Showing 3001 words to 6000 words out of 38502 words
Chapter 2 - BAWAN ALLAH COMPLETE DOCUMENT BY Maman Muhammad .txt
ya iya zama , ballan tana kuma Amarya?"
Mik'e wa yayi zaune yace "ya Allah ga Bawan ka nan mak'ask'anci daga cikin bayin ka ya Allah ka taimake mu ya Allah kafi kowa sanin halin da muke ciki " wasu k'walla masu zafi da tuk'uk'i a zuciya suka zubo mai ,
Da k'yar ya had'iye wani Abu mai kama da dutse a wuyan shi ya koma ya kwanta ,
Chan kuma yayi zumbur ya mik'e ya nufi gana most go d'in kayan shi ya ciro wani gwangwani , nan ya bud'e kud'i ne a ciki , nan ya hau k'irgawa , naira dubu takwas da d'ari biyar ne , ajiyar zuciya yayi sannan ya mai da kud'in ya ajiye , da yamma bayan sun had'u da Umar a islamiyya yake gaya mishi yadda suka yi da Malam
Umar sai da yayi dariya mai isarsa sannan ya ce " wato kai yanzun aure za'a maka ?, auren ma na dole"ya k'ara k'yalk'yale wa da wata dariya har yana rik'e cikin shi
Abdallah da yaga abin na Umar da rainin wayau aciki kawai sai ya mik'e ya fice ya bashi wuri ,
Umar ya biyo shi yana "ustaz tsaya mana ya muna magana zaka gudu kuma"
Abdallah be kula shi ba sai ma ture hanun Umar da yayi a kafad'ar shi cikin fushi ya k'ara sauri,
Umar na ganin haka ya ce "yau maza sun yi fushi , sai naje biko"
Abdallah kuwa yana shiga afusace ba kowa a tsakar gidan sai wani bokiti da aka cika shi da ruwa aka aje ,
Aiko ya suri bokitin yayi bayi dashi , haka ya ringa watsa ruwan a kanshi yana ajiyar zuciya ,
Hafsa kuwa ta fito d'aki daga ita sai zani tana 'yan wak'e- wak'en ta da sosan wanka a hannun ta ta k'arasa inda bokitin yake yace d'aukeni inda kika aje ni ,
Ta ringa zagaye a tsakar gidan tana fad'in" anan fa na ajiye shi "
Mama da ta fito da buta za tayi alwalar magrib tace"ke hafsa ke dawa kike ta surutu kamar kanki be miki dad'i"
Hafsa cikin muryar kuka tace "Mama ruwa na na ajiye a bokiti zanyi wanka na fito ban ganshi ba"
Mama tace "yanzun hafsa ba na hana Ki wankan magrib ba?"
"Mama to AI wankan tsarki zanyi gashi lokacin sallah ya kusa "
"Uhum" kawai Mama tace
"Duk ma aljanin da ya d'auka ya fito dashi kafin......."hafsa bata k'arasa maganar ba taji an buga mata wani Abu akai ta baya , tana juya wa taga Abdallah ne ya buga mata bokitin da take nema , AI sai ta hau kame -kame
"Dalla ni rufe min baki mare kunya kawai" ya sakar mata bokitin a k'afa
Aiko tayi tsalle tana "wayyo Mama ya karya ni"
Mama kam bata bi ta Kansu ba ta gama akwalar ta ta shige d'aki
*DA SAFE*
Abdallah yakai ma Malam sadaki bayan ya nuna ma Mama tasa albarka , na n Malam ya sa ranar d'aurin aure kwana goma kuma ya ce baya buk'atar komai ,
Abdallah yayi godiya sosai ya tafi
[12/14/2017, 8:13 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*Dedicated to BAWAN ALLAH fans group ina jin dad'in comments d'inku so let's keep it up*❤
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
5⃣
Kuyi hak'uri readers wasu na k'orafin ban fad'i wacece hafsa ba
Hafsa yarinyar wan Mama ce taje garin su dai-dai lokacin aka hafsa ta isa yaye sai aka bata ita ta taho da ita , da wan nata yaga ta nuna sha'awar a bar mata hafsa sai ya amince wannan ne dalilin zaman hafsa agurin Mama
Cigaban labari
Da biki ya rage saura sati d'aya Mama ta shirya domin zuwa k'auyen su Dan ta sanar ma 'yan uwa su , kud'in aikin da Abdallah yayi na ranar shi ya d'auka ya bata ta tafi ,
Alokacin da taje musu da zancen sun ji dad'i sosai har ma wan nata ya ce da lokaci be k'ure ba da sun zo sun ma Malam godiya , kwanan ta biyu ta ce zata koma aikuwa aka shiga had'a mata kud'i da kayan abinci Allah Sarki da taga abinda aka had'a mata sai da tayi kuka hatsine buhu guda aka mata sai kuma kud'i nai ra dubu hamsi , Mama tayi kuka har tace ba zata amshi kud'in ba sunyi yawa , Baban hafsa ne ya ce mata "idan ba kin raina bane Hindatu Ki karb'a" da haka ta karb'i kud'in tare da godiya ta dawo gida cike da murna da jin dad'i,
Abdallah ma kanshi ya ji dad'in ganin kud'in
Ranar talata da safe suna zaune sai Mama ta ce "Bawan Allah ya kamata ka gyara d'akin chan naka tun da dai ba wani sai shi "
"To " kawai yace
"Ke hafsa shiga Ki d'auko min lalita ta a d'aki" Mama ta fad'i tana nuna hafsa
Bayan hafsa ta kawo lalita Mama ta kwance ta Ciro kud'in nan ta mik'e mai ta ce ya k'irga
Ya gama k'irga yace "dubu hamsin ne Mama "
Tace"to ka dauki yadda zai isheka ka gyara d'akin chan kafin dangin Amarya su buk'aci sa wani Abu "
Nan ma "to" yace
"Haba bawan Allah ina ta magana kayi shiru sai dai ka Bini da to"
Cikin sanyin jiki Abdallah ya ce "Wallah Mama jiki name duk a mace gani nake duk yarinyar da aka had'a ta dani an cuce ta domin ba zan k'are ta da komai ba sai k'uncin rayuwa"
"Kayi hak'uri Bawan Allah , Allah da yayi mu ahaka bai manta da mu ba , wani hanin ga Allah baiwa ne sai dai kawai muyita gode ma Allah," Mama ta fad'i tana share k'wallar da ta gangaro mata
Abdallah kuwa ji yayi tuk'uk'in da yake ji sai k'aruwa yake
Umar ne ya shigo da sallamar shi , duk suka amsa , bayan gaishe-gaishe Mama ta ce
"To kaga ga Umar nan yazo tashi kuje Ku hanzarta lokaci na tafiya "
Nan dai ya mik'e jiki ba k'wari suka fita , suna fita Umar Umar ya dasa shak'iyyan cin shi ya fara " Ango Ango kasha k'amshi "
Ni irin kallo Abdallah ya masa sai Umar ya had'iye yawu , daga nan ya tsuke bakin shi be k'ara cewa komai ba
Siminti suka siyo da katako sai kuma net da penti suna dawo wa suka hau aikin abin su ,
Ba su suka gama ba sai dare sannan Abdallah ya bi Umar d'akin shi Dan ya kwana
Da safe
Misalin k'arfe shad'aya na safe wasu mata su biyu shigo gidan da sallama
Mama na tankad'an gari , hafsa na hura wuta ,suka amsa musu sallamar sannan suka k'ara sa shigowa wasu yara ne yan matasa biyu suka shigo da da wasu manyan ledoji guda biyu
D'aya k'anwar Malam ce d'aya kuma yayar amaryar Malam d'in ce
Da fara'a a Mama tace "ah 'ah sannun Ku da zuwa yaya ma'u"
"Yauwa"suka amsa suma cikin fara'a ,
Hafsa ce tayi sauri ta d'auko tabarma ta shimfid'a musu suka zauna ,
Bayan gaishe gashe suka ce sunzo gyara d'akin Amarya ne , nan Mama ta nuna musu d'akin suka hau gyara ,
Leda duka shimfid'a ,suka sa labule ,
Suka rufe d'akin suka Mama makullin kwadon suka yi sallama
Hafsa ce ta ce ma Mama "Mama komai yana son gyara kinga yadda aka gyara d'akin yaya kamar ba shi ba "
Mama tace " shiyasa aka ce mana tsafta cikon addini"
Hafsa ta ce" lallai kam , Mama bari naje na duba Ummi kwana biyu bana ganin ta a islamiyya"
"Aiko nima ta kwana biyu bata zo gidan nan ba ko lafiya ?je Ki dubo ta"
Hafsa ta suri hijab d'inta ta fita
*Wace ce Ummi*
Ummi ita kad'ai ce 'ya mace ga Malam wadda Amarya sa ta Haifa masa asalin sunan ta ZAINAB k'awar Hafsa ce tare suka taso
*cigaban labari*
Bayan sun gama d'aukar karatu a wajen Malam Abdallah yace
"Malam lafiya Ummi bata zuwa makaranta kwana biyu?"
Malam yace "Ummi bata jin dad'i ne amma dai ta ji sauki "
Dukkan su suka yi mata fatan alkhairi suka kwashi littattafan su suka k'ara gaba
*Ranar d'aurin Aure*
Yau take juma'a kuma da an idar da sallar juma'a ne za'a d'aura auren Abdallah da Amaryar sa ,
Abdallah kuwa yau tun safe da ya tashi yake fama da wani matsanan cin ciwon kai ga jiri da yake gani , Umar har fita yayi yaje ya siyo mai magani ya sha amma a banza , sai da Umar yayi ta mai addu'a sannan ya samu yayi barci ,
Umar kuwa da yaga Abdallah yayi barci wanka yaje yayi sannan ya shirya cikin yadin shi mai sauk'in kud'i ya fita wajen daurin auren amma me kafin ya k'arasa har an d'aura ,
Malam ne ya k'araso wajen da Umar ke tsaye yana mamakin har an d'aura aure
"Umar ina abokin naka yake?"
"Wallah Malam yana can d'akina kwance yana fama da zazzabi amma dai yanzun yayi barci" Umar ya bada amsa
Cikin tausayi Malam yace " subhanallah Allah ya sawak'e"
Nan suka zauna suka CI gaba da tattaunawa
Gidan su Mama cike yake da mutane 'yan biki , yamma nayi kowa ya fara watse wa Dan 'yan garin su ma motar da ta kawo su tana jiran su , Dan Baban hafsa yace ba zasu zo su d'ora mata d'awai niya ba ,
Hafsa ce ta shigo a guje ta ce ma Mama " Mama ga Ummi can an sata a napep za'a kaita asibiti ciwon ta ya tashi"
"Hasbunallahu wani'imal malwakil , Ummi Allah ya yaye miki wannan lalura" Mama ta fad'i cikin jimami
Hafsa ta k'ara cewa" Mama bari na bisu"
"Ah'ah hafsa baki San asibitin da zasu je ba kiyi hak'uri ki jirasu"
Hafsa ba Dan taso ba ta hak'ura , domin tasan ciwon k'awar tata idan ya tashi har suma take yi
Allah Sarki Ummi Allah Sarki Abdallah😥🤫
[12/15/2017, 11:17 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*wannan page d'in ma naku ne ina matuk'ar k'aunarku kamar yadda kuke k'aunar BAWAN ALLAH*❤💋
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
Page 6⃣
Abdallah be farka ba sai wajen k'arfe shida na yamma , yana duba agogon wayar shi yaga lokacin sallah yayi yamik'e cikin sauri ya d'auki buta yayi cikin gidan , Maman su Umar ma bata nan , tana can gidan biki , alwala yayi ya fara jero azahar da la'asar bayan ya idar yayi addu'oi sannan ya fito ya kulle gida ya gangara Neman Umar ,
Yana cikin Neman shi ne yaji ana kiran magrib , kawai sai ya wuce massalaci , sai da aka idar da sallah yazo zai fita yaji an dafa kafad'ar shi yana juya wa yaga Ashe Umar ne ,
Murmushi ya masa ,
Shima Umar murmushin yayi sannan ya ce "Aboki ya jikin naka?"
"Alhamdulillah"abdallah ya amsa ,
Sannan suka jero suna tafiya ,
Anan ne Umar yake gaya ma Abdallah Malam yana Neman shi , daga nan kai tsaye gidan Malam suka nufa , amma da suka je aka ce Malam yaje asibiti duba Ummi ,
Cikin hanzari Abdallah ya kira wayar Malam , ringing biyu aka d'aga , banji me aka ce a d'ayan b'angaren ba naji Abdallah ya ce "to Allah ya kawo ku lafiya "
Banyan sunyi sallar issha sai suka Kama hanyar gida , Anan suka had'u da Malam shima ya dawo massalaci Dan basu ganshi a can ba ,
Bayan sun gaisa malam yace "Abdallah ya jikin naka?"
"Alhamdulillah Malam na samu sauk'i , ya jikin Ummin?"
"Jiki yayi sauk'i tana gida ma yanzun haka "
"To Allah ya k'ara lafiya"
"Amin" Malam ya amsa , sannan ya buk'aci su biyo shi rumfar k'ofar gidan shi ,
Bayan sun k'arasa sun zauna Malam ya fara magana,
"To Abdallah yau dai Allah ya nuna mana ranar da ka zama cikakken mutum , domin shi aure shi ne yake cika kamalar D'an Adam , ina fatan zaka yi hak'uri ka zauna lafiya da duk macen da ta Kasan ce matar ka , kuma kayi hak'uri da halin yarin tarta , na zab'a maka ita ne saboda nasan cewar zaku zama natsuwa a tsakanin junan ku, inai maka fatan alkhairi , Allah ya Sanya albarka acikin wannan auran yaba ku zaman lafiya da zuri'ah mai albarka Amin"
Tunda Malam ya fara koro bayani jikin Umar da Abdallah yayi sanyi lak'was , Abdallah duk jarumtar shi sai da k'walla ta zubo mai ,
Umar kuwa bubbuga bayan shi yayi
Abdallah ya fara magana cikin rawar murya " insha Allah Malam bazan baka kunya ba , zab'in ka shine nawa tamkar mahaifi kake agurina nagode Allah ya saka da alkhairi "
"Ba komai Abdallah da kai da Umar kun chan-chanci fiye da haka aguri na , Allah ya jikin iya-yen ku ya k'ara kyautata mak'wancin su"
"Amin "dukkan su suka ce nan Malam ya k'ara yi musu nasiha , sannan ya ce su tashi su tafi dare na dad'a yi , har sun mik'e sai Malam yace ,
"Abdallah sun kai maka Amaryar ka tun d'azun ba kowa ma agidan"
"To" d'in da ya saba fad'i ita ya fad'i yanzun ma , suka yi sallama suka fita
Suna fita Umar ya shek'e da dariya " yau abokina zai angwance kai Allah ya samu a danshin ku"
Abdallah Ya kawo hannu zai kai masa duka kenan Umar ya gudu yana fad'in "Aboki karka rufe k'ofar gida zan kawo ma Mama sak'on ta"
Bai bi ta kanshi ba ya kulle k'ofar gidan ya shige abin sa ,
Yana shiga yaga Mama da hafsa suna kwance a tsakar gida suna fira Kasan cewar ana D'an zafi lokacin
Da sallama ya shiga , duk suka amsa masa ya janyo bokiti ya zauna yana fad'in
"Ina wuni Mama ?"
"Lafiya lau " ta fad'i yana k'ok'arin mik'e wa zaune
Sannan ta k'ara cewa "ya jikin naka?"
"Alhamdulillah naji sauk'i"
Nan suka D'an tab'a fira sannan Mama tace mishi" su zasu shiga su kwanta dare yayi "
Mik'e wa yayi yaje kusa da hafsa ya shure ta da k'afa sannan yace " ke baki iya ma mutane sannu bako?"
Cikin murya me kama da ta barci tace "yaya barci fa nake"
"Dallah rufe min baki tunda ga waje nake jiyo hirar Ki Ki ce min wai barci kike yi"
Mama kuwa tunda suka fara ta kakkab'e tabarmar ta ta shige d'aki
Yana ganin mama ta shige ya juya ya kalli hafsa "to uwar gulma ko anan zaki kwana ne?"
Pillow d'inta d'auka ta runtuma d'aki aguje.
Tsaki yaja , ya nufi k'ofar d'akin shi , yana isa ya d'aga labulen tare da sallama , mutum ya gani kwance cikin hijab cire takalman sa yayi ya k'arasa shiga d'akin ,
Azuciyar shi yace "lallai ma wannan baccin ta ma take sha"
Pillow ya ja ya kwanta ak'asan Leda , can dai yaji bazai iya hak'uri ba yana son ganin wace ce amaryar tashi , zaga ya wa yayi ta inda fuskarta ke kallo , ganin ko wace ce ya sa shi yin taga-taga zai fad'i
Masu karatu kunsan wa ya gani 😱
Cikin tsananin mamaki yace"Ummi?!"
To fa muje zuwa Dan jin yadda zama zai Kasan ce tsakanin Ummi da Abdallah
[12/16/2017, 9:38 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
Page 7⃣
Jingina da bango yayi yana k'are ma Ummi kallon mamaki , bawai baya son Ummi bane , Ummi macen rufin asiri ce , yasan halin Ummi akwai hankali natsuwa da sanin yakamata uwa uba kuma tarbiyya , Ummi mace ce San kowa k'in Wanda ya rasa , tana da kyawu dai-dai gwar-gwado ba za'a kirata da mummuna ba , ita ba fara bace kuma ba za'a ce mata bak'a ba zamu iya kiran ta chocolate colour , ba tada tsawo sosai kuma ba gajera bace sannan yatsunta suna da tsawo , tana da dogon hanci da yalwatattun idanuwa ba tada fad'in fuska sosai, gakuma D'an k'aramin bakin ta , kai masu karatu Ummi kyakyyawa ce ba laifi🙅🏾♀
Wani gwauron numfashi ya ja ya zame agurin ya zauna yana kallon ta kamar wata sabuwar hallita ,
Ya kai kusan awa biyu a wurin yana kallon ta azuciyar shi yace "tabbas Ummi kyakyyawa ce amma me yasa yau naga kyanta ya fita daban, ? mutane suna ciwo suyi muzai-muzai , amma Ummi kyau ta k'ara ko ita din ta daban ce ko kuma ido nane ?"
Duk wad'an nan tambayoyin ba shida amso shin su Dan haka kawai mik'e wa yayi , ya fita yayo alwala ya raya daran da sallah ,
Ummi kuwa juyin barci tayi ta farka wani irin mugun fitsari taji ya matse ta , ga tsoro tana ji ba zata iya fita waje ita kad'ai ba sai matse matse take , Abdallah kuma alokacin ya idar da sallah yana jiran yaji an kira sallar asuba yana jingine idon shi a lumshe amma ba barci ya ke ba ,
Ummi kuwa da taga idan bata je tayi fitsarin nan ba to tabbas zata malale sabuwar katifar ta da fitsari ,
A hankali take kiran sunan "yaya Abdallah ? Yaya Abdallah? Yaya Abdallah?"
Shi kuwa ya na ji kasa amsawa yayi sakamakon wani Abu da yaji yana sukan zuciyar sa , ana ukun da ta kira shi ne ya daure ya ce mata
"Na am"
"Fitsari nake ji"
"To kije kiyi mana "
Cikin d'auriya da matse fitsarin tace "wallahi tsoro nake ji "
Azuciyar shi yace " ko a gida wake raka ta oho?"
Afili kuma sai cewa yayi" kiyi addu'a ki fita babu abin da zai same Ki da yardar Allah"
" wayyo Allah yaya zai zubo"
Dafe kanshi yayi a zuciya ya ce "ni kam naga ta kai na "
Azahiri kuma yace " tashi muje "
"To kayi gaba"ta fad'i cikin shagwab'a
Gaba yayi ya barta a baya tana tafe tana hard'e k'afafuwa , har ta isa nesa da bakin bayin ya tsaya tare da mik'a mata buta , sannan ya ce" adai yi addu'a "
"Uhum" kawai tace ta k'ara sa bayin aciki ma ta k'ara sa