɗauka ta.Ina nan zaune ta dawo hannunta riƙe da wata tasa da kuma ƙaramin towel,na lumshe ido lokacin da ta soma tsoma towel ɗin a ruwa tana matse shi sai kuma ta dinga dadanna shi a kaina.Cikin ikon Allah na ji ciwon kan yayi sauƙi,“Ammy ya isa haka je ki huta mana ban san yaushe za ki daina ɗawainiya da ni ba,kamar wani ƙaramin yaro dai sai ririta ni kike” na faɗa ina mai riƙe hannunta mai ɗauke da towel ɗin.




Ta dungure mini goshi cikin faɗanta da ta saba yi min ta ce “ sai ranar da ka kawo matar aurenka a gidan nan.Wai HAROON yaushe za ka yi aure ?”


Da sauri na miƙe ina mai cewa “ aure! Aure dai kullum shine zancenki Ammy,duka nawa nake?”


“Yanzu na haife ka” ta bani amsar da ta saka ni dariya,sai kuma na ce “ kar ki damu zan nemo miki suruka kafin ƙarshen shekarar nan in sha Allah!” na furta ina mamakin furucina na ƙarshe da na ambaci sunan maƙagina,wanda a ƙalla zan kai shekaru biyar da muka yi hannun riga ni da umarninsa.Yanzu haka ambaton sunansa sai da na ji maƙogorona yayi min wani zafi,halshena kuwa tamkar an saka reza ne an tsaga shi.






“Allah ya nuna mini wannan babbar rana, Ubangiji yasa ina da rai albarkacin Manzon Rahama Ya Rabb ka dubi Harunana ka basa mata ƴar aljanna mai haska duk wani duhun gidansa” ita ce addu'ar Ammy gare ni,ban ko amsa ba na yi gaba abina.




Ina fitowa harabar tsakar gida direbana yayi saurin tashi tare da nufar motar da a yau ita ce zan shiga.Da kansa ya buɗe mini gidan baya na zauna,sannan ya ja motar. Hanyar babban ofis ɗina ya ɗauka amma na yi saurin dakatar da shi.“ Ka ga kai ni wurin da zan ɗan shaƙi iska yau ban ra'ayin aiki ko kaɗan ” na faɗa don haka kawai nake jin yau raina a dagule babu daɗi ga wani irin bugawa da zuciyata take.






Gudu yake da ni amma hankalina ba ya ga hanya na lula sosai cikin tunani,ƙiiiii ya ja wani uban burki sai a lokacin na dubi gabana.Wata kyakkyawar budurwa na hango tana tsallakar da yara ƴan makaranta,yayin da duk ababen hawa suka tsaya suna jiran sai yaran sun gama wucewa.




“Yi haƙuri yalaɓai bari na canza hanya” cewar direba ,da sauri na ce “no ! Jira” ido kawai na tsura mata yadda take ta zulumniya cikin ƙaton hijabinta ,yayin da hannunta kuma wanda ya sha jan lalle ke faman kamo na yara.




Ido na lumshe sa'ilin da ta game dukkan hannuwanta alamun godiya ,ban san mun bar wurin ba sai da na ji direba yana cewa “ba don Malam Zainab ba ce da ƙila mutanen nan ba su tsaya ba sai an samu waɗanda za su ce sai sun wuce”


“Ka san ta ne dama?” na samu kaina da tambayarsa.


Yayi ƴar dariya ya ce “to wane ne zai ce bai san Malama Zainab ba,yarinyar da duk shekara ita ce ke cin gasar musabaƙa ta duniya.Makarantar can ma gwamnati ne ya buɗa mata ita da sunanta,yalaɓai in ka ji yadda ɗalibanta ke yin larabci kai kace ƙyanƙyasar Saudiya ce uwa uba ita in tana yi.Zaƙin muryar.....”




“Ya isa haka juya ka mayar da ni gida” na yi saurin katse shi saboda bugun zuciyata da na ji sai ƙara hauhawa yake.Muna isa gida ko wani burki mai kyau bai yi ba na yi saurin fita daga motar ba tare da na jira ya buɗe min ba.




Ammy na falo ta ga na shigo a hargitse,ta yo kaina tana tambayar lafiya amma ban bata amsa ba na haye step ina taka shi bibiyu yayin da ita kuma ta mara min baya tana faman kiran sunana.Ina isa ɗaki kuma na rufe shi gam da key,ga ƙofar na jingina ina sauke numfashi kafin dakyar na ƙarasa na je na zauna kan kujera ina kallon kaina cikin baƙin madubin da shine silar canza rayuwata daga jiya zuwa yau.A zahiri ni mutum ne complet,amma a cikin madubi ba komai ne ba face ƙwarangwal ba tsoka saboda da kaina na sayar da ruhina ga MAFIYA.........
[26/12 à 09:33] MRS SADAUKI: *MAFIYA*


02


Karon farko kenan da na yi da na sanin shiga MAFIYA,a tsawon shekarun da na yi a ciki na yi su ne cikin farin ciki.Hawayen takaici nake yi yayin da ƙwarangwal ɗin da ke cikin madubi ke ƙyartata dariya,ita ƙwarangwal ɗin nan ba kowa ba ne face Ni,inuwata ce ko kuma na ce ruɓaɓen ruhina.Daga can bakin ƙofa ina jin Ammy na buga wa tare da kiran sunana amma na kasa tashi ,zuciyata ta yi rauni ba zan iya tsayuwa gabanta ba na shaida mata alƙawarin da na yi mata na samo matar aure ne ya cika sai dai kuma baƙin ruhina da farin ruhin kyakkyawar budurwar nan sam ba za su iya zama a inuwa ɗaya ba saboda rayuwar da ta rage min ƙalilan ce.






Wayata ce ta ɗauki ruri,ina dubawa na ga sunan Oga.A dole na ɗaga,“ ka zo muna da meeting ɗin gaggawa” shine abin da ya faɗa kafin ya kashe.


Jiki babu ƙwari na miƙe na shiga toilet na wanke fuskata na goge ta da towel sannan na fito.A bakin ƙofa na ga Ammy idonta sun yi jawur,na sakar mata murmushi na ce “ kar fa ki damu kan ki zan nemo wata tun da wannan ɗin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login