Showing 21001 words to 24000 words out of 38502 words

Chapter 8 - BAWAN ALLAH COMPLETE DOCUMENT BY Maman Muhammad .txt

20 Dec 2024

2531

ta tace"Aunty Ummi kefa ake kira"




Jiki a sanyaye Ummi tabi bayan shi har zuwa office d'in mutum , ita dai bata taba ganin shi ba amma , gashi kallon da yake mata kad'ai yana sa hanjin ta juyawa ,


Mutumin ya kalli Wanda suka shigo tare ya ce masa "you can go"


"Ok Sir" matashin ya bada amsa tare da barin office d'in




Juyawa yayi ya kalli Ummi wadda da ka ganta Kasan a firgice take "zauna mana 'yammata" yafad'i tare da nuna mata kujerar dake opposite d'in shi ya ,


Cikin sanyi ta zauna ,


Murmushi yayi sannan yace " Malam Zainab nasan baki sanni ba amma ni nasan Ki kuma ina bibiyar Ki , Ki bani dama in yaye miki k'unci da kewar dake addabar zuciyar Ki"




Cikin zaro ido da firgici Ummi tace "Subhanallah nifa matar aure ce"


Ido ya kanne mata irin nasu na 'yana duniya yace "karki damu Zainab dama ba aure zamuyi ba kawai zamu d'an huta ne mu mori junan mu "


Ummi kam salati kawai take ta faman rafsawa


Shikuwa k'aton banzan sai ya sake ce mata "karki damu babu Wanda zai San meke faruwa a tsakanin mu daga ni sai ke , kuma nayi miki alk'awarin samun nasara arayuwar duk abinda kike buk'ata indai kud'i nayin shi zanyi miki "




Cikin hasala ta fara magana "kaico kaico shin da kake cewa babu mai ganin mu Allah da ya hallice mu fa? Idan ka manta bari na tuna maka , Allah ne ya hallice mu baki d'aya Dan haka ko k'asa muka hak'a muka shige Allah yana kallon mu kuma baka isa kai D'an Adam kayi Katanga tsakaninka da mahaliccin ka ba, kuma ka sani bana buk'ar taimakon wani abun hallitta balle kai azzalumi Allah ne gatana kuma shi na dogara shi kad'ai zai biya mun buk'atuna "




Wata dariyar mugunta yayi sannan yace" duk kalaman Ki bazasu sa na chanja k'uduri na a kanki ba baby kin had'u , Ki taimaka min na lashi zumar nan"




Wani bak'in ciki ne ya turnuk'e Ummi gashi tana so tayi kuka ta kasa kai sai ta mik'e zata fita , takai dai dai wajan k'ofa tajiyo muryar shi yana cewa "baby na baki kwana biyu kije kiyi tunani Idan baki amince ba kuma duk abin da ya biyo baya ke kika ja"




Wani dogon tsaki taja tare da fad'in "Allah ya fika "ta fita


Shiko jingina yayi yana jin sha'awar ta yana k'ara azazzalar shi,




Ita kuwa Ummi kanta ne yake juyawa nan ta lallab'a wa tana tana tafiya a hankili Chan sai ta fara ganin duhu ba tare da tasan inda take ba ta duk'e awaje ta jingina da glass d'in da yake hanyar mutane basu cika wuce wa sosai Shiya sa ta d'au tsawon lokacin da ita kanta bata san lokacin da ta d'auka awajen ba,


Kamar daga sama taji wata sassanyar murya tana fad'in "Baiwar Allah lafiya kike zaune anan ?"


Ahankali ta d'ago kanta tare da sauke idanun ta akan matashin kallo d'aya tayi mai ta sake kauda kanta domin gaskiya guy d'in ya had'u ga iya dressing fa kyau kuma da ganin alama iyayen sa masu k'unbar Susa ne ba tare da Cewa komai ba mik'e wa tayi har ta juya zata tafi sai kuma taji ya k'ara cewa " Sis ga jakar Ki"


Ba tare da ta juyo ba ta karb'a tare da fad'in "thanks"


Murmushi yayi tare da biyo ta abaya yana fad'in "Suna na Aminullah Alhassan ina department of business administration ina two hundred level"




Bata bashi amsa ba sai ma k'ara sauri da tayi , domin ita duk atunanin ta shima shed'anar yazo mata dashi,


Sake jin muryar shi tayi yana cewa " tunda dai ba zaki yi sharing k'uncun Ki dani ba to Dan Allah ki saurareni bai kamata kitafi kina d'auke da fuskar shanu ba" ya k'ari ke yana murmushi ,


Ita ko kalaman shi na k'arshe yasa ta juyo wa daidai lokacin kuma ya saki murmushi


"Me kake nufi da fuskar shanu?" Ta k'ara tamke fuskarta


D'aga kafad'ar shi yayi sannan ya ce "ba abinda nake nufi ,amma da zaki runk'a yin dariya tauraruwar Ki sai ta fi haskawa"




Ta bud'e baki zata yi magana kenan ta ji an tab'o ta ta baya rud'e ta juya , Hafsa ce tsaye sai nishi take kamar wadda tayi gudun famfalank'i duk da yana yin da Ummi ke ciki taso tayi dariya amma sai ta daure tace


"Ke kuma fa lafiya? kinzo sai nishi kike kamar wata zakanya"




"Eh dole Ki ce haka mana bayan duk kin gama ba mutane wahalar nemanki for more than an hour Ashe kina nan"


"To ina ruwanki da nema na ko ni yarinya ce da zan b'ata?"


Cikin b'acin rai Hafsa tace "naga Wanda ya fiki shekaru ma ya b'ata har yanzun ba labarin shi bare ke , to Ki sani ko kin b'ata ba zanje Neman Ki ba"




Nan Ummi ta had'a girar sama da k'asa tsabar bak'in ciki ma ta rasa me zata ce


Hafsa na ganin hakan tasan k'awar tata fushi tayi kawai sai ta rungumeta tana lallashi cikin sigar tsokana har sai da tayi dariya sannan ta jata suka bar gurin




Shiko Aminullah tunda suka fara yake kallon su har suka tafi yana binsu da ido , ahankali kuma ya furta "I love your dramer"
[1/4, 8:49 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com




2⃣9⃣➕3⃣0⃣










Tunda suka koma gida Hafsa ta lura Ummi tana cikin wata damuwar da tafi tada tana so ta tambaye ta amma kuma ta kasa , wani tunanin ne kuma ya sake bijiro matashin saurayin da ta ganshi tare da Ummi meye tsakanin su?, ita dai takan Ganshi amma ba kullum ba kuma tana Ki k'ayenta na yawan yin zancen akan suna son shi, wata zuciyar kuma tana cewa karki zargi k'awarki domin kema kinsan ba halinta bane , daga k'arshe dai ta yenke shawarar zuwa ta tambayeta ,




Koda ta Shiga d'akin ta sameta a zaune atsakiyar katifa ta had'a kanta da gwuiwoyin ta tana kuka bilhak'i da gaskiya ,


Azuciyar Hafsa ko cewa tayi "ita kam Aunty Ummi kuka baya mata wuya" k'arasawa tayi kusa da ita cikin tausayi ta dafa kafad'ar ta , har wannan lokacin Ummi bata d'ago ba ,




Cikin sanyin murya Hafsa tace "k'awata me ke damun Ki ne ?, ko maganar da na fad'a miki d'azun ne?"




Girgiza kai tayi alamar "A'ah "


Hafsa ta sake cewar " to mene ne ? Kinji yadda jikin Ki yayi zafi kuwa?"




Cikin kuka Ummi ta sanar ma da Hafsa abin da wannan lecturer d'in ya fad'a mata har had'uwar su a Aminullah ,




"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un lallai wannan anyi D'an iska , insha Allah ba zai samu nasara ba "


Nan dai Hafsa tayi ta kwantar mata da hankali har ta D'an saki ranta ,


🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼


*THE NEXT DAY AT SCHOOL*




Bayan sun samu interval d'in lecture suka fito waje suna shan iska ita ko Ummi zuciyarta cunkushe yake da fargaba domin bata San me zai faru gobe tsakanin ta da wannan shed'anin ba,




Hafsa ce ta gaji da shirun tace " Aunty Ummi ba dai tunanin wannan fasik'in kike ba ?"




Ajiyar zuciya Ummi tayi sannan ta ce " dole inyi tunanin shi mana Hafsa kaidin wani mutum d'in yafi sharrin shed'an"


"Hakane amma Allah ba zai bashi galaba a kanki da yardar Allah"




Ummi ta bud'i baki zata yi magana kenan taji wani k'amshi ya doki hancin ta juyawa tayi ta kalli Hafsa taga ita ma ita take kallo a tare suka d'aga idanuwan su suka zuba kan Aminullah, nan da nan dukkan su suka d'auke Kansu ,


A cikin Takun da baifi uku ba ya k'araso inda suke tare da sallama ,


A dak'ile suka masa mai murmushi yayi sannan ya ce "sisters ya kuke ?"
Ba samu amsa daga bakin Ummi ba sai dai Hafsa ce tace "lafiya " itama a dak'ile ta amsa ,




Kallon Ummi yayi yaga ta wani d'auke kai murmushi yayi yace "sis ba dai fushin jiya ya shafe ni ba?"


Nan ma bata tanka mai ba sai ya koma kusa da Hafsa kujerar da ke kusa da ita ya zauna tare da fad'in "sis wai me ke damun k'awar Ki ne tun jiya nake ganin ranta a b'ace jiya da k'yar nayi bacci saboda halin da na ganta ciki"


Hafsa ko baki ta saki azuciyar ta tace "lallai wannan bashida hankali "


Daya ji shirun yayi yawa ne yace "au kema shiru zaki yi ?"


Wata zuciya ce tace ma Hafsa Ki fad'a mishi abinda ke faruwa ko zai iya temaka muku,


Nan ta bashi labarin komai daya faru ,


Cikin b'acin rai yace "ya sunan lecturer ?"


Shiru tayi tana so ta tuna sunan da taji an fad'i jiya da k'yar ta tuna


Ta kalli Aminullah tace "D'an Asabe"


Murmushi mugunta yayi yace" hakane na tuna jiya akusa da office d'in shi na ganta dama kuma ina da case dashi double fire kenan "


Matsawa yayi kusa da Ummi ya ce "karki damu sis insha Allah daga kanki bazai k'ara marmarin zina ba ",


Da k'yar ta iya cewa "nagode"


Sallama yayi musu tare da fad'in "ku jira result zuwa gobe "ya Shiga motar shi domin k'arasawa department d'in su




Ummi ce ta juya ta ce ma Hafsa "ke banza ce wallahi ya kawai daga ganin mutum zaki zauna Ki saki baki kina ta surutu , to yanzun da kika gaya mishi me zai iya yi?"




"Haba Aunty Ummi Ki fahimceni ni ba da wata manufa na fad'i mai ba kawai gani nake zai iya taimakawa amma idan banyi miki dai dai ba to Ki yafeni"




Ajiyar zuciya Ummi tayi tare da fad'in "shikenan ya wuce" nan dai sukayi ta hirarrakin su daga k'arshe suka koma class ,




Shiko Aminullah tunda ya tafi yake shirya k'ulum botom da zai shirya ma D'an Asabe cikin murnar samun mafita yace "zaka ci ubanka" ya saki wata dariyar mugunta,




🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼




*AT NIGHT*


Wata dalleliyar mota ce k'irar CRV ta faka a parking space din Quarters d'in lecturers da ke cikin makarantar b'arayin me zaman banza da b'arayin driver aka bud'e , wasu matasa ne guda biyu cikin bak'ak'en kaya d'aya yana zuk'ar segret d'ayan kuma yana tofar da miyau gami da toshe hanci yana fad'in "wallah kai banza ne nagaya maka bana son warin wannan abar amma saboda tsabar iskanci sai ka shata a gabana ".




D'ayan yace "guy charge nake domin naji dad'in karta rashin mutum ci ",


Dai dai nan suka isa inda suke son Shiga , tab'a k'ofar sukayi suka jita a bud'e , sai d'ayan ya cema mai shan segret d'in ya lek'a ta window'n' ko akwai matsala , bayan minti biyu ya dawo yace"ya sama kanshi jaraba ba dole ya manta ya bar k'oda bud'e ba yana chan yana shanawa"


Cike da takaici d'ayan yayi k'wafa ahankali suka tura k'ofar suka Shiga tare da lab'e wa abayan wata kujera dake lungu ,


Sai alokacin na gane waye d'ayan Ashe Aminullah ne , tab


Lokaci zuwa lokaci suna duban agogo suda suka zo tun k'arfe goma gashi gashi yanzun shabiyu , d'ayan ya bud'e baki zai yi magana kenan suka ji an bud'e k'ofa lakwaf sukayi wata budurwa ce ta fito cikin wasu tsinannun English wears sai wani taku take cikin yauk'i , sai da wuce da kimanin minti talatin sannan suka mik'e suka kashe kulle k'ofar har zasu bud'e k'ofar bedroom d'in sai abokin Aminullah yace tayani mu harmutsa d'akin nan sai da suka ma d'akin biji-biji sannan suka kashe globe d'in d'akin suka fad'a bedroom d'in




🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣
[1/5, 9:22 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*




*MRS NN ONE💋*






® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*


_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_




# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com






3⃣1⃣






Ko da suka Shiga d'akin yana kwance akan gado ya lullub'e da alama barci ya fara yi , Aminullah ne yayi ma abokin shi nuni da ya zagaya ta d'ayan b'arayin koma ya nemi kan bedside drower ya zauna tare da d'ora k'afa d'aya kan gadon , sunsa D'an Asabe a tsakiya ,




Wata 'yar k'aramar wuk'a Aminullah ya Ciro a aljihun shi me kama da ta wanzamai , ahankali yake yawo da wuk'ar akan wuyan D'an Asabe , mak'wat ya had'iye wani miyau chan dai dayaji waiwayin ya isheshi sai ya kawo duka zafin da yaji a hannunshi shi ya sashi farkawa ciki magagin bacci azabar dake k'ara ratsa shi ne yasa shi bud'e ido me zai gani jini ne keta zuba a hannun shi cikin firgici ya d'aga kanshi yayi tozali da Aminullah wani wawan mari ya sakar mai yanda sai da ya daina gani na 'yan sakwanni , wata muguwar dariya ce yaji abayan shi yana juyawa yaji an sake d'auke shi da wani Marin cikin firgice ya fara fad'in,




"Wayyo Allah na Dan Allah me na miki?, su waye ku?"




Cikin wata irin murya Aminullah yace " zakasan ko mu su waye , zaka San ko me kamana amma sai kayi laushi tukun , oya come down my friend!"




Jiki na rawa ya sakko a gadon kamar Wanda beda jini ajikin shi ,


Abokin Aminullah ya ce "maza kayi frog jump sau hamsin"


Cikin zarana D'an Asabe ya ce "Oga ina da matsalar ciwon k'afa fa "




"Keep quite sanda kake turmushe 'ya'ya da matan mutane kana tuna k'afarka na ciwo ne banza kawai" ya had'a mai da wani Marin ,


Chan kuka ga D'an Asabe yahau tsallen kwad'o , shiko Aminullah gefe ya koma ya barshi da gwaska




A wahale D'an Asabe yayi frog jump ashirin shima yana yi ya tuntsurawa dukkan ninsu dariya suke ta cikin k'yallen da suka rufe fuskokin su , sai da wahala sannan Aminullah ya taso daga inda yake yace "guy tale min shi namai kaciya ".




Nan D'an Asabe ya hau muzurai da ido jikin shi sai kyarma yake ,




Nan guy ya Fara kici-kicin cire mai wando , cikin magiya D'an Asabe yace "Dan Allah Dan Allah kar ku min wallahi anmin tun ina D'an shekara bakwai"


Wata harara guy ya wurga mai sannan cikin k'arfi ya ja gajeran wandan ya yi k'asa , hankalin shi be k'ara tashi ba sai da yaga Aminullah yayo kanshi da Aska AI ba shiri ya zabura zai gudu gajeran wandon shi ya tad'iyeshi ya fad'i ji kake TIM!! , D'an Asabe yasha k'asa , da dai yaga har yanzun k'ara Mateo shi yake AI sai ya tak'ark'are yayi parlour a guje haba basai wani sabon satin ba ji kuke k'um! Gwaram !!,


D'an Asabe ko na chan parlour yana cin karo da kayan d'akin da aka yamutsa idan yayi sai yaci karo ko ya hantsala ,




Sukam su Aminullah suna chan suna jiyo ihun shi , sukam sai dariya suke ci ma'ishin su sai da suka gama dariyar sannan suka fita parlour suka kunna switch d'in gloves d'in D'an Asabe ne zigidir a tsaye tsakiyan center table sai muzurai yake fuskar nan duk ta kumbura ga wata uwar zufa da ke ketomai kamar yayi gudun famfalank'i




K'arasa wa suka yi kusa da shi sannan Aminullah ya fara magana "wato kai k'wallan D'an iska ko iskan cin naka ya koma kan matan aure ko to kad'an ma ka gani muddun zaka ci gaba da irin haka"


Cikin rawar baki D'an Asabe yace "wallahi yallab'ai indai wannan ne na daina amma Dan Allah ku k'yale ni haka"




Cikin tsawa guy yace "kai! Kana tunanin zamu tafi ne bamu tab'a lafiyar jikin ka ba to kayi k'arya "damk'o shi yayi turmushe yace "Man zo ka D'an sha jinin shi"




D'an Asabe sai zillo yake amma ya kasa k'wacewa , yana ji yana gani ajikiyi mai siririn yanka ajikin shi sannan suka k'ara mai da gargad'in yaje ya ba Zainab Kabir k'uri in na haka ba next time kaciya zasu mishi




Jiki na rawa yace" wannan duk mai sauk'i ne ai "


Suka tafi suka barshi suna ta shek'a dariya




🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣




Washe gari da yake juma'a su Ummi basu da lectures d'in safe Dan haka sai k'are biyu suka je school suna Shiga class sai ga wani yazo ya ce" Zainab Kabir taje inji Malam D'an Asabe " sosai firgici ya bayyana a fuskarta , tana cikin tunani sai taji mutum akan ta Aminullah ne tsaye cikin manyan kaya brown d'in shadda ne ajikin shi anyi mata aiki da coffee din zare hular kanshi ma ratsin coffee da brown Kasan ce warshi fari sai abun ya k'ara sajewa farar fatar shi murmuahi kawai yake mata yayin da d'ayan hanunshi yake sanye cikin aljihun shi , ahankali ya matso kusa da ita yace " minti biyu please" yana gama fad'in hakan ya juya ya fita ,


Hafsa ce ta kalleta tace "Aunty Ki je mana maybe ya Samar mana mafita ne "


Jiki a sanyaye ta fita yana hangota sai ya fara tafiya ahaka har sai da suka kusan office d'in D'an Asabe sannan ya tsaya tana K'araso wa ya fara magana a hankali ,


"Karki ji tsoro kije hak'uri kawai ze baki , na ruga da na gama da shi" ya k'arike maganar cikin murmushi




Kallon shi tayi sannan tace "Anya wannan ba wani *SABON SALON YAUDARA* bane kuka zomin dashi?"




Cikin sanyin murya yace "Ki yarda da ni Zainab bazan tab'a cutar da wata 'ya mace ba most especially ma ke da nake so kinga bazaki je ba shikenan dama hak'uri zai baki"




Ummi wata fassara tayi daban cikin tsiwa tace" owoo dama badan Allah zaka taimaka min ba saboda na kub'uta a hannun kai na fad'o naka hannun ko , to bari kaji idan baka sani ba ni nan da kake ji da gani matar aure ce na wuce na tsaya kuna ball dani kuyi duk abin da kuka ga zaku iya ni *DA ALLAH NA DOGARA* " tana kai wa nan ta koma da baya tana tafe tana share k'walla har ta bangaje Hafsa da tazo Neman ta tafad'a ma anshiga ajinsu ita kuma ganin Ummi ta wuce a fusace kamar zakanya chan kuma ga Aminullah ya d'ora hannayen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login