Showing 18001 words to 21000 words out of 38502 words
Chapter 7 - BAWAN ALLAH COMPLETE DOCUMENT BY Maman Muhammad .txt
ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
2⃣6⃣
Mama ce zaune a tsakar gida ta zabga tagumi tana kallon Ummi da keta faman wanki , hak'ik'a yarinyar tana matuk'ar bata tausayi tayi aure amma bata San miye auren ba balle ta tantance dad'in shi , babu abinda ta tsinta a cikinshi sai wahala ita irin tata k'addarar auren kenan , can kuma ta mik'e kamar an tsikare ta , ta zari Hijab d'inta da ke sagale jikin k'ofa sannan ta juya ta ce ma Ummi "bari naje na dawo"
"To Mama adawo lafiya"
Mama na fita bata zame ko ina ba sai gidan su Ummi ta ci sa'a ta samu Malam yana nan bayan sun gaggaisa ta fara fad'in abin da ya kawo ta ,
"Dama Malam Maganar Ummi ne ya kawo ni"
Malam yace "to Allah yasa dai ba laifi tayi ba"
"Ko kad'an Malam Ummi bata laifi , sai dai mune muke k'ok'arin yi mata laifi"
"Kamar yaya kenan?"
"Malam tunda kaga har yanzun Abdallah bai dawo ba kuma gashi shekara har ta gota Dan Allah anema ma yarinyar nan sauk'i a raba ta da wannan auran"
Shiru Malam yayi sannan yayi ajiyar zuciya yace "maganar Ki gaskiya ne amma kafin mu yanke hukunci ya kamata muji ta bakin Ummin , Dan haka idan kin koma Ki turo min ita "
"To shikenan Malam mungode Allah ya k'ara girma"
Nan suka k'ara tattaunawa akan maganar sannan Mama ta yi musu sallama ta tafi ,
Mama kuwa bayan sallar isha ta kira Ummi tace mata taje Malam yana Neman ta , sai da ta D'an ji gaban ta ya fad'i amma kuma ta daure ta tafi ,
Kai tsaye cikin gidan su ta nufa bayan gaishe-gaishe suna D'an fira da k'anan ta a tsakar gida sai ga Malam ya shigo , Maman Ummi ta shimfid'a mai tabar ma ya zauna suka gaisa sannan ya k'ara da cewa " Ummi dama ba wani Abu bane yasa nakira Ki akan auran Ki ne da Abdallah shin kin yarda a raba ko kuwa zaki iya hak'urin jiran shi?"
Tunda Malam ke magana hawaye suke ambaliya a fuskar Ummi , ta kasa magana ,
Malam ne ya sake magana "ina jinki Ummi baki ce komai ba "
Ummi ta fara magana muryar ta na rawa " Baba Dan Allah karku raba ku D'an k'ara mai lokaci Dan Allah Baba"
Shiru Malam yayi domin ya fahimci 'yar tashi tana son mijin ta "shikenan Ummi mun k'ara mai shekara d'aya idan be dawo ba ko ba da yardar Ki ba za'a warware auren nan"
"Baba na amince na gode"
"Shikenan Allah yayi miki albarka shi kuma Allah ya bayyanar mana dashi"
"Amin" Ummi tace sannan kuma tayi shiru
"To tashi Ki tafi dare nayi ko kuma akwai Wani Abu ne "
Shiru tayi kamar bazata ce komai ba sannan kuma ta fara magana bakinta na rawa "Baba dama alfarma nake nema"
"Ki fad'eta ko menene indai bai sab'a ma addini na ba zanyi miki shi "
"Baba dama so nake Dan Allah ka barni na cigaba da zuwa makarantar boko"
D'agowa yayi ya kalli 'yar tasa cikin natsuwa sannan yace "Ummi ba nak'i kiyi karatu bane , ah'a imani ne yayi rauni a zukatan wasu , duk da cewar bani da kokwanto akan tarbiyyar da na baki , amma igiyar auran da ke kanki?"
"Insha Allah Baba nayi maka alk'awarin kare mutunci na ko ina da aure ko banda shi , Dan Allah Baba ka amince min karatun shi zai rage min damuwa"
Jinjina kai yayi tare da gamsuwa da zancen 'yar tasa sannan yace " kije zanyi shawara duk abin da na yanke zaki ji"
Godiya tayi sannan suka yi sallama ta Shiga d'akin Ummin ta , sukayi sallama sannan ta Shiga d'akin abokiyar zaman Umman nata ta fito ta koma gida ,
Da sallama ta Shiga Hafsa da Mama ne a tsakar gida sai kuma Umar da ke zaune gefe d'aya yana sharb'ar tuwan dawa miyar kuka da taji daddawa , dukan suka amsa mata sannan suka gaisa da Umar , tayi ma Mama barka da dare ta wuce d'akin ta ,
Katifar ta tahau ta yi matashi da pillow d'aya d'aya kuma ta rungume shi tsam ajikin ta kamar za'a k'wace mata shi , wasu zafafan hawaye suka gangaro mata a fuska a hankali ta fara magana " mijina *KADAWO GARENI* ( by Rafee'at D/Dukko) suna shirin rabamu , hakan yana nufin rabuwa ta har abada domin duk randa na aka katse igiyar auran mu na tabbata bazan moruba" nan dai tayi ta Sumbatun ta har bacci yayi gaba da ita
Kamar yadda ta saba karfe uku na dare take tashi ta gabatar da nafilfili har sai alfijir ya keto sannan ta had'a da raka'atanil fijri sannan bayan tayi sallah tak'ara da karatun littafi mai tsarki sannan ta fito tsakar gida Susan abinyi ita da sahibar ta, wannan itace d'abi'ar Ummi,
A b'angaren Abdallah kuwa karatun shi kawai yasa gaba ba ruwan shi da kula 'yan mata , kuma har sun gaji da naci idan ma suka dameshi har mari yake had'awa dashi , sau dayawa Saifullah yana k'ok'arin tank'wara shi amma ina Abdallah kaifi d'aya ne baya tank'waruwa , haka rayuwa take cigaba da wanzuwa atsakanin su,
Ab'angaren Ummi kuwa ranar wata juma'a Malam ya aiko mata da wata takarda a nannad'e a cikin Leda yaron yace mata gashi ita da Hafsa ,
Tana bud'ewa form ne na wata makarantar gwamnati ya sama masu , ai aguje ta ruga d'akin Hafsa tana k'wala mata kira ,
Saida ta Shiga d'akin sannan ta b'oye takardar tare da fad'in " nazo miki da albishir amma sai kin ban goro"
Hafsa da ta farka daga bacci ta fara magana had'e da mik'a "lallai AUNTY Ummi wannan al-amarin mai girma ne tunda na ganki cikin farin ciki"
"Ke nidai Ki daina b'ata min lokaci Ki bani goro nabaki albishir "
Hafsa tace "to naji zan siyan miki biscuit d'in nera goma "
Ummi ta bita da harara tare da fad'in " saboda kin maidani k'aramar yarin ya ko? To Ki bari lokacin da kika tanadi goron kizo Ki karb'i albishir d'in naki " ta kama hanyar k'ofa
Cikin hanzari Hafsa ta bi bayan ta tana fad'in " haba Aunty Ummi tawa , Aunty Ummi ta yaya Abda...."
Ummi ta katse ta tare da nuna mata form d'in dai dai nan Mama ta fito tana fad'in "hayaniyar me nakeji ne?"
Ummi ta gayawa Mama ko mene ne , Mama taji dad'i sosai sannan ta bi Malam da addu'ar fatan alkhairi sannan ta ce ma su Ummi suje suyi mishi godiya
@08165728746
[1/2, 7:22 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*Dedicated this page to you my k'awalli , Allah ya raya mana Sadeeq, kekuma Allah ya.....🤭 kindai gane ba sai na k'araso ba*🤣
❤ *Much love dear*❤
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
2⃣7⃣
Cikin sa'a Ummi da Hafsa suka fara zuwa makaranta , uniform d'in yayi musu kyau Kasan ce warshi Navy blue da white sunyi matuk'ar kyau a cikin shi , SSS1 aka sasu , Kasan cewar makarantar tana da d'an nisa da unguwar su amma sabo tsabar son ayi karatun haka suke takowa suje a k'afa su dawo a k'afa , babu ranan da zasu fita maza basu biyo su ba sunan Sam magana da su amma Sam basa sauraran su hakan yasa dole Ummi ta fara sa nik'ab amma duk a banza , Dan wasu ma da suka gane gidan nasu kai tsaye suke zuwa Susa yara suyi sallama , duk da Hafsa tasha gaya musu cewar Ummi matar aure ce amma Sam basa yarda , tun Malam be San meke faruwa har yazo ya sani amma dai ya zuba mata ido ne kawai lokacin da suka d'iba ya ciki,
A b'angaren Dr Ahmad kuwa komai zai yi ma Abdallah tsakani da Allah yake yi mai baya la'akari da cewar bashi ya haife shiba duk wani Abu na more rayuwa ya mallaka mai tun daga kan suturar sawa har zuwa mota me tsada tare da sauran a bubuwan more rayuwa Dr baya k'yashin sai mishi , yanzun haka yana nan yana gina wani tamfatsetsen asibiti da niyyar idan Abdallah ya dawo ya mallaka mai shi,
A b'angaran Abdallah kuwa karatun shi yake sosai ya madai hankalin shi , shima Saifullah ba baya ba yana da k'ak'walwa sai dai shi wani lokacin yana da barkwanci kamar Umar, a haka suke karatun su Wanda ko Hutu akayi basa dawo wa Nigeria,
*BAYAN SHEKARA D'AYA*
Ummi ce zaune gaban Malam , Ummin ta , Mama da kuma Inna a bokiyar zaman Babar ta duk sun tsura mata ido , ita ko sai faman k'walla take share wa ,
Cikin sanyi Malam ya fara magana "Ummi tun d'azun muke miki magana baki bamu amsa ba gashi sai kuka kike yi "
Cikin kukan ta fara magana " Baba Dan Allah kar ku raba in da yaya Abdallah wallahi ni ina ji ajiki na yana Raye be mutu ba "
Mama ce tace "to yanzun Ummi ai ba zaki zauna kiyi ta jiran shi ba yan zun kusan shekara uku fa , kiyi hak'uri Ummi "
Ummi ta kalli Mama tace "yanzun Mama har da ke ake shirin rabani da Abdallah ?"
Karin Mama tayi magana Inna ta amshe " Ummi muna sonki muna k'aunar Ki shiyasa mukayi wannan tunanin Ki fahimce mu ba muna nufin cizguna miki bane"
Malam yayi gyran murya yace " shikenan Ummi na sake k'ara miki shekara d'aya amma kisani daga wannan ba k'ari ,"
Shiru tayi sannan kuma ta jinjina kanta alamar ta yarda ,
Sannan Malam ya ce ta tashi ta tafi ,
Tana Shiga gida Hafsa ta samu tana shara , Hafsa na ganinta ta shigo idon nan jajir ga k'walla suna sintiri a Kumatun ta ta saki tsitsiyar ta nufi kanta tana fad'in
"Aunty Ummi lafiya ?, mai aka miki?"
Cikin sauri Ummi ta k'arasa kusa da Hafsa tan rungume ta tana kuka tana fadin " Hafsa zasu raba ni da farin cikina da jin dad'i na ,"
Hafsa cikin d'aurewar kai ta ce "Aunty mene ne wannan abun da za'a rabaki dashi ?"
Cikin kukan ta sake cewa "zasu rabani da yaya Abdallah bayan duk sun San ba mutuwa yayi"
Cikin sigar lallashi Hafsa take shafa bayan Ummi tare da fad'in " kiyi shiru Aunty Ummi , babu Wanda zai raba ku , kuma insha Allah yaya zai dawo gare Ki"
Sun kusan minti goma atsaye Hafsa tana ta faman lallashin Ummi sannan ta hak'ura ta tafi d'akin ta kan katifarta ta fad'a tare da dafe kanta da take ji kamar ana sa gatari ana Sara mata shi, ahankali kuma take fad'in
"Yaya Abdallah meya ka nisanta dani? Shin baka San ina sonka bane ? Shin baka tunanin halin Dana ke ciki?, yaya rashin ka zai sa su guntule igiyar auran mu"
Ta k'arasa tare da sakin kuka mai siririn sauti nan da nan jikin ta yayi zafi sai zazzab'i chan kuma ta hau rawar sanyi ,
Shiko Abdallah suna zaune a d'aki shi da Saifullah suna buga game sai Saifullah yaji abokin nashi yayi shiru juyawa yayi ya kalleshi tare da fad'in "bro's how far?"
Kai Kawai ya girgiza mishi domin wani irin bugawa da ya wuce misali yake jin zuciyar shi tana mishi , Wanda har ya kasa magana,
Sake tab'ashi Saifullah yayi sannan yace "ba kada lafiya ne aboki na ?"
Cikin rauni ya kalli Saifullah ya girgiza gami da dauriya suka cigaba da game d'in .
Hafsa kuwa data ga Ummi ko alwalar magrib bata fito tayi ba gashi har an idar da sallar Isha yasa ta d'auki kwanon abincin su ta bita ta d'aki tana Shiga ta same ta tana ta rawar sanyi , ahankali ta k'arasa kusa da ita tare da tab'a wuyanta zafi rau ga wani irin numfashi da take yi sama sama , a tsorace Hafsa tace
"Aunty Ummi bakida lafiya ne?"
Ummi kawai ido ta bita dashi sai wasu zafafan k'walla dake gangaro mata,
Hafsa na ganin haka ta mik'e cikin sauri ta fita , fitarta yayi daidai da sallamar Umar ta amsa shi cikin firgice ta sanar ma da Mama halin da Ummi ke ciki, dukkan su suka d'unguma suka Shiga d'akin
Cikin tausayin Ummin , Umar ya ce ma Mama ta D'an shafa mata ruwan sanyi bari ya he ya siyo mata magani ya dawo ,
Haka kuwa akayi ba'afi minti ashirin sai gashi ya dawo d'auke da ledar magani ,shafa mata ruwan sanyin da mama tayi yasa ta D'an ji dama-dama
Cikin sanyin murya yace mata "sannu Ummi"
"Yauwa "ta fad'i sannan ya mik'a ma Hafsa maganin tare da fad'in "ku bata ta sha idan taci abinci , no zan Shiga gida sai da safe"
Godiya suka yi mai ,shiko rashin jin dad'in hakan yasa shi yamutsa fuska tare da fad'in"haba Mama yanzun Dan nayi muku wani Abu sai kun gode min idan kina gode min sai naga kamar kin ban-bantani da Abdallah Wanda bana jin dad'in hakan"
Ajiyar zuciya Mama tayi sannan tace "Allah yayi muku albarka , Allah ya jib'inci lamuran ku ya kare ku daga sharrin masharranta ya sada ku da alkhairin sa"
Cikin jin dad'in addu'ar mama duk suka amsa da "amin"
Sannan Umar yayi musu sai da safe ya fita,
[1/3, 3:37 PM] Maman Muhammad: *BAWAN ALLAH*
*MRS NN ONE💋*
*Readers bansan da bakin da zan gode muku ba akan addu'oin fatan alkhairi da kuke min nagode nagode Allah ya bar k'auna Allah ya sada mu a aljannatul firdaus*🤝
*Fiddausi (maman junior)*❤
*k'ungiyata abin alfaharina ina jidaku ina alfahari da ku da bazarku nake rawa REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS Allah ya k'ara mana hazak'a da basirar nishad'antar da masu karatu*🤝
® *_REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ ơʄ řɛąɖɛřŞ_
# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# *IG PML WRITERS*
# https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035
# http://maryamsbello.blogspot.com
2⃣8⃣
Ummi kam kwanan ta uku taji sauki har ta fara zuwa makaranta sai dai damuwa da yayi mata yawa tana yawan tunani wani lokacin sai kazo kusa da ita ka gama duk abinda zakayi bata sani ba ,
Hafsa kam ta shiga damuwa ganin halin da k'awarta take ciki ,
Wata rana suna school antashi break Hafsa ta fita ta samo musu D'an abin da zasuci , tana fita Ummi ta dasa tunani har Hafsa ta dawo bata San ta dawo ba, saida ta tab'ata tare da fad'in
"Wallah Aunty har za'a iya sace Ki baki sani ba "
Harara ta balla mata tare da fad'in "tunda na zama gunki ko?"
"A'ah ni bance kin zama gunki ba , nidai CI Waran nan Principal yana Neman mu a office d'in shi"
D'an kwab'e baki tayi sannan suka fara ci , Hafsa tana tunatar da ita illar tunani , ahaka suka gama ci sannan suka nufi office din P C kamar yadda suke Kiran shi , ko da suka suka isa sun Tarar da students takwas gefen P C vice d'in shine yana rik'e da wani file a hannun shi , bayan sun gaida su P C ya fara magana kamar haka ,
"Lura da yanayin k'ok'arin ku a aji shiyasa muka zab'eku , kuna da k'ok'arin da yawuce ace kuna SSS2, Dan haka mun yi muku alfarma kuje ku sanar ma iyayen ku zasu biya Rabin kudin jarabawar W A E C sauran kuma gwamnati zata biya "
Cike da jin dad'i d'aliban suka fara godiya gami da nuna farincikin su ,
Vice Principal ya ciro receipt me d'auke da iya yawan kud'in da zasu biya , sannan suka k'ara godiya suka koma classes d'in su ,
Ummi da Hafsa kuwa sai zumud'i ake akoma gida , Dan Ummi har ta manta da bak'in cikin da take tare dashi ,
Bayan an tashi kai tsaye gidan Malam suka nufa suka gaya mai shi kanshi yaji dad'i sannan yace musu suje gida ba wani damu wa insha Allah bazai gagara ba , da murna suka tafi,
Gidan Mama kuwa da sallama suka Shiga Hafsa ce tayi turus ganin mahaifinta cikin sanyi ta k'arasa Ummi kuwa Dama bata San Hafsa ta tsaya ba nan duk suka gaishe shi tare da tambayar mutanan gida sannan Ummi ta nufi d'akin ta Mama ko tana band'aki basu sameta a tsakar gidan ba,
Baban Hafsa ya kalleta cikin kula yace "ya makaranta ba dai wata Matsala ko ?"
Bayanin da PC yayi musu shi tayi mai ,murmushi yayi sannan yace " to ai ba damu wa idan na koma gida zan turo Bello da kud'in " cike da jin dad'i Hafsa ta fara godiya Baban ya sake cewa " Hafsa Ki natsu Ki maida hankalin Ki kiyi karatun nan Dan nan gaba inyi alfahari da ke"
"Insha Allah Baba ba za'a samu wata Matsala ba"
Dai dai nan Mama ta fito tana fad'in " 'yan makaranta an dawo?"
"Eh Mama ya gida ?"
"Lafiya lau "
Hafsa ta tashi ta Shige d'akin ta domin ta chanja kaya tayi sallah ,
Ummi kuwa da yake ba sallar take ba kwanciyar tayi har saida Ummi ta kawo musu abinci sannan ta tashi suka ci,
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
Ko wani Uba ya jajirce wajen Samar ma 'yar sa farin ciki kuma yanzun Alhamdulillah an dace Dan yanzun har sun gama zana exams d'insu both NECO , WAEC Nd JAMB, admission kawai suke jira,
Cikin sa'a kuwa suka samu admission a A B U ,dukan su zasu karanci Medicine bak'aramin dad'i suka ji ba mu sammam ma iyayen da su kad'ai suka San kud'in da suka kashe,
Bayan suyi registration da wuri ba har sai da aka fara lectures , sannan suka gama suka fara attending ,
Mutane da dama suna son yima Ummi magana daga mazan har matan amma rashin sakin fuskarta kesa su kasa zuwa wurin ta , ita ko bata San ma suna yi ba , Hafsa ce mai D'an sakin fuska har tayi k'awaye,
Watanni sunja lokaci ya tafi wata rana umma na zaune a class d'in su sai ga wani lecturer ya aiko wai a kira masa Zainab Kabir ,
Wani fad'uwar gaba ne ya Ziyarci zuciyar ta kawai sai ta fara fad'in "INNALLILAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN"
Hafsa dake gefen