Showing 12001 words to 15000 words out of 38502 words
Chapter 5 - BAWAN ALLAH COMPLETE DOCUMENT BY Maman Muhammad .txt
"
Ogan yace fito min dashi na ragaje shi kawai zagayowa yayi ya damk'o wiyan Abdallah ya fito dashi dai dai lokacin idon Abdallah yakai kan Umar dake kwance jini yana ta zuba a hancin shi da alama suma yayi fincikewa yayi daga ruk'on da suka mai ya tafi wajen Umar aguje yana fad'in "Umar meya same ka ta...." Wani irin zafi yaji Wanda saida jini ya fito ta hancin shi Ashe bakin bindiga suka buga ma a kai
"Muzaka yi ma taurin kai to ba irin mu ake yima ba" haka suka yita dukan Abdallah duk da ya suma basu k'yale shi ba , saida suka tabbata sunyi mishi babbar illa sannan suka k'yale shi
Matan kuwa Dama su biyu ne nan suka tasa k'eyar su suka tafi dasu mazan kuma suka barsu kwance tare da k'wace duk wata dukiya dake tare dasu
[12/26/2017, 8:56 AM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*This page is mine💃💃 💃💃happy anniversary to my self I hope you ga _ys will wishes me*_ 😘🏌♀
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
Kasan cewar dare ne kuma wurin ba wurin tsayawar mutane bane shiya sa basu samu temako ba sai da safe , wani me mota ne yazo wuce wa yaga mutane kwance kamar mattatu , nan da nan ya d'aga waya ya kira 'yan sanda , ba b'ata lokaci aka kwashe su sai asibitin Aminu kano , direct emergency aka wuce da su ,
Da bincike da bincike kowa D'an uwan sa ya runk'a zuwa amma banda mutum biyu , wato Umar da Abdallah , Umar ya farka sai dai be San inda kanshi yake ba , Abdallah kuwa har yanzun bema ko motsa ba, likitoci suna iya k'ok'arin su akan shi domin duk ciki ya fisu shan a zaba,
*ZARIA*
Ummi , Mama da kuma Hafsa kowa yayi cirko-cirko a tsakar gida , kowanan su da a binda yake sak'awa acikin ransa , iya k'ololuwar tashin hankali suna cikin su ,
"Ummi sake Kiran wayar muji" Mama ta fad'i cikin wata murya me ban tausayi
Ummi jiki ba k'wari ta danna number Abdallah , still a kashe wasu hawaye ne suka sake yi mata ambaliya a fuska ,
"Aunty Ummi swich up ko?"
Ita dai Ummi d'aga kawai tayi domin Sam ta kasa bada amsa ,
Haka suka zauna a wajen har kusan k'arfe biyu na dare , Ummi ce taga kukan ba zai fisheta ta ba ta mik'e ta d'auki buta yau ko tsoron ba ta ji , ta nufi bayi , tana fitowa ta d'aura alwala duk sai suka bita da ido , Mama a zuciyar ta tace "wannan ita kad'ai ce mafita"
Duk sai sukayi alwala suka shige d'aki, kowa ya kai kukan shi ga Allah Wanda shi kad'ai ne buwayi gagara misali mai biyan buk'atun bayin sa,
Koda safiya tayi suna zaune a tsakar gida sunyi jigum gidan tamkar ba mutane ,
A haka Maman Umar ta shigo da sallama Wanda da ganinta ita ma Kasan batayi kwanan dad'i ba , bayan sun gaisa sama-sama sai tace
"Wai yaran nan basu dawo bane? "
Mama cikin jimami tace"wallahi bamu gansu ba jiya kwana ne kawai ba muyi a tsakar gidan nan ba "
"Inalillahi wa inna'ilaihir raji'un, ya Allah ka sa muji alkhairi" cewar Maman Umar
"Amin " duk suka amsa
Hafsa ce tace "Mama ya kamata aje a fad'a ma Malam ko da temakon da zai iya yi"
"Hakane Hafsa kinyi tunani me kyau , yanzun tashi kije Ki sanar mishi "
"To Mama" ta mik'e jiki ba kwari ta fita ,
Ummi kuwa wata alwalar ta sake yi ta nufi d'aki ,
Mama ta kalli Maman Umar tace " ina jin tausayin kaina ina jin tausayin yarinyar nan jiya haka ta kwana banda kuka da sallah babu abin da take yi "
Maman Umar tace "wallah jibi yadda duk ta susuce , Ya Allah ka bayyanar mana da yaran"
"Amin" dukkan su suka amsa
Bayan Hafsa ta sanar ma da Malam halin da ake ciki ba shiri ya bazamo ya taho gidan Dan jin cikakken bayani ,
Mama ta fara magana "wallah Malam tunda suka fita jiya babu su ba labarin su har yau"
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un , ai ni Da naga ban gansu a masallaci ba da asuba inace ko gajiyar hanyace , Allah ka bayyanar mana da su"
"Amin" kowa yace
Dai-dai nan Ummi ta fito daga d'aki Dan ta jiyo muryar mahaifin nata , ahankali ta tako gefen Hafsa ta zauna tare da gaishe shi , bayan ya gaisa ya fara yi musu nasiha tare da kwantar da hankali , gami da cewar" Idan har dare yayi basu dawo ba to gobe shida wasu almajiran shi zasu tafi kano Neman su"
Nan dai sukayi godiya ya tafi ,
Mama ta kalli Hafsa ta ce "je Ki dama ma Ummi koko tasha magani"
"Mama nak'oshi"Ummi tace tana kifa kanta akan gwuiwoyinta
"Baki CI komai bafa Ummi rabon Ki da abinci tun jiya da rana shi d'in ma ba wani ci ka kayi ba kina ta jagwal-gwalawa , "
Ummi dai shiru tayi
Maman Umar tace " haba Ummi Ki yi hak'uri ko kokon Ki sha kinga ba lafiya ce ta wada ce Ki ba "
"To"kawai tace
"Ke Hafsa je Ki damo mata"
Wasa-wasa har dare ba wani chanji hakan yasa Malam ya nemi biyu daga cikin manyan almajiran shi da su raka shi kano , safiya nayi kuwa suka bazama,
*_kano_*
Tunda likitoci suka yi iya bakin k'ok'arin su akan Abdallah cikin ikon Allah numfashin shi ya dawo amma kuma gashi nan kwance kamar gawa , wani Babban Doctor suka kari yazo ya duba shi , koda yazo yaga Abdallah Sam ya kasa d'auke idanun shi a kansa , wani Doctor ne ya matso kusa yana magana
"Ka sanshi ne Doctor?"
Shiru yayi yana tunanin abinda zai ce sai kuma yace"ina 'yan uwansa suke?"
Nan wancen Doctor din ya kwashe duk tsautsayin da ya faru da su Abdallah ya fad'a masa ,
Cikin tausaya wa Doctor ya ce "wannan yaron wani mak'oci nane , ayi masa duk abinda ya dace",
Suka chanja Abdallah d'aki , ana fita dashi Umar ya farka , babu Wanda ya fara kira sai Abdallah ,
Bayan ya D'an huta suka fara yi mishi tambayoyi kamar haka
Wani Doctor Usman ya fara cewa "ya sunan ka?"
"Umar" a tak'aice ya bashi amsar
"Inane garinku?"
"Zaria"
"Mekazo yi a kano?"
"Munzo Sarin kaya ne nida d'an'uwa na Abdallah"
Doctor Usman ya maimaita Kalmar "D'an uwa fa kace?"
"Eh" inji Umar yana dad'a kallon Doctor d'in
"To gaskiya duk cikin Ku ku goma da aka kawo babu Wanda 'yan'uwan shi basu zo ne manshi ba sai kai"
"A'ah likita indai ina cikin asibitin nan to na tabbata Abdallah na ciki iyayen mu d'aya da shi "
"To mudai kai kad'ai ka rage mana anan "
Wani mugun fad'uwar gaba ne ya ziyarci Umar shidai yasan last seen d'inshi da Abdallah ya ganshi cikin mota tsaye kuma yaji sanda d'aya daga cikin 'yanfashin yayi magana akan Abdallah afili ya furta "innalillahi wa inna'ilaihirraji'un, Allah kasa ba sun tafi min da d'an'uwa na ba"
"Maybe sunzo basu gane ka bane dubi yadda ka chanja kammani gaba d'aya" Doctor ya fad'i yana nuna masa wani d'an k'aramin madubi
Daya kalli fuskarshi sai da gabanshi ya fad'i tabbas yasan ba kowa zai gane shi ba Dan ko shi kanshi badan yasan shine ajikin madubin ba daya k'aryata kanshi,
Doctor ne ya tsinke mishi tunani da cewa " idan ka haddace number d'aya daga cikin 'yan uwan ka kabani sai na sanar musu"
Shiru Umar yayi sannan ya tuna number Malam nan ya bada , alokacin Malam suka shigo garin kano wayar shi Nokia rakani toilet ta fara ruri , ganin bak'uwar lamba yayi cikin sanyin jiki ya amsa tare da sallama
Ad'ayan b'angaren ma aka amsa tare da fad'in "suna na Doctor Usman ina aiki a asibin Aminu kano dake cikin garin kano , muna da wani patient me suna Umar yace kai D'an'uwan sane"
"Alhamdulillah dama yanzun su muka zo nema"
Nan Doctor yayi ma Malam kwatancen inda zai same shi idan yaje asibitin , basu b'ata lokaci ba suka isa Kasan cewar asibitin yana farkon gari ne , koda suka k'arasa asibitin basu sha wahala ba suka samu Doctor Usman tunda akwai waya nan yayi musu jagora zuwa d'akin da Umar yake nan ya kaisu Malam cikin razani da tashin hankali ya k'arasa inda Umar ke jingine , gaba d'aya halittar shi ta sauya nan suka jajanta ma juna Malam ya tambaye shi labarin abinda ya faru , shi kuma ya kwashe ya sanar masa
"To ina Abdallah?"
Abinda Doctor dai ya gayama Umar shi ya gaya musu game da Abdallah nan hankali ya k'ara tashi har dare ana Neman Abdallah amma babu bayani
Washe gari da safe aka sallami Umar , suna ji suna gani suka kamo hanya ba tare da Abdallah ba kowa da zullumi acikin zuciyar shi , "me zasu ce ma Mama akan *Bawan Allah* ?????"
[12/27/2017, 8:23 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*To readers ina Wanda ya shirya zuwa kano Neman bawan Allah Sadiya neman bawan wa Allah Wanda rashinsa Sam baiyi mata d@d'i ba cikin sa'a ko ta samu abokan tafiya Maman sa'a tace ba'a barta a baya ba dole su nema wa Ummi farincikin ta , aceeya kuwa cewa tayi jirgin ya tsaya ajigawa ya d'auke , Amne kuwa da yake 'yar black stormach ce 🤪cewa ta ba inda za'a je saboda man fuel yayi tsada , Aunty axland ma tace ba'a barta a baya ba*🤣🤣🤣
❤ *Gaisuwar fatan alkhair agareku masoya masu bibiyar littafin bawan Allah sakon ku na fatan alkhairi yana isowa agarene nagode agaskiya bansan da bakin da zan gode muku ba amma kusa ni har cikin raina inajin dad'in yadda kuka amshi wannan litttafin nagode sosai Allah ya had'a fuskokin mu a aljannatul firdaus Amin ya Allah*❤❤❤. *one luv*😘
*Ameenart Nd fatima (MAMAN Sadeeq) wannan page d'in naku ne dama d'aukacin yan Bawan Allah fans , I really like your comments❤*
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
Page 21----22
Haka nan su Malam suka tattara suka koma Zaria ba tare Abdallah ba zuciyoyin su cike da zullumin me zasu gaya ma mahaifiyar shi da kuma matar shi , ahaka suka sauka a tasha suka hau napep , direct gidan su Umar suka wuce ,
Aiko Maman Umar na ganin shi sai kuka domin yadda ta Ganshi ba k'aramin firgita tayi ba nan k'annen shi suka hau ihu " yaya Umar oyoyo !"
D'an autan su ne ya fita da gudu yaje gidan su Abdallah Ummi na alwalar la'asar Mama na kofar d'aki Hafsa kuma tafito daga bayan gida ,
Yaron ya k'arasa kusa da Mama cikin zumud'i yake ce mata "Mama yaya Umar ya dawo "
Cikin zafin nama Ummi ta waigo tana kallon shi
Mama ko cewa tayi "da gaske ?!"
"Eh Mama amma ya dawo kanshi a d'aure da wani Abu"
AI nan Ummi ta yarda butar hannun da dama already akwai hijab ajikin ta AI sai ta nufi k'ofar gida ,
"Ke Ummi ina zaki je ?" Mama ta fad'i yadda taga Ummi zata fita kamar zautacciya
"Ina zuwa Mama "kawai Ummi tace tasa kai
Hafsa da sai yanzun ta k'araso waje sai k'wala kira tayi "Aunty Ummi jira ni"
AI ina AUNTY Ummi gudu-gudu sauri-sauri ta runk'a had'a wa ,
💔💔💔💔💔💔💔💔
*Kano*
Yau kwana bakwai kenan ana fama da Abdallah amma Sam be san ana yi ba gashi zuciyar shi tana aiki amma kuma gangar jikin shi bata motsi , duk sun sare da al-amarin shi,
Yauma kamar kullum likitoci ne zaune awani k'awataccen office suna tattaunawa akan Abdallah , wata nurse ta shigo cikin sauri ta fara gaya musu patient din room no 18 ya farka kamar jira suke nan suka mik'e cikin sauri suka k'ara k'ofar d'akin ,
A zaune suka same shi akan gadon ya sakko da k'afafun shi k'asa , ya rik'e kanshi dake tsananin Sara masa ,
Koda suka bud'e k'ofar suka shigo kallo kawai ya bisu dashi domin be tab'a ganin su ba ,
Doctor d'in nan ne da ya ce ya sanshi ya matsa kusa da shi ya fara magana
"Ni sunana Dr Ahmad , zan iya sanin naka sunan?"
Shiru yayi bece komai ba , Dr Ahmad ya sake cewa "ko zan iya sanin naka sunan?"
"Ban sani ba" ita ce amsar da ta fito daga bakin Abdallah
Dukkan su likitocin suka kalli junan su
Dr Ahmad ya sake jefa mashi wata tambayar "ya sunan garin ku?".
Girgiza kai yayi nan ma alamar be sani ba
Nan likitoci suka sake firgita wani likita ne ya ce mai "nan ina ne ?" K'are ma d'akin kallo yayi tas sannan ya runtse idon shi gami da matse hannun shi kamar zai kai naushi
Dr Ahmad ne yace su k'yale shi ya huta , nan suka yi mai allurar barci ya koma
💔
[12/28/2017, 7:26 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
🌹 *ZURI'A D'AYA*🌹
*BY UMMU BASHEER*
🌹 *Congratulation sister for successful completing your amazing book ZURI'A D'AYA more grace to your powerful elbow*🌹
🌹 *KEEP SHINING DEAR*🌹
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
#PMLWRITERS@GMAIL.COM
# WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
2⃣3⃣ 2⃣4⃣
Akwana bakwan nan kuwa babu abinda su Ummi suke sai addu'a , Malam sai da yaje kano sau uku amma duk bawani cigaba
Wata safiya ce Malam ya yi sallama gidan su Abdallah aka bashi izinin Shiga , bayan 'yan gaishe-gaishe da k'ara jajanta ma juna , sai ya k'ara da cewa
"Nayi istihara akan b'atan yaron nan alamu sun nuna yana nan da rai kuma cikin kyakyawan masauki sai dai akwai k'unci a tattare da shi"
Mama ta share k'walla ta ce " to Malam yanzun ya za'ayi?"
"Addu'a , Addu'a ita ce kad'ai mafita"
Nan dai suka cigaba da tattaunawa , Ummi kam tana d'aki duk tunani ya gama addabar ta shi yasa ma bata ji zuwan Malam d'in ba ,
*KANO*
Dr Ahmad ne zaune a office d'in shi tunani duk ya da meshi ya kasa samun solution akan damuwar shi,
Nan ya d'aga waya ya kira Dr Usman ba b'ata lokaci sai gashi ya iso ,
Bayan ya zauna ne Dr Ahmad ya fara,
"Dama akan maganar patient d'in nan ne yaron mak'oci na , ina so zan maida shi zuwa k'asar London domin duba lafiyar shi"
Ido Dr Usman ya zaro" you just say London?"
"Yeah ,any think?"
"No sir"
"OK yanzun ina son kuyi discharging d'in shi domin in samu gudanar da shirye shirye na cikin sauki ?"
"Ok sir insha Allah ba damu wa"
Nan suka yi sallama ya tafi ,
Kamar yadda Dr Ahmad ya buk'ata haka aka sallami Abdallah alokacin da ya tashi aiki ya shiga d'akin shi domin tafiya dashi
Yauma kamar kullum azaune ya same shi yayi shiru ba tunani yake ba domin ba shida abinda zai tuna
Da sallama ya shigo d'akin , Abdallah ya amsa mai sannan ya k'arasa shiga d'akin d'auke da murmushi a fuskar shi ,
"Abdallah tashi mu tafi gida "
Sunan da yaji an kirashi da shi sai da ya razana ya kasa tuna inda ya San sunan amma tabbas sunan yana da muhimmaci a wajen shi ,
Dr ne ya katse mai shirun shi da cewa "ko kafi so ka CI gaba da zama a nan ne kayi ta barci?"
Kai ya girgiza alamar baya so
"To tashi mu tafi"
Cikin natsuwa ya mik'e ya bi bayan shi ,
Suna fita daga d'akin suka CI karo da Dr Usman rik'e da wani file a hannun shi , yace
.
"Yawwa sir ga records din "
Nan ya karb'a tare da godiya nan Dr Usman ya raka su har bakin mota sannan ya juyo , shikuwa ya tada motar shi ya d'au hanya , hanyar gidan shi ya d'auka da ke cikin G R A gidan Babban gida ne kuma da kagani Kasan Wanda ya mallaki wannan gidan ba k'aramar dukiya gareshi ba ,
Flat ne guda biyu a gidan tangama tangama , bayan yayi parking motarsa ya fito Abdallah ma ya mik'e ya fito d'aya daga cikin flat d'in suka nufa shi dai Abdallah tafiya kawai yake batare Da yasan inda aka dosa ba, ,
Key yasa ya bud'e k'ofar d'akin sannan ya ba Abdallah izinin shiga , tun da Abdallah ya d'aga kai bai sauke ba har sai da yaci tuntub'e da center table , shiko Dr murmushi kawai yake sannan yace ,
"Nan d'akin ka ne akwai duk wani abun buk'ata aciki bari nasa akawo maka abinci"
Kai kawai ya gyad'a tare da zama acikin d'aya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun d'akin,
Tunani da yawa yake acikin ransa , wane ne shi?, waye kuma wannan mutumin? Waye Abdallah , sunan da yafi d'aga masa hankali kenan idan ya tuna,
Yana nan zaune Dr ya shigo shi da wani matashi d'auke da tire a hannu ,
Cike da mamaki matashin ya tsaya yana kallon Abdallah , sai da Dr ya daka masa tsawa sannan ya aje kayan abincin ya fita ,
Kusa dashi Dr ya ya zauna sannan ya dafa kafad'ar shi yace"Babana tashi muje na nuna maka d'akin ka kayi wanka lokacin magrib yayi "
Jin maganar sallah ya sashi saurin mik'e wa , wata k'ofa ya bud'e suka kutsa , bedroom ne na gani na fad'a tamkar a k'asar turai , duk kayan more rayuwa akwai gidan , directtoilet ya wuce da shi ya nuna masa yadda zaiyi amfani da komai sannan ya kullo masa k'ofar ya fita,
Cikin tsoro Abdallah ke wanka har ya gama ya fito kayan da ya cire ne ajikin shi ganin wasu kaya yayi an aje mai su akan bed nan ya cire na jikin shi ya sasu , k'ananan kaya ne sunyi matuk'ar yi mishi kyau asalin kyanshi da talauci ya b'oye duk sun bayyana, masu karatu zanso kuga *Bawan Allah*
Ko da ya fito pallor